NOVELSUncategorized
TARAYYA 31-32

31
Not edited.
Kallon adama dake qoqarin saukowa gado yayi yaga yanda jikinta ke rawa saidai Sam bata tata yakeyiba mafarkinsa ya girgiza tunaninsa da zuciyarsa matuqa sbd su mutane ne dasuka
Basason ‘yaya mata sbd muguwar aqidar dasuke ciki ta wani irin mulki da ake gudanarwa na tsantsar iko kowa yasan mulkin mace a mineelik masifa ce dabaza’aso maimaitawaba sbd jinin matansu bazai iya controlling na abinda yake tareda throne dinba kamar namiji shiyasa mulkinsu yake zama tamkar masifa ko annoba sbd mulkine na tsantsar zubarda jini Wanda babu yaro ba babba bare mata bare maza,ba tsoho ba tsohuwa.
Alqawarine yadauka bazai taba bari mace ta mulki mineelik ba koda zai rasa ransane sbd yasan duk macen dazata hau zaiyi wuya basuyi ajalin junaba dayaga haka ya roqi Allah yayi gaggawar daukar ransa.
Cikeda rudu adama takallesa tana goge fuskarta dahar lokacin take gumi tace,
Sultan nayi mugun mafarkinda gwara nayi mutuwar qasqanci a hannun 6arayi dana fuskanci irin abinda Nagani a mafarkin.
Bai kalletaba bare yatsaya sauraran abinda take fada sbd tunanin daya cika zuciyarsa akaro na farko arayuwarsa dayaji mulki yafara fita ransa sbd duba da irin mutuwar da sarakunan mineelik keyi yayi tunanin zai iya tsallakewa ya sauka mulkin salin alin batareda fuskantar irin qarshen sauran sarakunan ba shiyasa ya tattara duk dagewarsa akan ganin maheer ya karbi mulkin amma yaqi gashi matarsama ta haifi namiji arabasa da wannan masifar abu yaqi yiyuwa ta wani 6angare ga daular shiefffs na jiran rashin magajinsu su zamo bayi a qarqashinsu Wanda yafison ya sare kansa daga gangar jikinsa dayaga wannan baqar ranar yanzu kuma ga wata masifar nason 6ullowa sbd baisan me mafarkinsa na assultana yake nufi ba.
Hannunsa ya daga ahankali ya shafo fuskarsa cikin mamaki saiyaga zufa ne ke tsatsafo masa,
Rabon da yayi zufa a rayuwarsa harya manta.
Irin tarbarda akayiwa isowarsu ta qara sanyaya jikin rumanah sbd tafara fargabar itama me zata Haifa sbd ganin irin dubban jama’ar dasuka dogara da abinda zata haifa.
Lokacinda mamani tayi ido biyu da rumanah da cikin dake jikinta wani mugun jiri mai qarfi ya ‘dibeta nuratu tayi saurin tareta tana kallon idanuwanta dake cikowa da qwallar baqin ciki tace,
Mamani lafiya?
Kasa riqe hawayenta tayi sbd baqin cikin daya rufe zuciyarta tace,
Har abada bazanyi lafiyar zuciya ba sbd bulama da asma’u har bayan barinsu duniya basu bar kurwata ta zauna lafiya ba bayan duk balain dasuka sako rayuwata aciki dan haka wlh bazan zauna nashaqi numfashi mai dadiba sai ranar dana gama lalata dukkanin zuriar da suka bari aduniya….
Sakinta nuratu tayi cikeda mamaki da baqin cikin halin mahaifiyar tata muryarta na rawa tace,
Mamani dazaki cire abinda yake ranki gameda rumanah dakin cire sbd zai kaikine matakin halaka sbd yanxu tariga ta taka wani matsayinda duk Wanda yayi mata wani ganganci zai iya rasa rayuwarsa sbd dukkanin burin daular nan da zagayenta akanta da cikinta yake dan haka ki nesanta kanki da ita sbd gujewa rasa rayuwarki..ke mahaifiyatace ina sonki fiyeda komai amma bazan iya kallo ki cuci rumanah ba dan haka karkiyi abinda zai barni da rashin zabi face na fadi gaskiyar dazaki rasa rayuwarki.
Tana gama fadar haka tabar gurin cikeda damuwa
Duk murnarta da farin cikin ganin rumanah din ya 6aci sbd mamani.
Kukan 6aqin ciki mamani tasake tana tsinewa bulama da asma’u ta juya ta nufi gurin adama da sai alokacin zata fito tarbon.
Kallo daya tayiwa cikin rumanah taji tari mai qarfi ya sarqeta kamar ranta zai fita
take ta gigice da gudu akaje aka kawo mata ruwa ta karba tasha idanuwanta dasuka firfito sukai jajir sbd tari numfashinta na fita da sauri ta juya tabar gurin nanma idonta ya sauka kan na suhailat dake tsaye gefen Maheer ai take taji qaramar hauka na neman kama zuciyarta tana isa palonta na farko dukkanin bayi da kuyangin part din suka fice sbd gudun laifi lurada halinda take ciki.
Mamani data sake biyota da ruwa ta miqa mata har lokacin itama jitake kamar ta cinnawa mineelik wuta kowa ya babbake ya mutu ko zataji abinda ya tsaya mata a maqoshi ya fada.
Karbar ruwan tayi tasake sha tana cewa,
Burina dana gina tun ina budurwa bazai taba rushewaba kan baiwa ‘yar bayi,
Babu Wanda bazan iya raba gangar jikinsa da kansaba kan burina sbd burina shine burin karagar mineelik..
Cikin tsananin damuwa da baqin cikin mamani daya kasa dannuwa aranta tace,
Duk inda bulama da asma’u suka sauka saisun bar masifar data addabi kowa awajen
Shiyasa bazan numfasaba saina tabbarda na tarwatsa rayuwar rumanah da abinda ke cikinta.
Kallonta adama tayi da jajayen idanuwanta baqin cikinta na ninkuwa tace,
Ko bulama ne aduniya bai isa ya shiga tsakanina da hawa throne din mineelik ba bare ‘yarsa dan haka ni adama ayau ina sake daukarwa kaina alqawarin kawarda ko wanene ya shiga hanyata ta cimma burina
Idan nace ko wanene ina nufin ko wanene ciki bancire kowaba.
Cikin takaici mamani tace,
Allah yasa gurin haihuwa ta mutu daga ita har abinda zata haifa kowama ya huta.
Kobata mutu gurin haihuwa ba ta haifi namiji saiya mutu kozan rasa rayuwatane”””adama ta fada tana miqewa tsaye.
Tsayawa tayi tareda juyowa takalli mamani itama mamani ita takalla sai alokacin kowannensu yadawo nutsuwarsa jiki na rawa mamani ta zube tana sunkuyar dakai
Adama fuskewa tayi sbd duk duniya daga ita sai bokanta ne suka San da sirrinta sai yanzu da 6acin rai yasata fadar abinda ke ranta saidai kuma ga alama tasamu wadda zata riqa amfani da ita Dan cimma burinta musamman da kusancinsu da rumanar zasuyi amfani tunda tana yiwa mamani kallon uwa.
Wani irin babban sabon sashe da aka zubawa tsaro na musamman aka kaita Wanda yake gefen part din yarima maheer duk wani abin jin dadi da hutawa anxuba mata shi ga kuyangi na musamman da aka kawo mata.
Bayan duk wata aladar tarbonsu anyi angama da daddare bayan tayi wanka ta saka kayan bacci ta kwanta bakin gado tareda lumshe idanuwanta ta bude ahankali tareda kiran sunansa cikin zuciyarta.
Suhailat kuwa sbd yanayin jikinta da gajiya yasa tana kwantawa bacci ya dauketa cikin tsananin gajiya.
Abincin da aka aikawa kowaccensu daga part din sultana zaarah babu wadda tasamu damar ci har gwara suhailat tasha madara mai zafi sbd sanyi datakeji kamar zai kamata.
Rumanah kuwa kwance take tayi lamo cikin zurfi a tunani da tsananin son ganinsa sbd har lokacin takasa daina tuno yanayin dasuka rabu ‘dazun hakan na raunana zuciyarta da kuzarinta ahaka bacci yadan ‘dauketa tanayi tana farkowa hardai akai asuba tayi sallah takoma ta kwanta nanne tasamu baccin yadauketa sosai.
Qarfe goma ta fito palonta anan ta tararda dining shaqe da kalolin abinci ta kalli qofa kamar tana jiran isowar wani hardai tagaji ta nufi dining tana fidda wani irin qamshi mai dadi.
Fara cin abincinta kenan taji muryar data sakata dakatawa ta juyo da sauri suka hada ido da nuratu dake cikin tsananin farin cikin ganin rumanah din.
Miqewa rumanah tayi zata nufeta Jakadiya data kawo mata nuratu din tayi gyaran murya dole ta tsaya tana kallon nuratu cikeda farin ciki
Nuratu ‘dince taqaraso gaban rumanah tana kallon cikinta tana sake bayyanarda farin cikinta zata zube qasa rumanah ta riqota tareda Rungumeta duk da tsinin cikinta baibari sun rungume juna sosaiba.
Cikin tsananin murna rumanah tace,
Tun jiya yakamata ace ke nafara gani da mamani amma shine kikaqi zuwa sai yanzu danace anemoki ina mamani?
Baki washe tace,
Mamani qila wani aiki ya hanata zuwa nima sbd tun jiyan nake yawo a hanyar sashen nan sbd kawai naganki amma bansamu damaba yanxu ana cewa kekenemanmu na aje aikina nazo bakisan yanda na matsu nagankiba rumanah nayi kewarki sosai kinbarni cikin kadaicinki…
Hawaye suka sakata kasa cigaba da maganarta
Rumanah ma hawayen ne suka ciko mata idanuwa ta riqe hannunta tace,
Nayi kewarki nima nuratu saidai bayanda zanyine sbd kinsan da zabi ake bawa mutum nafison zama taredaku duk da ayanxu komai ya canxa arayuwata saidai matsayinku nanan keda mamani bazan ta6a canzakuba arayuwata.
Murmushin qarfin hali nuratu tayi tace,
Mamani bazata taba daukarki ayanda kika dauketaba.
Ni zan cigaba da daukarta matsayin yayar mahaifiyata har qarshen rayuwata bazan taba duba abinda takeminba tunda na saba.
Karkice haka rumanah sbd yanxu akwai banbanci bazanzo na rasataba sbd yi miki wani abu yanxu daidai yakeda rasa rayuwarta.
Karki damu da wannan yanxu zo muci abinci tare nayi kewar hakan sbd bansaniba kozan sake samun irin wannan damar tacin abinci tare dake.
Zama sukayi a babban dining din mai kujeru goma sha biyu nuratu na ‘dar ‘dar rumanah najanta da magana sbd tasaki jikinta ahaka sukaci abinci nuratu taci abinda takeso ta qoshi suka nufi palonta na qurya nan suka fara fira
Nuratu takalli cikin rumanah dayayi mata kyau matuqa musamman sbd bai sakata qiba ba tsawo yayi sosai.
Murmushi tayi cikin kulawa tace,
Nayi farin cikin ganin rayuwarki ta canxa rumanah gashi zaki haifar mana ‘yaya jinin sarauta.
Kallonta rumanah tayi tasaki murmushi kawai sbd tunaninta ba akan firar tasu yakeba.
Agurinta nuratu ta wuni sai tsakar dare ta tafi koshi da sharadin gobe Jakadiya zata saka acanza mata aiki adawo da ita gurinta.
Mamani kuwa sunyi jiran zuwanta harsun gaji bata zoba gashi dokace akan rumanah bazata fita koinaba idanba da qwaqwaran daliliba harsaita haihu.
Washe gari aka dawo da nuratu aiki gurinta duk yanda taso hanata aiki tabarwa sauran kuyangin qi tayi saidatayi.
Kowace safiya da maraice sai Ammy ta Aiko mata da madara mai zafi itada suhailat harsukai kwana uku inda tun tana dannewa harsaida damuwarta ta daqushe kuzarinta matuqa dan ita kadai tasan halinda zuciyarta take ciki na rashin ganinsa gashi da alama bazata sake ganinsa ba saita haihu qila hakan ke sata kwantawa tayi kukanta sbd ji take nutsuwarta na neman gagararta abincima tun nuratu na iya yinta dan ganin taci har abin yafi qarfinta ta sanarda Jakadiya rashin cin isashen abincinda rumanar keyi.
Lokacinda Jakadiya taje ta sanarda ammy hakan yarima na tareda ita bai ‘dagoba amma ammy kallo ‘daya tayi masa tagano halinda yake ciki musamman dama tana lureda shikansa miskilanci da mulkine yahana agano halinda yake ciki na rashinta.
Jakadiya tayiwa wani irin kallo nan take tagano me take nufi ta gyada kai ta wuce zuciyarta fal tsoro da mamakin irin sonda yarima kewa rumanah haka ta wuce taje kitchen ta bada umarnin ayi dukkanin girkinda akasan yarima maheer naso a shirya a palonsa na musamman zaici abincin daren tareda matansa.
Da daddare koda Jakadiya tazo kiranta cin abinci cikin yanayi na rashin walwala tace batajin dadin cikinta bazata iyacin abinciba yanzu sai zuwa anjima.
Ba musu Jakadiya ta tafi
Koda yafito cin abincin cikin wata irin shiga ta musamman ta kayan shan iska qamshinsa na fita ahankali.
Suhailat dake zaune da cikinta ya kalla cikeda kewarta da tausayinta ya ware mata hannu ta taso ahankali tashige jikinsa ta rungumesa tareda sakin ajiyar zuciya.
Cikin kulawa ya dagota tareda kallon fuskarta da cikinta ya shafi fuskarta ahankali yace,
Hey hw are you?
Murmushin mai ciwo tasaki na qarfin hali tace,
Lafiya klau I missed you””ya fada tana zamewa daga jikinsa ta zauna kan dining sbd ita kadai tasan me ta hango a cikin idanuwansa.
Zama yayi yana sake kallonta ganin jikinta yayi sanyi lokaci ‘daya duk saiyaji lissafinsa na sake kwancewa abincin gabaki daya yafita ransa.
Itama abincin fita ranta yayi saidai hakanan ta tsakuri kadan taci ta miqe tazo tayi kissing forehead dinsa tace,
Gud night””ta fice tana mayarda hawayen idonta.
Harta fice bai motsaba sbd damuwa da takaicin kansa dayaji akaro na farko.
Saqone yazowa Jakadiya daga yarima maheer cikin gaggawa ta nufi sashen rumanah ta bada umarnin duk wata baiwa dake sashen rabarshi cikin mintuna biyu kacal.
Babu 6ata lokaci dukkaninsu suka watse bayan koina yadauki sabon qamshi sai masu tsaron qofar shigowa ne kawai.
Kwance take lamo bakin gado idanuwanta a rufe tayi nisa cikin tunani.
Ahankali taji qamshinsa yana shiga hancinta ta bude ido tareda lumshewa zuciyarta na sake shiga damuwa sbd tasan har abada bazaizo sashentaba sbd atarihin sarautar mineelik ba’a taba yin sarki ko yariman dayaje ‘dakin matarsaba saidai ita taje to mezaisa shi yazo gurinta.
Shafo fuskarta yayi ahankali cikeda kulawa yana kallon kyakkyawar fuskarta tayi saurin bude idanuwanta dasuka ciko da hawayen ganinsa saita samu kanta da mayarda idanuwanta ta rufe.
Rintse ido yayi cikeda mamakin kansa ya kamo hannunta ya riqe cikin nasa murya qasa qasa yace,
Are you angry?
Bude ido tayi takallesa sbd bata taba tunanin zai kulaba harya tambaya.
Idonta dake kansa yakalla yana sake matse hannunta cikin nasa yace,
Tashi zaune.
Ba musu ta tashi zaune ya saki hannunta ya fito palo tabisa da kallo zuciyarta na qara mutuwa a sonsa,
Jin soyayyarsa takeyi har cikin jini da ruwan jikinta kowane bugawar zuciyarta da sonsa take fita tana fata da roqon Allah yasa kar soyayyarsa tasakata kaucewa hanya takoina koda kuwa sonsa da kishinsa zasu kasheta.
Jakadiya na ganin fitowarsa tayi saurin qarasowa tace,
Allah yataimaki uban magajin mineelik akwai abinda ake buqatane?
Hannayensa ya zuba cikin aljihun wandonsa cikin wani irin miskilanci yace,
Ahado abincin cin mutum biyu.
Cikin qanqanin lokaci ta dibi abincin cin mutum biyo ta jero a tray takawo masa ga mamakinta hannu yasa yakarba ya juya dakin yabarta da baki sake sbd tsananin mamaki.
Duk yanda yaso tasakar masa fuska qi tayi yasamu ya lalla6ata taci abincin ganin shi baici ba yasata daukar abincin itama ta basa babu musu yaringa ci harsaidata kwatanci ya qoshi ta ajiye tana kallonsa da mamaki yadauki tray din yamiqawa Jakadiya dake palo ta fice da kayan.
Brush yakaita har toilet tayo suka dawo ta zauna bakin gado ya zauna kusada ita tareda kallon fuskarta dahar lokacin take kadaran kadahan duk saiya rasa me ke masa dadi baimasan mezaice mataba sbd baisan menene yake faruwaba gabaki daya ta qarasa dame masa lissafi ya dafe goshinsa tareda rintse ido ya bude ya miqe zai tafi kawai yadawo yajawota jikinsa ya rungumeta batareda yace komaiba.
Rungumesa itama tayi tareda barin hawayenta datake riqewa suka gangaro tana sake qanqamesa.
Tun jekadiya na jiran fitowarsa harta gane ba fitowar zaiyiba tabar palon takoma palon farko ta dasa sabon jira.
Tunda tabaro gurinsa mararta tafara ciwo ahankali tana shiga bedroom dinta takwanta tana qoqarin danne ciwon datake ji amma alamarin yafara qarfafa kafin tayi wani yunquri ciwon mara ya taso mata gaba ‘daya gashi cikinta yanxune yashiga cikin wata na bakwai.,
Cikin qanqanin lokaci ta tabbarda naquda ce ta taso mata mai tsananin azaba sbd bata taba jin irin wannan ba a duk haihuwarta tun tana boyewa tuni yaci qarfinta koda Carolina taji kamar nishinta a dakin da sauri ta fita zuwa neman mutane duk da dare ya tsala sosai har anyi kiran farko.
Asubar farin yabaro part din yakoma nasa ita kuwa zazzabi ne mai qarfi ya rufeta bayan wankan datayi da asubar amma bata nuna masaba saida ya fice takwanta tana rawar sanyi mararta na mata ciwo ahankali.
Qarfe takwas na safe ta shirya daqyar tana daddaurewa sbd ta masa alqawarin zuwa gurin ammy yin breakfast su hadu acan.
Nuratu na lureda kamar batajin dadi amma tayi shiru sbd ganin kamar batason yin ko magana suka fito suka nufi sashen sultana ana biyeda ita bayi kuwa sai zubewa sukeyi suna bata hanya cikin tsananin girmamawa.
Jakadiya nacan tareda masu karbar haihuwa sashen suhailat hankulansu duk atashe sbd haihuwar tazo mata da gardama matuqa
Shikansa lokacinda labarin ya iso masa hankalinsa ya tashi dan haka ko gurin ammy bai nufaba ya kira doctors din dake karbar haihuwar kasancewar yasansu duka matane suke karbar haihuwa a masarautar in brief sukai masa bayanin haihuwa ce zatayi ta wata bakwai kuma tazo da gardama sosai.
Kafin su isa sashen ammy ta lurada akwai abinda yake faruwa a masarautar sbd koina yayi tsit babu dogon motsi nuratu ce ta sanarda ita suhailat ce ke naquda.
Faduwa gabanta yayi zuciyarta na cikeda mamaki da tausayin suhailar da ita kanta batace komaiba sai sanyi da jikinta yayi tana mata fatan haihuwa lafiya.
Cikeda kaduwa da rashin sukuni ammy ta kalli Jakadiya tace,
Ya Allah karabasu lafiya saidai ina cikin damuwa da fargabar yaya haihuwar rumanah zata zo itama Allah kadai yasan mezata haifa.
Numfashi mai qarfi da sanyin jiki Jakadiya tasaki cikin rashin sanin abinyi itama tace,
Mafita ‘dayace itace idan har anason sirrin mutuwar iyayen rumanah yazamo sirri daga gareta muyi adduar kar asamu namiji daga gareta idanma ansamu namijin mutuwarsa itace mafita.
Kallonta sultana tayi da sauri tana sake shiga rudu tace,
Mutuwarsa na nufin qarasa bankado komai Wanda kinsan hukuncinda zamu fuskaanta agun sultan zaifi musan hanyarda zamubi musan wannan sirrin yacigaba da zama sirri kamar yanda sultan yafada tun farko…
Saidai kuma zuciyata na quna da fargabar yanda zan fuskanci rumanah ranarda tasan mune sanadin mutwar iyayenta….
Da qarfi ruwan haihuwa suka 6alle mata lokaci ‘daya sbd masifa da tashin hankalinda tashiga lokaci ‘daya
Cikin tashin hankali suka juyo cikeda mamaki da tashin hankalin abinda taji kafin suyo kanta ta durqushe agurin cikin tsananin azabar ciwon mara nan take naquda mai qarfi ta taso mata.
#mamuhgee.
[12:36 AM, 7/30/2019] +218 94-4138736: TARAYYA
wattpad @mamuhgee
Haske writers association????
32
Not edited
A gagguce
Dafe cikinta tayi cikeda tsananin azaba da wani irin juyi da cikin keyi mata.
Arikice Nuratu ta riqota tana kiran sunanta cikin tsoro da tashin hankali
Su ammy atare sukayo kanta cikin sobon tashin hankali da fargaba
Ammy ta riqota tana kiran sunanta cikin damuwa take kiran sunanta.
A gaggauce suka kamata sukai sashenta da ita inda tun kafin su isa ta qarasa rikicewa sbd azabar naqudar.
Cikin gaggawa Jakadiya ta isa gaban sultan dake zaune cikin royalhall suna jiran haihuwar suhailat ta zube qasa kanta qasa ta sanarda shi ummu-rumanah ta shiga naquda yanxunan.
Da wani irin kallo ya dubeta zuciyarsa na shiga wani sabon farin cikin sbd yasan cikinsu biyun dole asamu namiji insha Allah.
Wani murmushi yasaki na qasaita cikin nuna isa yace,
Kije idan akasamu namiji a mineelik yau namiki na miki alqawarin dukiyarda bazaki iya qirgata da kankiba sai antayaki.
Cikin fargaba tayi godia ta fice hankalinta tashe sbd daga ita har sultana a gigice suke basa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali sbd fargabar haihuwar rumanah dakuma babban sirrin dataji Wanda basusan ta yaya zasu fara fuskartartaba saidai abinda suka sani kome zatayi wannan sirrin bazai fadu garetaba babban tsoronsu da tashin hankalinsu kar Maheer yaji wannan alamari.
Kai tsaye sashen yarima ta nufa lokacin yana zaune palonsa na farko zaune ya dora qafafunsa kan table din dake gabansa ya rufe idanuwansa kallo daya zaka masa kasan kadaici yake buqata baya buqatar hayaniya sbd yanayin naqudar suhailat dayake cinsa musamman yanda yasan ta wahala haihuwarta ta qarshe gashi yanxu har lokacin bata haihuba yana iya sensing azabar datake ciki.
Gabansa Jakadiya ta tsaya tareda rusunawa cikin jimami tace,
Allah yataimaki uban magajin mineelik uwardakina ummu-rumanah ta shiga naquda yanxunan..
Idanuwansa dake rufe ya bude ahankali ya zuba mata suna sake canxawa sbd dama tuni suka canxa sbd zaman jiran na kashesa.,
Miqewa tayi ta fice jikinta a sanyaye sbd gabaki daya ta rasa nutsuwarta jitake kamar zata zauce sbd fargabar tashin hankalinda zai biyo baya idan rumanah ta haihu ta tambayi abinda taji ayau din.
Wayarsa daya kashe ya dauka ya kunna tareda kiran Dr ammenen muryarsa na bayyanarda tsananin damuwarsa da tashin hankalinsa yace mata tabar Dr noorah da nurse agurin suhailat taje gurin rumanah takuma babbatarda tana basa bayanin komai harta haihu idan kuma taga da damuwa takirasa kawai zaizo yakarbi haihuwar da kansa duk abinda zai faru yafaru.
Aje wayar yayi zuciyarsa kamar zata buga,
Yanxune yake sake takaicin haihuwarsu anan sbd acan shine zai karbi haihuwar kowaccensu da kansa musamman ita datake ta farkonta tana tsananin buqatarsa.
Dafe goshinsa yayi ya miqe yayi ciki ganin kamar zai iya rasa hakurinsa yaje musamman dayaga anfara jan lokaci babu wadda ta haihu.
Duk iya galabaituwa kowaccensu ta galabaitu sbd kowacce gadan gadan naqudar ta taso mata babu sauqi,
Duk Wanda ke cikin mineelik hankalinta a tashe yake tsit koina ana jiran tsammani
Sultan ma wannan karon saida hankalinsa yatashi shi fargabarsa kar doguwar naqudar tasa a rasa ‘yayan dake cikin.
Ammy duk inda nutsuwa da kwanciyar hankali suke basa tareda ita ko zama takasayi addua tajeyi tana qarawa musamman datake jiyo irin azabarda rumanar ke ciki sbd tana palo suna ciki tareda masu karbar haihuwar.
Zufa mai zafi Jakadiya ta sharce lokacinda Dr ammenen takalli nurse tace,
Get ready ga babyn nan fitowa yanzu Ku kawo komai kusa.
Zufa Jakadiya ta gogewa rumanah data fice hayyacinta cikin tsananin tausayi da tashin hankali take mata sannu.
Cikin wata irin rikitacciyar azaba tayi wani irin nishi mai qara Atake baby ya fado Dr ammenen ta qarasa jawosa tareda yanke uwa ta ‘dagasa sama ya buga wani irin kukan jarirai babu qaqqautawa.
Kadan yarage Jakadiya bata fadawa rumanah ba sbd rudewa da ganin abinda aka haifa.
Miqa mata shi Dr tayi jikinta na matuqar tsuma ta karbesa aka nado cikin farin zanin auduga mai tsananin laushi ta qura masa ido tana jera ajiyar zuciya ba qaqqautawa.
Wata sabuwar azaba ta tasowa rumanah cikin tashin hankali Dr takalli cikinta tana cewa nurse wani babyn na zuwa.
Jiki na rawa Jakadiya ta fito ammy data jiyo kukan jariri ta matso bakin qofar jikinta na ‘dan rawa zuciyarta kamar zata fado sbd bugawar datakeyi a qofar sukayi karo da jakadiya hannunta na rawa ta karbi jaririn tana qoqarin budewa taga menene cikin rawar murya Jakadiya tace,
NAMIJI NE.
Da sauri ammy ta dago ta kalleta tareda hadiye yawu ta qurawa yaron ido jajir dashi babu inda ya dauko rumanah Sak maheer ne saitaji bazata iya cutatar dashiba.
Nurse ce tazo ta karbesa sbd aankeshi dazasuyi su kintsashi kafin dayan babyn yafado sbd naqudar takoma qasa tsananin wahala take sha ko ayanxun.
Jiki na matuqar 6ari Jakadiya ta isa qofar sashen maheer tun a qofar ta zube tareda ‘daga murya tace,
Allah yataimaki uban magajin mineelik ummu-rumanah tasauka lafiya ansamu magajin mineelik da yardar Allah.
Zabura yayi daga kishingiden dayake yana sakin ajiyar zuciya da qarfi yana rufe ido sbd zaman jiran dayake shine abu mafi azabtuwa a tsawon rayuwarsa ayau ya raina zamtaowarsa likita tunda bai taimaki matarsaba lokacinda takeda tsananin buqarsa.
Fitowa yayi cikin wata irin qasaita hannuwansa zube a aljihunsa ya tsaya nesa da jakadiyar yana kallonta kamar tana daukeda abinda aka haifar yace,
Kije ina miki albishir da zama jakadiyar magajin mineelik tareda kyautar werik’i(gold)
Murna fal cikin ranta tace,
Ameseginalehu(godiya)
Miqewa tayi zata fita abakin qofa taci karo da ‘yar saqo daga sashen suhailat ta durqusa qasa cikin girmamawa da rawar jiki tace,
Gimbiyar yarima ta sauka ansamu NAMIJI saidai likita tace sanarda yarima bazata sake haihuwaba mmahaifarta tasamu matsala wannan itace haihuwarta ta qarshe.
Zaro ido Jakadiya tayi cikeda tsananin mamaki da farin ciki tareda tausayin suhailat tajuya takoma gurin maheer tasanar dashi atake ya sake lafta mata wata kyautar zuciyarsa na harbawa da qarfi
Ya zauna ahankali tareda lumshe ido yana yiwa Allah godia.
Koda Jakadiya takoma sashen rumanah haihuwar tazo gadan gadan nan wani babyn ya fado Dr ta ciresa nanma sukaga namiji atake aka shiryasu jikin Jakadiya babu inda baya rawa ta zube gaban sultan kanta qasa cikin tsananin farin ciki tace,
Allah yataimaki kakan magajin mineelik ummu-rumanah ta sauka lafiya ansamu ‘yan biyu duka MAZA sai gimbiyar yarima itama ta samu ‘da namiji
Ina yiwa sultan farin cikin ganin wannan rana mai tarin cikar buri da biyan buqata,
Ayau mineelik ta samu qaruwar ‘yaya uku uku duka maza ina sake taya sultan murnar ganin wannan rana.
Wani irin murmushi yake fitarwa mai bayyanarda farin cikin da zuciyarsa ke ciki bamai misaltuwa bane
Dukkanin Wanda ke royalhall din farin cikine mai tsanani a fuskarsa nan take aka buga bell din mineelik aka sanarda haihuwar magajin mineelik atake labarin farin cikin ya bazu koina Ethiopia ta dauka kowa farin ciki yake da wannan burin na qasar daya cika.
Dayake ba qaramar wuya dukkaninsu suka sha ba ana kimtsasu sai bacci banda rumanah data rufe idone kawai zuciyarta cikeda tashin hankali da fargaba tareda baqin cikin abinda kunnuwanta sukaji mata ammy na fada da bakinta.
Hawayen idonta suka gangaro batareda tadamu da gogesuba ta bude idanuwanta dasukai ja hawayen nacigaba da 6alle mata.,
Idan kunnuwanta sun jimata daidai ammynta ke fadar sune suka kashe mata iyaye kenan ba mutuwar Allah sukayiba qarfi da yaji aka rabasu da rayuwarsa,aka rabasu da ‘yarsu,Ashe shiyasa aka ‘yantasu???
Girgiza kanta tayi hawayenta na tsananta tace,
Ammy bazatayi hakaba nice banji daidaiba,ammy bazata iya kashe kowaba bare iyayena.
Sakin siririn kuka tayi tareda kifa kanta a pillow.
Suhailat kuwa bacci tayi sosai sbd ta galabaita fiyeda yanda ta tsammata saidai tana haihuwar taji batajin komai.
Lokacinda aka kaiwa maheer yaran duka yana tareda khaleefa daya iso ranar khaleefa ne yakarbi sauran biyun maheer kuwa Wanda aka fara haihuwa ya karba akaro na farko dayaji jikinsa yayi sanyi sbd soyayyar yaron dayaji shima yau yahaifi magajin kansa bama na mineelik kawaiba.
Qura masa idanuwansa yayi ganin yaron shine Zak sai lips din mahaifiyarsa daya dauko ya sa hannu ahankali ya shafo lips din tareda sakin wani irin murmushi qasa qasa yayiwa yaron addua kafin ya furta,
ABEEL HASSAN.
Kallonsa khaleefa yayi cikeda farin ciki ya maimaita sunan yana jinjina kai kafi ya karbesa ya miqa masa babyn suhailat da ba’ason motsasa sosai.
Qura masa ido yayi cikeda tausayinsa da qaunarsa mai qarfi shima shiya dauko Zak saidai zamansa qarami sosai yasa yafisu haske.
Addua yamasa sosai cikin rada rada ya furta,
Jemaal.
Koda ya karbi Hussain din abeel abrar bayan yamasa addua ya rada masa,
ABEEL HUSSAIN
Koda aka kaisu gurin sultan kowa saida yatabbatarda yau ranar daban take arayuwarsa ya ‘dagasu daya bayan daya yayi musu addua kafin aka sanar dashi sunayen da yarima maheer ya rada musu sultan mai damuba sbd ayau angama masa komai arayuwa ya ‘daga abeel cikin babbar murya yace asanarda kowa ga magajin mineelik ABEEL HASSAN.
Atake akaje dakin tarihi aka saka sunansa da sunan mahaifiyarsa nan aka fara shagulgulan haihuwar.
Har dare ammy bata samu ganin rumanah ba sbd tunda tayi wanka take rufe a dakinta tace bata buqatar kowa Hutu take buqata.
Lokacinda aka kawo mata yaranta qura musu ido tayi hawaye na gangaro mata sbd idan bar aka iya raba iyayenta da ita za’a iya rabata da ‘yayanta saidai batajin hakan zata iya yiwuwa koda zata rasa rantane.
Rungumesu tayi tareda rufe ido qaunarsu data mahaifinsu na shigarta tako ina.
Da daddare lafiyyan abinci kala kala aka aika gefen kowaccensu aka jera.
Duk yanda Jakadiya da ammy sukaso ganinta qin bari tayi ta dasun shigo zata rufe ido tana bacci idan sun fita zata cigaba da kukanta.
Kukane takeyi na rashin Sanin abinyi sbd ko ganin kowa batason yi.
Lokacinda labarin haihuwar tasamu adama da ‘yar dakinta mamani kadan yarage adama bata yanke jikiba mamani kuwa kasa daurewa tayi saidatayi kuka taji sauki sauqi cikin ranta.
Koda aka kawo mata yaran saka musu albarka saidata kai zuciyarta qololuwa gurin bugawa kafin ta iya kallonsu idanuwanta na cikowa da hawayen baqin ciki tasaka musu albarkar dole.
Suna fita ta miqe batareda takalli mamani dake matsar hawayeba cikin tsananin tashin hankali tace,
Duk yanda za’ayi ayi yaran nan bazasukai ranar sunansuba batareda sunbar duniyaba kije yanxu ina buqatar kadaici gobe zan fada miki abinda zakiyi sbd inason alhakin mutuwarsu ya rataya akan kakarsu da jakadiya sbd inason qulla gaba mai tsanani tsakaninsu da yarima tareda matansa kuma inason sultan ne da kansa zai yankewa sultana hukuncin kisa ta yanda abin zai riqa bibiyarsa yana damunsa da haka zansamu sauqin aikina akansa.
Acikin daren yakira suhailat yaji yajikinta tareda jemaal duk da khaleefa yadubasa sosai yafadi dokokin daza’abi kafin suna shi dole za’a koma Georgia dashi sbd yanayinsa acan za’a fara kula dashi.
Duk yanda yaso ganinta yasan abune mai wuya saidai kuma bayajin zai iya bacci bai dubotaba bayan baqar wahalar dayasan tashiga yau gurin haihuwa saidai koda ya aika asanarda Jakadiya taje tayi ma sashen isonsa ta sanardashi har lokacin bata fitoba taji jiki sosai hutawa takeyi haka ya hakura saidai asubar fari ya isa dakinta lokacin tana zaune bakin gado tasaka yaran agaba hawaye nabin fuskarta.
Qamshinsa yasata rintse idanuwanta hawayenta na sake gudu.
Zama yayi kusada ita tareda riqo hannunta baice komaiba ya kwantarda kanta jikinsa sai kawai tasaki kukan datake ruqewa ahankali
Cikeda mamaki da damuwa ya kalleta zaiyi magana ta zame daga jikinsa tana tsaida hawayenta cikin dasashiyar murya tace,
Kaina na ciwo ina buqatar hutawa.
Da mamaki yakalleta saidai baice komaiba ya miqe ya fice
Ta saki sabon kuka cikin rashin Sanin abinyi.
Duk inda hankalinsu ammy yake yatashi dashi kansa maheer din sbd kwana uku da haihuwar ko kadan rumanah takasa bari ko ‘dayansu ya ganta duk wani tashin hankali suna ciki
Ta hargitse tarasa abinyi gabaki daya ta birkice shikansa ta hanasa ganin kanta bare yasan meke faruwa babban tashin hankalin daya riskesu shine sanarwar da akayi za’a bawa uwar magajin mineelik kujerarta ta uwar sultan.
Sam ammy ta rasa ina zata saka kanta shikansa baya cikin nutsuwa sbd bazai taba bari ta karbi sunan uwar sultan ba gashi dole zata karba itace zata bawa duk Wanda takeso riqon kwarya.
Yau kwanansu biyar da haihuwar dukkanin yaran suna sashen ammy tun safe.
Tunda sukazo abeel hassan ke kuka sosai anmayardashi gurin hamaifiyarsa saima qara birkicewa da yayi nan hankula suka tashi tuni sultan yasa atara duk masu magani da likitocin mineelik amma sai qara rikicewa yakeyi nan hankalin rumanah itama yayi masifar tashi ta rikice.
Cikin tashin hankali suka dunguma zuwa royalhall inda ake duba yaron kowa hankalinsa atashe yake.
Kallo daya yayiwa rumanah yaji lissafinsa yasake kwancewa kafin yayi wani yunquri sarkin gida yossouf Kaleb yashigo jikinsa na matuqar rawa ya zube gaban jakadiya yayi mata magana qasa qasa hankali tashe jikinsa na wani irin mazari.
Zaro ido Jakadiya tayi cikin sabon tashin hankali jikinta yadauki muguwar rawa kowa hankalinsa nakanta anajiran jin saqon menene
Ta zube gaban sultan tareda sauke kanta jikinta na tsananta rawa cikin muryar tashin hankali da tsananin fargabar rasa rayuwarta tace,
Allah yataimaki sultan ina cikin baqin cikin sanardakai ankama baiwa mamani da dafin baqin maciji tabawa abeel Hussain da jemaal antabbatarda sun rasu saidai ankamata.
Rumanah dake zaune ta miqe a firgice jikinta na rawa saidai ko daga qafa batayiba ta yanke jiki ta fadi agurin.
Cikin tashin hankali yayi kanta kai tsaye yadauketa yabar palon su ammy na mara masa baya hankali tashe musamman sultana da a sashenta suke shaf tashin hankalin abeel hassan yasa suka mantasu acan.
Sultan kuwa numfashi ya sauke cikin wani irin yanayi ya miqe tsaye idanuwansa na canzawa.
Suhailat na zaune tana shan magani daqyar sbd ciwon ciki da jirin datake fama dashi tun safiyar yau din
Jakadiya ta shigo mata.
Murya na rawa tace,
Ina neman afuwar saqon baqin cikin danazo dashi Allah yakarbi ran jemaal……..
Bata qarasaba suhailat ta miqe tsaye atake jini ya 6alle mata ta yanke jiki ta fadi.
#mamuhgee