SHU’UMIN NAMIJI COMPLETE HAUSA NOVEL

Ita da Husnah suna fitowa a lecture sukayi mawa kansu ma zauni a inda suka saba zama ko da yaushe.
Cike da tsananin farinciki Husnah tace “Naji daɗi ƙwarai Zahrah da kika amincewa Dr, wallahi gayen ya haɗu da yawa ƙawata, tabbas idan kika auresa kin more don nasan za kisha madaran soyayya!”
Hararan wasa Zahrah ta wurgamawa Husnah, cike da son basar da zancen tashiga shafa cikin ta ” Nifa yunwa nakeji” tafaɗa tana mai turo baki gaba.
“Kada dai kice zakimin sakalci, domin niba Doctor bane” Husnah tafaɗa cikin tsokana. dukan wasa Zahrah takai mawa Husnah, da sauri Husnah ta kauce.
Cafeteria suka nufa acan suka cika cikinsu, daganan suka sake shiga cikin wani lecture’n.
Jikin wata bishiya dake kusa da ƙofar fita daga makarantar yayi parking motar sa, gyara zama yayi haɗe da duba agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa. Kallonsa ya mayar zuwa bakin tangamemen gate ɗin makarantar tasu, hakanan yakejin ba zai iya fuskantar ta gaba da gaba ba.
Amatuƙar gajiye su Zahrah suka fito a lecture. Tare suke tafe ita da Husnah, domin yau zataimawa Husnah rakiya ne zuwa super market. kai tsaye suka nufi ƙofar fita daga makarantar kasancewa driver’n gidansu Husnah najiransu a waje.
Wani irin faɗuwar gaba taji, ya risketa adai dai lokacin da ta fito daga cikin makarantar.
Daga ɓanagaren Zaid kuwa zuciyarsa ne tashiga dukan uku uku, alokacin da’idanunsa suka sauƙa akan Zahrah, hanu yasa ya murje idanunsa domin tabbatarwa da kansa cewa ita ɗince kokuwa gizo idanunsa suke masa.
Tabbas itaɗince Zahrah’n sane, har yanzu tananan da kyawunta, dakuma surarta mai ɗaukar hankalin duk wani lafiyayyen ɗa Namiji.
“ZAHRAH!” yaƙira sunanta a bayyane, duk da kuwa yasan cewa bazata ji sa ba. dai dai lokacin daya soma yunƙurin buɗe murfin motarsa don yaƙarasa gareta, dai dai lokacin itakuma ta shige cikin mota tare da Husnah.
13/December/2019
*Voted, Comment, and Share please…. Follow me on Wattpad @fatymasardauna
????????????????????????????????????????
SHU’UMIN NAMIJI !!
Written By
Phatymasardauna
Dedicated to My Brother KHABIER
????Kainuwa Writers Association
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
WATTPAD
@fatymasardauna
_______
Editing is not allowed????
CHAPTER 57 to 58
Cikin Hanzari ya buɗe murfin motar tasa ya fito, sai dai baikai ga ƙarasawa garesu ba, motar su ta gangara kan titi haɗe da ɗaukar hanya.
Hannayensa duka biyu yasanya ya kama ƙugunsa, haɗe da furzar da iskan numfashi ta bakinsa, sam baiso haka ba, amma babu yanda ya’iya dole binsu zaiyi.
Kallonsa yamaida ga sauran cincirindon ɗaliban da suke tsaye a bakin gate ɗin makarantar.
Gani yayi gaba ɗaya sun saki baki da hanci suna kallonsa, sai kace wanda suka ga baƙon halitta, bama kamar ƴan matan dake tsaye a wajen.
Tsuka mai sauti yayi haɗe da komawa cikin motarsa, da gudun gaske ya cilla motar tasa kan titi, haɗe da rufa mawa motar su Zahrah baya.
“Yadai, naga lokaci ɗaya duk kinyi wata iri dake?” Husnah tatambayi Zahrah wacce tazama silently lokaci ɗaya.
A jiyar zuciya ta sauƙe haɗe da maida kallonta ga Husnah ” Faɗuwar gaba nakeji Husnah, ban kuma san dalilin hakan ba” Zahrah ta faɗi haka cikin damuwa.
“To fa, Allah dai ya tsare, amma ki yawanta addu’a, domin hakanne zaisa koma mene ne yazo da sauƙi” inji cewar Husnah.
“Insha Allah!” Zahrah tafaɗi hakan tana mai kwantar da kanta a jikin kujeran motar, tanajin Husnah tace da Driver’n ya karkata akalar motar, ta sanja shawara shoprite kawai zasuje, bamusu kuwa ya sanja hanya zuwa Shoprite ɗin. Itadai Zahrah batace dasu komai ba.
Basu wani jima suna tafiya ba, suka iso tangamemen Shoprite ɗin. “Muje ko” Husnah tace da Zahrah tana mai ƙoƙarin buɗe murfin motar.
Cikin sanyin jiki Zahrah, tafito daga cikin motar suka nufi cikin shoprite ɗin.
Basket biyu Husnah ta ɗauka nata ɗaya na Zahrah ma ɗaya, acewarta Zahrah ta zaɓi duk wani abun da take so, sam bahaka Zahrah tasoba amma babu yanda ta’iya, domin kuwa Husnah kafiya gareta, idan tace kayi abu tofa wai dole sai kayi.
Kayan shafa suka soma ɗauka, kafun suka garzaya zuwa kan su jaka da takalma ƴan yayi, basu tsaya anan ba hadda kayan ciye ciye sai da suka ɗauka.
Cike da gajiyawa Zahrah ke tura Basket ɗin da kayanta ke ciki, ita mamaki ma take yanda Husnah tasa suka jidi kaya mai yawa har haka, amma idan tayi la’akari da irin gata da kuma kuɗin da mahaifin Husnah ke dashi, to sai tagama ba wani abun mamaki bane, kuma kuɗin kayan bazai mawa Husnah wahalar biya ba, domin kuwa anshagwaɓata sosai agida.
Daki daki aka lissafa kayan nasu, inda Zahrah ta ɗauki kayan dubu ishirin Husnah kuwa na dubu ishirin da biyar ta eba, ƙoƙarin miƙa wa Cashier ATM card ɗin dake hanunta Husnah ta soma yi. Amma sai Cashier’n yayi murmushi haɗe da cewa
“Ai Hajiya ba’a buƙatar kuɗin ku, domin kuwa an riga da an biya muku, tunkafun ku kammala sayayyan, sannan wanda yabiya muku yace idan ma kuna da buƙatar ƙari, to kukoma ku ƙara, duk shi zai biya kuɗin”
Cike da mamaki Zahrah da Husnah suka shiga kallon juna.
“Anbiyamana fa kace Cashier? shin ka kosan me kake cewa?” Husnah tatambayeshi cike da mamaki.
“Ƙwarai kuwa nasan me nake cewa, kudai ku ɗau kayanku kawai kuje, sannan ku gode mawa Allah, don shi yaje fo muku tsuntsu daga sama gasashshe ” Cashier’n nan yafaɗi haka yana mai washe baki, kasan cewar shima anbarmasa kyautan ragowan canjin su.
Mamakine ya lulluɓe su Zahrah domin su a iyaka sanin su basu da wani wanda zai biya musu kuɗin siyayyan da sukayi, domin kuwa basu zo da kowa ba banda driver, inakuwa driver zaisamu maƙudan kuɗaɗe irin haka har ya biya musu kuɗin siyayya alhali shima yana fama da kansa.
“Kozaka iya faɗamana wanda ya biya mana kuɗin ?” Husnah ta tambaya.
“A gaskia bansan saba, sai dai da duk kan alamu irin larabawan nan ne da suke zuwa Nigeria lokaci zuwa lokaci” Cashier ɗin nan yafaɗa musu haka, domin shi a yanda yafahimta, da dukkan alamu wanda.yabiya musu kuɗin baiyi zubi da ƴan nan gida Nigeria ba, duk da kuwa cewa muma muna da kyawawan maza amma kuma kyawun wani ya ɗare na wani.
Idanu Zahrah da Husnah suka zaro atare, sakamakon jin abun da Cashier yace.
“Balarabe fa kace?” Husnah ta sake tambaya cike da mamaki.
“Eh Balarabe, kece Zahrah ko?” Cashier’n nan ya tambaya yana mai nuna Zahrah da hanunsa.
“Ya’akayi kasan sunana ?” Zahrah ta tambayesa cike da mamaki.
Murmushi kawai yayi haɗe da miƙa mata wata farar takarda.
“Ungo yace inbaki”
Cikin tsoro Zahrah ta karɓi takardan da Cashier ke miƙo mata, haɗe da buɗewa.
“Kiɗauki duk wani abun da kikeso MY ZAHRAH! ban damuba koda duka Shoprite ɗin zaki ce kinaso, zan iya mallaka miki kome kikeso a duniyar nan, ko da kuwa dukiyata zata ƙare” abun da aka rubuta a jikin takardan kenan.
Wani irin bugawa Zahrah taji ƙirjinta yayi, “To waye?” tatambayi kanta a fili.