SHU’UMIN NAMIJI COMPLETE HAUSA NOVEL

Aunty Raliya da kanta, ta jere masa kayan fruit da juice agabansa, cikin tsokana tace dashi
“Ango kasha ƙamshi, duk gajiyar shirye shiryen bikinne haka?”
Ɗan ɓata fuska yayi haɗe da ɗaukan apple ƙwaya ɗaya ya kai bakinsa.
“Ango labari ya sauya salo” yafaɗi hakan bayan ya cinye gutsuren apple ɗin dake bakinsa.
Cikin mamaki Aunty Raliya tace “bangane ba mekake nufi?”
Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da gyara zamansa.
“Akwai matsala Aunty!” yafaɗi hakan lokacin da gaba ɗaya yanayin fuskarsa ya sauya.
“Matsala! wace irin matsala Uncle?” Aunty Raliya tatambaya cike da ɗaurewar kai.
“Akwai wacce nakeso na aura, yarinyar tana matuƙar buƙatar taimakona, nayi ƙoƙarin na fahimtar da Hajiya hakan, amma taƙi saurarata, yanzu haka daga gida nake, nasoma yi mata bayani, tace natashi na bata waje, gaba ɗaya kaina yakulle bansan yazanyiba Aunty Raliya!”
Ya faɗi haka cikin damuwa.
Ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Aunty Raliya ta sauƙe “Turƙashi, lallai kuwa kazo da babbar magana, amma maiyasa tunda baka bayyana wacce kake so ɗinba, sai yanzu da komai yariga da yayi nisa? kafasan Hajiya da kafiya balallai ne ta fahimce ka ba, shawarata a gareka shine, kamabar wannan zancen, domin balallai kasamu abun da kakeso ba!” Aunty Raliya tafaɗi hakan da’iyaka gaskiyarta.
Cike da rauni Dr Sadeeq ya kalli Yayartasa. “Dan Allah taimakona zakiyi Aunty, kije kisameta kibata baki, wallahi inamatuƙar son Zahrah, sannan kuma yarinyar tana buƙatar kulawata, nikaɗai nasan matsalarta, please Aunty!!” yafaɗi haka yana me marairaice fuska, hadda haɗa hannuwansa biyu ga Aunty Raliya’n alamar roƙo.
Kallon mamaki Aunty Raliya tashiga binsa dashi, “wai yaushe Sadeeq yazama bawan soyayya ne?” ta tambayi kanta.
“Abune me matuƙar wuya amincewar Hajiya, amma zan jarraba, saidai kafun naje gareta, dole sainasan wacece yarinyar kuma su waye iyayenta, saboda kada aje Hajiya ta amince, akuma zo asamu wani mummunan labari akan ta”
Wani irin bugawa ƙirjin Dr Sadeeq yayi, domin kuwa anzo wajen, lallai baizama dole kowa yafahimcesa ba domin sanin sirrin Zahrah, zai iya sanyawa kowama yaƙi amincewa da aurensa da’ita, wanda shi a wajensa baiga ta’inda aurensu zai zamanto rashin dacewa ba, amma ba’a ƴar ɓoye a harkan aure, domin koda anɓoye tofa sai ya bayyana.
“Sunanta Zahrah, a unguwar Maraba take, sannan kuma marainiyace bata da uwa bata da uba, baffanta ne yake riƙonta, yarinyar tana da hankali sosai Aunty, sannan kuma tana da tarbiya, bata da wani aibu ko abun kushewa a tattare da’ita, saidai kuma…” kasa ƙarasa maganar yayi, domin kuwa baisan yanda yayartasa zata ɗauki maganar ba.
“Umm inajinka saidai kuma me?” Aunty Raliya tatambayesa cike da zaƙuwa.
“Ƙaddarace kuma tana kan kowa, haka kuma babu wanda ya’isa ya tsallake mata idan har tafaɗo kansa, akwai wani tsohon saurayinta da ya yaudareta yayi mata fyaɗe, watannin baya da suka wuce, wanda hakanne ma sanadin haɗuwata da’ita, amma ni banɗauki hakan amatsayin wani abu ba dazai hanani aurenta, kasancewar kowa da’irin tasa ƙaddaran a rayuwa!”
Sororo haka Aunty Raliya ta hangame ido da baki tana kallon Dr Sadeeq har ya idar da zancensa mai kama da tatsuniya.
Salati Aunty Raliya tasanya cike da tsantsar mamaki haɗi da al’ajabi, lallai Sadeeq baisan meyake faɗa ba.
“Fyaɗe! fyaɗe fa kace Sadeeq, anya kuwa kansan mekake faɗa? yanzu kai saboda rashin hankali irin naka, karasa wacce zaka gani kace kanaso, sai yarinyar da taraba budurcinta wa ƙattin maza, yarinyar da wani yagama sanin sirrinta!” Aunty Raliya ta faɗi haka cike da ɓacin rai.
Saurin rumtse idanunsa yayi domin jin magananganun Aunty Raliya’n yake tamkar sauƙan aradu, a kunnuwansa.
Cigaba tayi da cewa ” Lallai yanzu na tabbatar dacewa ba lafiyanka lau ba, taya kana cikekken namiji mai hankali da kuma kamala, karasa wacce zaka aminta da ta zamo uwar ƴaƴanka sai wacce wani ƙato ya haiƙemawa, yazama dole kasanja tunani Sadeeq, wannan ma ai zancen banzane, to gwarama kasani wannan yarinyar ba zaka taɓa aurenta ba matuƙar mu jininka ne!” Aunty Raliya ta ƙare maganar cikin hargowa.
“Haba Aunty maikikeson cewa ne? dan Allah kada kimin haka, nafaɗamiki matsalatane don bani da wacce tafiyemin ke, dama nasan za’a samu rashin fahimta, domin zakuga kamar Zahrah ba kamemmiyar mace bace, alhalin kuma bahaka take ba, tsautsayine yafaɗa mata, amma ni nayarda na amince zan aureta a haka, kada fa kimanta duk wanda yarufa asirin wani to Allah zai rufa masa nasa asirin, kitaimaka mu inganta rayuwar Zahrah, kitaimaka mucireta daga ƙunci, musanyata cikin farinciki!” yafaɗi haka cike da rauni.
Wani irin kallo Aunty Raliya tashiga yimasa, lallai Sadeeq baya cikin hankalinsa.
Murmushi mai ciwo Aunty Raliya tayi haɗe da cize laɓɓanta cikin takaici ta ce dashi.
“Kuskurenka na farko a rayuwa shine yarda dakayi cewa da gaske fyaɗe aka mata, shin ka ko san ƴan matan yanzu kuwa Sadeeq? to bari kaji wani abu, a shegen son kuɗi irin na ƴan matan yanzu, su da kansu suke saida budurcinsu ga wani daban, idan suka samu makahon da’idanunsa ya rufe ruf har yazo musu da zancen aure, sai su taƙarƙare su zabgamasa ƙarya kan cewa fyaɗe akamusu, bayan suda kansu suka kasa budurcin nasu a faifayi suka kai tallanshi kasuwa, ni ƴar uwarka ce ta jini bazan taɓa son wani abun da zai cutar da kai ba, saboda haka tun muna mubiyu nidakai, mubunne maganarnan anan, tun kafun ma yaje ga kunnen Hajiya, domin kasan idan taji cewa wacce kake shirin kawo mata ita amatsayin suruka, ba mutumiyar ƙwarai bace to zatayi mugun saɓa maka!!”
Take idanun Dr Sadeeq suka kaɗa sukayi ja, bakomaine ya sanya hakan ba face irin munanan kalaman da Aunty Raliya ta dinga jifan Zahrah dashi, tabbas yasan cewa mafi ƴawancin ƴan matan yanzu suna sayarda budurcinsu saboda abun duniya, amma banda Zahrah’nsa aciki, yasan Zahrah macece mai kamun kai, kuma duk wanda yayarda da ƙaddara dole ne ya tausayawa mata masu tsintar kansu a irin halin da Zahrah ta tsinci kanta a ciki.
“Ita bakamar yanda kike tunani bane Aunty Raliya, ki saurareni saina baki gaba ɗaya labarinta, marainiyace ta cancanci a tausaya mata, nima Namiji na tausaya mata balle ke mace, kuma dama ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ne!” Dr yafaɗi hakan cike da son ganar da Yayarta sa, cewa ba bu wani aibu agame da aurensa da Zahrah.
Gaba ɗaya duk iya abun da yasani agame da Zahrah, bai ɓoye mata ba, sai da yasanar mata, atunaninsa hakan zai sanya Aunty Raliya ta ƙaunaci Zahrah, amma me sai gani yayi tana taɓe baki haɗe da kawar da kanta gefe alamar ma ta’inda maganar tasa take shiga tanan take fita.
Yana idar da zancen ta dubeshi haɗe da ɓata fuska tace “Kagama? kai a tunaninka zaka bani wata hujja dazata sanya naga dacewar aurenka da’ita ne, hmm niba yarinya bace Sadeeq, yakuma zama dole kasanja tunani, kakuma manta da maganar wata wai ita Zahrah, idan kuma kafison kafuskanci ɓacin rai daga wajen Hajiya, to kaci gaba da zama akan bakan ka harmaganan takai ga kunnen Hajiya!!” tanakaiwa nan a zancenta ta miƙe fuuu tawuce cikin ɗakinta tabarshi zaune.