SHU’UMIN NAMIJI COMPLETE HAUSA NOVEL

“Yadai me aka rubuta acikin takarda’n?” Husnah ta tambayi Zahrah cike da zaƙuwa.
Bata takarda’n Zahrah tayi domin batasan me zatace da’ita ba.
Husnah tana gama karanta takarda’n tasaki murmushi haɗe da kallon Cashier’n nan daya zura musu idanu… “Mungode sosai, idan ka haɗu da wanda yabiyamana kuɗin, ka isar mana da saƙon godiya” daga haka ta kama hanun Zahrah suka fice daga cikin Shoprite ɗin, bayan sun ɗau ledodin siyayyarsu.
“Saida sukazo bakin mota kafun Husnah ta saki hanun Zahrah, still fuskarta ɗauke da murmushi tace “Mekika fahimta game da wannan takardan, da kuma biya mana kuɗin sayayya da akayi?”
Cikin ɗaurewar kai Zahrah tace “Ni ban fahimci komai ba, sai ma tsananin mamaki da nake, taya haka zata kasance, anya kuwa ba wata maƙarƙashiyan ake shirin ƙulla mana ba Husnah?”
Dariya sosai Husnah ta kwashe dashi, domin kuwa maganar Zahrah takai a dara.
“Maƙarƙashiyan soyayya ba, babu wani aljanu, kawai dai inaga wani ne yaganki kuma ya yaba, shine kawai” Husnah tafaɗa tana mai danne dariyanta.
“Bangane ba me kike nufi?” Zahrah ta tambaya cike da ruɗu, domin ita kwata kwata ma bata fahimci inda kalaman Husnah suka dosa ba.
“Kada ki damu zaki gane mushiga mota”
Jiki a sanyaye Zahrah tabuɗe murfin motar tashiga, a gidan baya sukai mawa kansu masauƙi ita da Husnah..
Suna shiga driver yayi mawa motar key suka ɗauki hanyar Suleja unguwar su Zahrah.
(yauwa kuyi haƙuri jiya nayi mistake sunan unguwar su Zahrah ba Maraba bane, sunan unguwarsu Zahrah Suleja ne, kainane ya ɗau charge shiyasa)
Yanaganin tafiyarsu yasaki ƙawataccen murmushinsa, “Haryanzu tananan da halinta na tsoro, yayi imani Zahrah bazata taɓa sanjawa ba”
” komai naki yana burgeni Zahrah, inason komai naki!” Zaid dake cikin motarsa yafaɗi haka cike da shauƙi.
“Nifa gaba ɗaya kaina ya kulle, kimin bayani mana Husnah, me takardan nan take nufi ne?” Zahrah tafaɗi haka cikin zaƙuwa.
“Ki kwantar da hankalinki ƙawata, kawai dai bazai wuce irin mutanen nan masu alkhairi bane suka aikata hakan, wayasani ma ko Dr Sadeeq ne” Husnah tafaɗi hakan tana mai kallon Zahrah.
“Mene? kinanufin wai Doctor ne zaiyi haka? gaskiya banjin cewa shi ne, domin idan da shi ne, dole zai bayyana kansa na gansa, kodai ke akeso amawa wannan hidiman akayi mistake aka ambaceni” Zahrah tafaɗi haka cikin kokonto.
Dariya Husnah takuma sawa, haɗe da dafa kafaɗan Zahrah..
“Wai lafiyanki kuwa Zahrah? kinga yanda kika firgice lokaci ɗaya sai kace wacce ta aikata aikin rashin gaskiya, to ni miye ma abun damuwa ne don wani yabiyamana kuɗin sayayya? kinga bafa mu muka sa sa ba, ko ma waye shi yasanya kansa, kishare kawai ƙawata” Husnah taƙare maganar ta ta bayan ta ɓare sweet ta jefa acikin bakinta.
“Hmmm” kawai Zahrah ta’iya cewa, haɗe da mai da kanta jikin kujera, itakam gaba ɗaya kanta ya kulle, taya za’ace bakasan mutum ba, amma kuma ya biyamaka kuɗin siyayyan da kayi, irin haka ne mutum sai yaje ya jefa kansa a matsala.
Tafiya suke amma Zahrah ta kasa cewa komai, sai ma Husnah ce keta ƙoƙarin janta da hira, amma jefi jefi take amsa mata, domin kuwa wannan faɗuwar gaban da takeji har yanzu baidaina ba.
A haka har suka iso ƙofar gidan su Zahrah’n… Har cikin gida Husnah tayimawa Zahrah rakiya, kana ta fito tashiga mota suka tafi.
Zama tayi akan katifarta haɗe da zubawa kayan siyayya da sukayi ido, sam zuciyarta bata kwanta da wanda yabiya musu kuɗin kayan ba, zuwa yanzu ya kamata ace tayi hankali, domin sarai yanzu tasan salon yaudaran maza baida ƙarshe, suna iya yimaka komai don su samu biyan buƙatarsu, wannan yana ɗaya daga cikin babban dalilin da yasanya ta amince da auren Dr Sadeeq, ko ba komai idan ya aureta ta tsallake wani babban siraɗi na daga yaudaran da Maza sukeyi mawa ƴan mata a wannan zamanin.
Ƙaran wayartane yakatseta daga tunanin da takeyi, cikin sanyin jiki ta ɗaga ƙiran nasa, haɗe da kara wayar akan kunnen ta.
“Barkanki da hutawa My Princess!”
Dr Sadeeq yafaɗa cike da tsantsar kulawa.
Ɗan guntun murmushi tayi haɗe da cewa “Kaima barkanka dai ya aiki?”
Ɓata fuska yayi tamkar dai tana ganinsa haɗe da cewa “Aiki ba daɗi kokaɗan, ya kundawo a super market ɗin kenan?”
“Eh” tabashi amsa a taƙaice. Domin tsabar gajiyan da ta kwaso har wani bacci bacci takeji.
“Naga kamar kingaji da yawa, ki samu ki ɗan huta, zuwa anjima zanzo gida, inaso na samu Baffa, idan yabani dama zanturo magabata na ayi maganar auren mu, domin banso akai nanda wata ɗaya ban mallakeki ba!” yaƙare maganar cikin yanayin shauƙi.
Wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, sakamakon jin abun da Dr Sadeeq yace. Wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki, wanda baza’a ƙirasa da farinciki ba, ba kuma za’a ƙirasa da yanayin baƙin ciki ba.
“Zahrah na!” yaƙira sunanta jin cewa tayi shiru batace dashi komai ba.
“Umm” ta’amsa masa a kasalance.
“Naji kinyi shiru, ko dai bakiyi farinciki da hakan bane?”
Yajefo mata tambayar da batayi zaton zai mata shi a yanzu ba..
“A’a nayi farinciki mana, kawai dai kainane ke ɗan min ciwo” tafaɗi haka don ta kare kanta, gudun kada yafuskanci wani abu.
“Ayya kiyi haƙuri, anjima idan zanzo zan tahomiki da magani ko, yanzu ki kwanta ki huta, nasan ma stress ne, insha Allah zuwa anjima zaki ji ki normal” yafaɗi hakan cike da kulawa.
“To” kawai ta’iya cewa dashi, haɗi da zare wayar akan kunnen ta.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauƙe, haɗe da share ruwan hawayen da suka fito daga cikin idanunta. “Yazama dole nakoyi soyayyarka Dr Sadeeq, domin bayan kai babu wani wanda zai bani kulawa kamar haka, ya Allah kamin maganin matsalolina!” tafaɗi hakan a bayyane, bayan ta ɗaga idanunta zuwa sama.
Da ƙƴar ma ta’iya cusa abincin da Inna ta bata, domin kuwa hakanan taji zuciyarta ta cunkushe.
Kwanciya tayi akan katifarta tana ƴan tunani, take bacci ɓarawo ya siɗaɗo ya ɗauketa, batare da tashiryawa hakan ba….
Zaune yake akan wata haɗaɗɗiyar kujera, wanda take ita kaɗaice kuma na mussaman acikin bedroom ɗinsa, dake cikin guest hause nashi. ɗan ƙaramin table ne aje a gabansa, wanda samansa ke ɗauke da zungureriyar kwalbar wine da kuma glass cup.
Wayar sace riƙe a hanunsa, gaba ɗaya hankalinsa akan wayartasa yake, murmushine ɗauke akan fuskarsa, yayinda yake playback ɗin vedi’on daya mata ɗazu fitowarta daga cikin shoprite, batare da ta sani ba.
Harzuwa yanzu bai tantance mai yakeji a jiki da zuciyarsa ba a game da Zahrah, abu ɗaya yasani shine, yasan cewa “yana matuƙar buƙatarta a kusa dashi, fiye da tunanin mai tunani, yakuma ɗauki haka, amatsayin fitinanniyar sha’awarta da yake” sake playback ɗin vedion yayi bayan yakai ƙarshe akaro na barkatai domin kuwa yayi playback ɗin vedi’on yafi sau goma daga zamansa a wajen zuwa yanzu.
Wani irin sanyi haɗe da kewarta ne suke ratsa zuciyarsa alokaci guda.
“A hankali zankuma cimma burina akanki Zahrah, akaro na biyu ma ina da tabbacin cewa zanyi nasara akan ki, domin niban kasance Loser ba, bakuma zantaɓa kasancewa Loser ba, har abada !” yafaɗi haka cike da son ƙarfafamawa kansa guiwa.. A taƙaice dai haka Zaid yayita playback na vedio ɗin da yayi mawa Zahrah yana kallo, zuciyarsa cike da nishaɗi, abu ɗayane zai hanasa zuwa gareta a yanzu, shine plan ɗin daya shirya mata, bakuma zai je gareta ba, harsai ya tabbatar da cewa ta gama rufzawa cikin tarkonsa, da ya ɗana mata a karo na biyu….
(????)