MATAR UBA COMPLETE

MATAR UBA 33

 

????????????????????????????????     *MATAR UBA*

????????????????????????????????

Daga Alkalamin ✍️

      

       *Milly*

                   Fadilah Yakub

                 *(MILHAAT)*

*????MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION????????️*

                   *M. W. A*

 *Bismillahir Rahmanir Rahim*

CHAPTER 33

Not edited

Duk suka yi dariya amma Banda Safiyya da kunya duk ta rufe ta dama tun shigowar ta ta lura da irin kallon da yake Mata.

Sai da Hashim ya kwana ya wuni aka salleme shi.

Safiyya ko da wasa ba ta Bari Baraka ta gano ta ba,abinda ta daina shine ta daina Shan wani abu da duk zata bata.

????????????????????????????????

…………”Hashim kana ganin baza ka nemi auren Diyya ba,in yaso idan kuka gama da matsalar Baraka sai a d’aura Muku Aure da Asiyah?”

Gyara Zama yayi yace

“Hakane mom Amma ni dama niya ta a d’aura auren Rana d’aya”

“A a a gaskiya hakan bai min ba,kaje ka samu kawun ka kuyi magana in yaso a safe Rana Nan da watae d’aya”

Murmushi yayi yace “Wata ‘daya mom da wuri haka?”

” Eh to me zaka jira? Tunda Allah yasa ba a d’aura a baya ba Kuma yanzu Kun dai daita ai sai a samu a d’aura kowa ma ya huta”

“Shikenan mom zanje na same shi jibi”

“Har jibi? Gaskiya yayi nisa, goben Nan nake so kaje”

“Toh Allah ya kaimu goben”

“Ameen”

Wayar sa Ce ta Fara ringing, dubawa yayi yace “Faisal ne,na manta ma yana jira zamuje gun amaryar sa”

“Faisal kuma da Amarya?”

“Eh gun Yesmin ba”

“Waya aura Masa Yesmin din?

“Za a d’aura ai soon Insha Allah”

“Hmm to Allah yasa,Amma Anya Khamal zai amince kuwa?”

Yar karamar dariya yayi yace “Tab mom ai an Riga  wuce gun, tunda har anyi musu engagement.”

Dariya tayi irin tasu ta manya Tace “Kai bana son shirme”

“Allah kuwa mom dagaske nake”

“Toh Allah ya tabbatar da Alhairi”

“Ameen,bara naje na same shi, kin San tunda na fara zuwa office bamu cika samun Zama ba”

“Hakane”

Mikewa yayi yace “sai ba dawo”

Ta amsa da “A dawo lafiya”

“Allah yasa”

Yana fita ya shiga motar sa,sai orji quarters Yana shiga gidan ta tarar da Faisal da Farees a zaune suna zaman jiran sa.

Wuri ya samu ya zauna bayan sun gaisa Faisal yace “Ya to mu wuce ko?”

Farees yace “Dad’i na da Kai azar’ba’bi, gidan su yarinyar Nan fa a Nan Nan tumfure yake Kuma da mota zamuje ba da kafa ba Kar ka tada mana hankali”

Baki a Bud’e Faisal ke kallon farees bai ce umfan ba har sai da ya ida maganar da ke bakinsa, ya ce “Amma ka bala’in raina min wayo ai gara ni akan ka,Kai da duk kwanan duniya sai ka had’u da Safiyya bayan Kun had’u ka kirata a wayae harda video call, Amma kana da bakin magana”

“Anyi video call da Kiran idan kaji haushi kaima kayi Mana”

“banji haushi ba,Kuma ka na zaman ka,zaka sha mamaki”

“Mtwsss ayi dai mu gani”

Hashim ba abinda yake yi banda dariya sai da yayi Mai isar sa harda rike ciki,cikin dariya yace “Guys guys ya Isa haka please ku tashi mu tafi please na roke ku”

Mikewa sukayi ba tare da sun ce dashi kala ba,hannun sa duk biyu yasa a aljihun sa Yana kallon su yace “da Wace motar zamu?”

Babu Wanda ya kulashi sai gani yayi tun nufi motar sa, ‘daga kafad’a yayi irin ko a jikina d’in nan  duk su ukun suka shiga hafeez ke jaan motar yayin da farees yake zaune a gaba,Faisal Kuma na baya.

Babu Wanda ya sake magana har suka Isa gidan su Yesmin, horn ya danna aka Bud’e musu gate d’in Yesmin bta window ta leka taga fitan su,tsalle ta daka hakan yayi dai dai da shigowar Nana d’akin,hab’ar ta ta rike Tace “Oh ni yarsu Yaran yanzu ko irin kunyar Nan ma Babu,Allah ya kyauta”

Yesmin kuwa darya ta yi Tace “Mummy ban San kin shigo bane”

“Ina Zaki sani ja’irar yarinya kawaii”

Sosa keya tayi “Mummy kin San…….” Bata karisa maganar ba wayar ta,ta Fara ringing dake ta San Mai Kiran nata ta zari gyalle ta fita cikin sauri.

A garden na gida ta tarar dasu ko wannen su wayarsa yake dannawa, da Sallama ta karisa inda suke suka Masa sannan ta zauna bayan sun gaisa Tace “Yau lafiya na gan Ku Shiru yau Babu Yar surutun da aka Saba?”

Murmushi Faisal yayi yace “Wallahi kuwa Yan surutun sunyi nisa ne shiyasa”

Farees yace “Uhmn hashim taso muje gidan su Safiyya please idan sun gama sai mu dawo mu d’auke shi”

Hashim zaro Ido yayi yace “Gidan su Safiyya fa kace? Wai kana nufin kai ma na maka rakiya ni Kuma in zauna ina kallon ku?”

“To me aciki? After all ai Asiyah na gidan”

“Kana magana kamar baka San me ke tafiya ba,Aunty Baraka fa na nan, idan ta ganni da Asiya to plan d’in mu ya lalace”

Yesmin Tace “Ai mummy Baraka tayi tafiya bata Nan”

Hashim da Farees a tare sukace “Haba dai?”

Yar karamar Dariya tayi tace “Allah kuwa”

Gani sukayi Hashim ga mike ya nufi inda sukayi parking motar su, Faisal yace “Au na d’auka baka son zuwa ne?”

“Waigowa yayi  yace,inji wa ai Wallahi da hakuri kawaii na fiku”

Yana maganar Yana tafiya,Yana Shiga motar ya sa Mata key yana yiwa Mai gadi horn tun Kan ya Isa gate d’in.

Farees ganin Hashim zai iya tafiya ya barshi yayi saurin Shiga motar Shima, Yesmin da Faisal dariya sukayi suka Fara hirar su irin ta masoya kana ganin su kasan masoyan Nan na matukar son junan su.

Zaro waya yayi ya Kira Asiyah tana picking yace “Nayi fushi”

“Yi hakuri rankashidad’e laifin me nayi?”

“Au Baki ma sani?”

“Gaskiya ban sani ba, Dan Allah me nayi?”

“Ashe mummy Bata gari Kuma baki fad’a min ba?”

“Wace Mummyn?”

“Mummy Baraka Mana”

“Oh Anya kuwa tana Nan fa,wa ya fad’a maka bata gari?”

“Daga majiya Mai Karfi”

“To ni Wallahi ban sani ba, Amma bari na tambayi Safiyya”

Katse wayar tayi bata d’au lokaci ba ta kirasa tace “gaskiya ne bata Nan”

Murmushi yayi yace “okay gamu Nan zuwa”

” Kai dawa?”

” Ni da farees zai Zo ganin Safiyya”

” Okay sai kunzo,kamar kasan dama nayi kewar ka”

“Baki kaini ba tun fa da aka sallameni a asibiti ban sake ganin ki ba, yanzu kimanin wata d’aya Kenan”

Murmushi kawaii tayi Tace “Sai kunzo”

Ya amsa da “Okay” ya katse wayar.

Komawa d’akin Safiyya tayie ta Sanar da ita cewar suna zuwa ai kuwa da Rawar jiki ta Fara Shiri, bayan sun iso a tsakar gidan suka zauna suna Shan hirar su duk a tare, sun dad’e suna hirar har Saida Faisal ya Kira farees a waya akan ya gama su yake jira.

Farees yace “Nifa ban gaji da kallon gimbiyar tawa ba Kai har ka gaji?”

Tsaki yayi ya kashe wayar, shi ko farees dariya ya Shiga yi, Hashim yace “Kai da fai…..” 

Kan ya karasa maganar Sai Kiran Faisal ya shigo wayar Hashim yana picking yace “Zaku dawo Nan ne ko na tafi?”

“Gamu Nan” 

Bai ce komai ba ya katse wayar, Hashim yace “Dad’i na da Faisal saurin Hawa yake”

Farees yace “Ni ai Dad’i nake ji in yi ta kunna shi”

Tab’e baki Hashim yayi yace ” Kunfi kusa” had’e da mikewa yace “Mu zamu tafi” duk su hud’un suka nufi inda sukayi parking.

“Asiya ke Wace irin shashace,baki da hankali ne kina ganin mutane na magana kizo ki Samu a gaba kina kallon” Safiyya ke wannan maganar a tsawace, cikin rashin fahimta duk su ukun suke kallon ta, sunkuyar da kanta kasa tayi cikin rad’a Tace “Mummy ce ta shigo Kar ku bari ta gane”

Sannan ta sake d’aga murya Tace “Sweetheart Dan Allah ka fad’a wa yarinyar nan cewa baka sonta yanzu Ni kake so,Kuma wurina kazo ba gunta ba.”

Gyaran murya yayi yace “My dear karki damu da duk wani abunda zatace Ni ke nake so Kuma ke zan aura,to me na tada hankalin?”

“Ai gani take kamar na mata snatching ne”

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button