SHU’UMIN NAMIJI COMPLETE HAUSA NOVEL

Kuka Zahrah ta fashe dashi, wanda batasan dalilin yinsaba, ita ta amincewa kanta cewa zata auri Dr Sadeeq amma saitakeji tamkar dole tayimawa kanta.
Batayi zato ba saiji tayi Dr Sadeeq yajawota jikinsa haɗe da sanya hannayensa duka biyu ya rungumeta. “Inasonki Zahrah, kuma nayi maki alƙawarin bazantaɓa wulaƙanta ki ba har’abada, kidaina kuka kinji princess ɗina!” yaƙare maganar tasa cikin sigar lallashi.
Daddaɗan ƙamshinsa shiyaso birkita mata tunani don haka tayi saurin janyewa daga jikinsa, tana mai yin ƙasa da kanta.
Sam shikam ma yamanta da cewa hakan da yayi ba’abu bane mai kyau, gaba ɗaya murna yacika masa zuciya.
“Uh sorry baby, gaba ɗaya kece kikamantar dani komai!!” Dr Sadeeq yafaɗi hakan yana mai dafe goshinsa.
Ƙasa ƙasa Zahrah tayi murmushi haɗe da kawar da kanta gefe, hakanan taji wani irin nauyin Dr Sadeeq ɗin yaƙaru acikin zuciyarta, haka kuma yaƙara girma acikin idanunta.
Wani irin kallo Dr Sadeeq yashiga yimawa Zahrah duk dacewa takau da kanta gefe, sai yanzu nema yake ƙara ganin haɗuwarta fiye da da, tabbas da Zahrah bata amince dashi ba to da ya tabka babban rashi, domin kuwa Zahrah tahaɗu, macece ita da kowanni Namiji zaiyi fatan mallaka.
Sam batayi tunanin kallonta yake ba, don haka taɗan juyo dan itama ta saci kallonsa, aikuwa karab idanunsu suka sauƙa akan najuna, da sauri Zahrah tayi ƙasa da kanta haɗe da cusa fuskarta tsakan kanun cinyoyinta.
Dariya Dr Sadeeq yayi cike da shauƙi haɗe da shafa sajen dake kwance akan fuskarsa. “Yaushe kika farajin kunyana? lallai zamu ɓata idan harkinajin kunyana!” ya faɗi hakan cike da zolaya.
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba, haɗe da marairaice fuska cike da shagwaɓa tace “To bakaine kaketa kallo na ba, saikace baka sanni ba!”
Lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu a lokaci guda, irin wannan salon shagwaɓan ai saita sashi bacci batare da yashiryawa hakan ba,lol.
“Ki faɗamin laifi ne don nakalli abar sona? saidai kiyi haƙuri amma kallonki yanzuma na fara, tunda kinamin kyau, kina kuma burgeni!” yanayin yanda yayi maganar abun burgewa ne, ga macen da tasan daɗin soyayya.
“Nidai kada ka wani ce inada kyau, daɗin bakine kawai nasan kakemin!” still da yanayin shagwaɓa tayi maganan.
Lumshe idanunsa yayi haɗe da fitar da iskan numfashi daga bakinsa, yanayin shagwaɓan Zahrah yafi komai burgesa a tattare da’ita, haka kuma sosai yake sauƙar masa da kasala. “Princess!!” yaƙira sunanta dawani irin murya mai taɓa zuciya.
A hankali ta ɗago idanunta ta kallesa, batare da ta amsa masa ba, ganin idanunsa a rufe, yasanya taɗan tsaya ƙaremawa fuskarsa kallo. “Duk kallona ɗaya da zaki yi bazai tafi a banza ba, sai kin biya kuɗi, gwamma ma kisani!” Dr Sadeeq yafaɗi haka batare da ya buɗe idanunsa ba.
Saurin ɗauke kanta tayi daga kallonsa haɗe da cewa “Niba kallonka nake ba”
“Zaki iya rantsewa cewa bani kike kallo ba?” yaje fo mata tambayar da batayi zato ba.
kanta tashiga girgizawa haɗe da cewa “Ai bankalleka sosai ba, kaɗan nakalleka!”
Dariya Dr Sadeeq yasanya wanda harsaida dimple ɗinsa suka bayyana, yanzu yayarda cewa Zahrah yarinyace ƙarama, kuma zakayi saurin kamata idan tamaka laifi.
Ƙoƙarin buɗe murfin motar Zahrah tasomayi, cikin mamaki Dr yace “ina zaki?”
“Zankoma gida ne, dama magana zan faɗa ma, shiyasa na ƙiraka, kuma nafaɗa ma, inada karatu, gobe muna da test a makaranta” Zahrah tafaɗi hakan dai dai lokacin da ta gama sanya ƙafafunta waje.
“Shikenan to My Princess kikulamin da kanki kinji, inasonki sosai!” Dr Sadeeq yafaɗa cike da kulawa.
Wani irin muguwar kunyarsace takama Zahrah, bashiri ta wuce cikin gida tana mai rufe fuskanta da tafukan hanunta.
Shima Dr ɗin murmushi yayi cike da jindaɗi, lallai idan ya auri Zahrah yakasance mutum mai sa’a, acikin satinnan insha Allah, zai sanarda ƙanin mahaifinsa azo a nemamasa auren Zahrah, a wajen Baffa.
“Aurenka da Salima fa?” Wata zuciyar ta jefo masa wannan tambayar, wani irin bugawa yaji ƙirjinsa yayi, gaba ɗaya amincewa dashi da Zahrah tayi yasanyashi manta halin da yake ciki na batun auren sa da Salima. Jiyayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, tabbas akwai ƙalubale a gabansa, domin kuwa yanada tabbacin cewa Hajiyarsa bazata taɓa sanja maganarta ba, gashi har ansoma shirye shiryen bikinsa da Salima, kuma shi a tsarinsa bai sha’awar auren mata biyu, Zahrah ita kaɗai ta’ishesa rayuwa, amma kuma tabbas yasan zai fuskanci matsaloli da yawa daga ƴan uwansa, matuƙar ya jajirce akan cewa Zahrah yakeso ba Salima ba, to amma dole zai jarraba sa’ansa, domin a gaskiya baijin cewa zai’iya haƙura da Zahrah.
Cike da sanyin jiki yayimawa motar tasa key, haɗe da nausawa kan titi.
Suna isa katafaren gidannasu, adai dai parking space motar tasu ta tsaya.
Bawani jinkiri Zaid yabuɗe murfin motar yafito, batare da yatsaya sauraran Mahaifinnasa ba, yanufi ɓangarensa kai tsaye.
Komai dake cikin ɓangaren nasa a gyare yake tsab, tamkar akwai wani wanda ke rayuwa a cikinsa, hakan kuma yasamo asaline da yawan gyara part ɗin da akeyi duk bayan kwana biyu, kasancewar Zaid mutum ne da bayason ƙazanta.
Direct bedroom ɗinsa yanufa, yanashiga yasoma rage kayan dake jikinsa, rigan wanka irin na maza mai gashi gashi a jiki yasanya, haɗe da sanya badroom slippers a ƙafafunsa, kai tsaye wajen fridge ɗin dake aje cikin ɗakin yanufa, maltina can yaciro haɗe da ɓalle ɗan ƙarfen da aka rufe bakin can ɗin dashi, yakai bakinsa, tunda yakai maltina can ɗin nan bakinsa bai ɗauke ba harsaida yatabbatar da cewa bakomai ciki ya shanye, cikin dustbin ɗin dake aje a ɗakin ya jefa can ɗin. Bathroom ya wuce haɗe da sakarmawa kansa shower. Wanka yakeyi amma gaba ɗaya tunaninsa baya garesa, yanaga shugar baby’nsa, amatuƙar matse yake da sha’awarta, haryanajin bazai iya daurewa yakai zuwa wani ɗan lokaci mai tsawo batare da’ita ba.
Bayan yafito a wanka yashiga shirya kansa cikin, haɗaɗɗun riga da wando masu kyau da tsadar gaske, gaskia komai na Zaid me kyau ne, domin kuwa kowani kaya yasanya saiya yi kyau, bakuma kayanne yake masa kyauba, shi ɗin kansa ne yake mawa kayan kyau,lol.
Haɗaɗɗen takalminsa sau ciki ƙiran kamfanin Gucci yasanya, aƙafansa, bayan ya ɗaura tsadadden agogon nan na Rolex a hanunsa mai kyau da burgewa. Daddaɗan ƙamshi ne kawai ke fita daga jikin shi, ƙamshine mai wahalar mantawa.
Black facing cap, yasanya akansa, domin kuwa yanayin garin ana ɗan busa sanyi, duk dakuwa cewa daga cikin sanyin yafito.
Wayarsa yaɗauka haɗe da car key ɗinsa, kai tsaye yafice daga cikin ɗakinnasa. Ɓangaren Mom ɗinsa yanufa. Hajiya Safara’u ne tsaye a gaban ƙatoton teburin cin abinci, yayinda Alhaji Ma’aruf ke zaune tana serving ɗinsa, batasan da shigowarsa ba saiji tayi ya rungumeta ta baya haɗe da ɗaura kansa akan kafaɗarta, cike da soyayyar mahaifiyarta sa yace “Barka da gida Momy!”
Cike da tsananin farinciki itama ta rungumesa haɗe da basa sumba a kan kumatunsa, “Barkanka da dawowa my son, ya gajiyar hanyar?”