NOVELSUncategorized

WUTSIYAR RAKUMI 33


*_Ummukulsoom a birnin ikko karo na biyu_*

        A wannan karonma isowar ,dare sukayi, babu abinda ke fita a fuskar Ummukulsoom sai murmushin takaici, da tuna shekara biyar da wasu watanni da suka shuɗe, ta shigo garin a matsayin matar cushe a wancan karon, ta barsa a matsayin bazawara, yanzu kuma ta dawo cikinsa matsayin mai neman ilimi, fatanta ta fita a matsayin mai tarin nasarar cikar burinta.
      Maman Ahmad dake kallonta itama tai murmushi tana nuna ma Attahir ita.
     Murmushi shima yayi kawai, ya tabbata tana tuno waɗancan shekarun  ne da suka shuɗe.
    Ɗaukarsu akazo yi, Attahir da maman Ahmad suka shiga mota ɗaya, Ummukulsoom da Bily ma suka shiga ɗayar.
       Tunda suka shigo Barrack ɗin Ummukulsoom ta fahimci wasu canje-canje da aka samu masu yawan gaske, su Attahir dai suna nan gidansu data sani, sai dai kayan ciki da aka canja.
     Sam hana dukkan tunani mai alaƙa da tuna baya tai yay tasiri a kanta, ana basu masaukinsu ma itace ta fara shirin barci ta kwanta ba tareda ta nema abinci ba, dan sam batajin wata yunwa.
         Bily ma dai shirin barci tai tazo gefenta ta kwanta suka lula duniyar barci hankalinsu kwance.

     Washe gari da safe da taimakonsu maman Ahmad ta gyara gidanta tsaf ya dawo nomal kamar yanda take buƙata, bayan sun kammala breakfast Attahir ya fita ya barsu suna hirarsu.

★★★★★★

       Kansa tsaye gidan Amaan ya nufa da ƙafa, yay sallama a falon da yake tsit babu motsin kowa, ko kaɗan bai kula da Amaan dake zaune a dining yana karyawa ba, shiko tun shigowarsa ya gansa, amma yaki magana, saima ɗauke kansa da yay ya cigaba da cin abincinsa.
    Sai da yaga Attahir zai nufi bedroom ɗinsa sannan yace, “Kai kuma fa?”.
       Juyowa Attahir yay ya kalli dani ɗin, “Oh ashe ga gwairon nan zaune yanacin girkin ƙato”. ‘Attahir ya faɗa cikin jan magana’. 
    Sai a kai sa’a Amaan ɗin bai tanka ba. Kujera Attahir yaja ya zauna shima, “Su Ajiwa masu guduwa, to laifin da kaine yasaka tserowa kana tsoron na maka hukunci ko?”.
        Shi kansa baisan murmushi ya suɓuce masaba, duk yanda yaso ɗaukar zafi da Attahir baya iyawa, ya ɗago manyan idanunsa akan Attahir, “Wai kai bazaka canja bane ba?”.
       Dariya Attahir yayi shima yana kallonsa, “Ajiwa inhar baka canjaba ya za ai nima na canja, shikenan saika gudo ka barmu bayan kuma tare mukaje”.
       “Share kawai Attahir, ya ka baro mutanen kd n?”.
      “Kowa lafiya yake”.
 “To Alhmdllh, ga abinci”.
         “Wa? Kaima kasan wannan ganganne Ajiwa, inada matata na zauna cin girkin ƙato, wannan sai ku gwauraye”.
       “Kai dai ka sani mara mutunci kawai”.
    Dariya Attahir yayi, yasan dai ƙarshen zancen kenan, babu wanda ya sake magana a cikinsu har  Amaan ya kammala cin abinci suka dawo falo, abinda ya shafi aikinsu suka cigaba da tattaunawa, tareda shirye-shiryen ƙarin girman da ake shirin ƙara musu. Koda wasa Attahir bai sanar masa da zuwan su Bily ba.

       ★★★

     Tsawon satin su Ummukulsoom uku a cikin Barrack ɗin ALLAH bai taɓa haɗata da Amaan ba, harma ta fara zuwa makaranta.
       
     Yau ta kasance Alhamis, da wuri Ummukulsoom ta dawo gida saboda lecture ɗin safe tayi, akwai abokin su Attahir Bello matarsa ta haihu, gidansu kuma yana maƙwaf taka da gidan Amaan ne, lokacin da Ummukulsoom ta dawo daga school ta iske Maman Ahmad da Bily sun gama shirin tafiya gidan sunan, ita kaɗai suke jira, ganin zata ɓata musu lokaci sai Ummu tace suyi gaba, ita zata taho tare da Ahmad idan an ɗakkosa daga makaranta.  
     Tafiya sukai kuwa suka barta a gidan ita kaɗai, wanka tai ta zauna taɗanci abinci, tana zaune a falo saiga Ahmad ya dawo.
      Oyoyo tai masa ya faɗa jikinta yana mai jin daɗin ganinta, yaron akwai wayo sosai.
     “Aunty ina su Mama?”.
 “Sun tafi gidan suna Amadina, muma yanzu idan kaci abinci zamuje mu samesu”.
     Tsallen murna ya farayi jin za’aje yawo, itakuma tana masa dariya.
     Wanka tai masa ta shirya sa tsaf yay ƙyau, sannan ta nufi ɗakinsu itama ta shirya baƙar jallabiya da akai mata ado da farin zare dayaji stons, ɗan ƙwalin kawai ta naɗa ta riƙe waya da handky a hannu, sai takalmin ƙafarta fari flat, tayi ƙyau masha ALLAH.
      Kulle gidan tayi ta kama hannun Ahmad suka tafi cikin nutsuwa, tunda ta fito daga gida gungun matasan sojojin suka zuba mata idanu, kowa na yaba halittar ubangiji a ransa, itako ko sashen da suke bata kallaba, tafiyarta take kanta tsaye Ahmad na mata surutu tana murmushi. Ba taɓa zuwa gidan tayiba, amma maman Ahmad tace tai mata kwatance, tareda cewa ko Ahmad tacewa suje gidansu abokinsa Sulaiman zai kaita, kuma ma ai tunda taron suna ake zata gane.
    Tsayawa tai daga tafiyar da takeyi ta kalli Ahmad, “My Amadi wai kasan ina kuwa zamuje?”.
     “Eh Aunty, ba kince gidan su Sulaiman abokina ba”.
     “Yauwa yaron kirki ashe baka mantaba kuwa, muje to”.
     Ci gaba sukai da tafiya, kasan cewar Ummukulsoom taga da ɗan mutane a wajen ɗai-ɗai kuma ga fararen kujeru da aketa shiryawa sai tabi Ahmad kai tsaye inda yake jan hannunta. Dukda ta zauna a Barrack ɗin bazata ƙarar da komaiba tunda a wancan lokacin bawani yawo takeba sosai, sai gidan maman Ahmad, shima zata iya irga zuwanta gidan kuma.

★★★★

         Zaune yake barandar gaban ƙofar falonsa, irin doguwar kujerar nance da akan ajiye a gaban ruwa, sai dai wannan mai taushice kamar nomal kujera, sanye yake da wando 3quarter na kakin sojoji, sai farar t-shet, gaba ɗaya hankalinsa ya tafi ga lap-top din dake a kan cinyarsa.
      Sam Ummukulsoom bata lura da shiba, sai mamakinma jin gidan da tai tsitt babu hayaniya, a ganinta ai bai kamata aji gidan suna haka ba, jitai kawai Ahmad ya ƙwace hannunsa ya shilla da gudu yana faɗin “Big Daddy”.
      Amaan da yaji muryar Ahmad ya ɗago da mamaki, sai idonsa suka sauka akanta, dai-dai itama ta ɗago dan son ganin wanene kuma Big Daddy? Ina Ahmad ya kawosu ne?.
       Tuni dukkan murmushin dake shinfiɗe a fuskar Ummukulsoom ya ɗauke gaba ɗaya, ɓacin ran ganinsa ya maye gurbinsa, gashi ta kasa janye ƙwayar idanunsa daga cikin nata, hakan shima ya kasa janye nasa duk yanda yaso, saima zuciyarsa dake wata irin harbawa da ganinta………….✍????


*_Jiya saida na gama typing tsaf nazo zanyi posting na danna delete by mistake????, har ƙwallan takaici nayi, ahiyyasa kuka jini tsit, gashinan dai na yau kam ko editing babu????????????‍♀️_*


_ZAFAFA BIYAR MASU ZUWA A HALIN YANZU????._

*ƊAURIN ƁOYE!* (Safiyya Huguma
*SAUYIN ƘADDARA!* (Hafsat rano)
*KAI MIN HALACCI!* (miss xoxo)
*BURI ƊAYA!* (Mamu gee)
*WUTSIYAR RAƘUMI..!* (Bilyn Abdull)

????????karku bari ayi babuku

*ga mai buqatar littafan zafafa biyar dukansu ko wasu daga ciki sai ya biya 500 ga dukka litattafan,ko 200 ga littafi  daya,ko 300 ga littafi biyu,ko 350 ga liitafi uku,ko 450 ga littafi hudu*

*za’a tura kudin ta wannan accnt number din*

Hafsat kabir umar
0225878823
GT bank

Saika tura shaidar biya ga wannan number

08030811300

Ga masu turo da katin waya kuma zaku tura katin MTN  ta wannan number din

07067124863


*_ƴan Niger kuma_*

_ZAKU BIYA NE DA KATIN;_
*_MTN ko MOOV_*

*Novel 1 Naira 200 = 350fc,*
*Novel 2 Naira 300 = 500fc*
*Novel 3 Naira 350 = 550fc*
*Novel 4 Naira 450 = 750fc*
*Novel 5 Naira 500 = 850fc*

 _TA NUMBER;_
 *+22795166177*   


Da zarar kin biya kai tsaye zaki tsinci kanki cikin gidan da zaki samu littafin da kika biya.


*Karki bari ayi babu ke, Abari ya huce shike kawo rabon wani????????????????????????????????



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*????????????

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button