AMANA TA CE 1-END

AMANA TA CE Page 31 to 40

Haka suka yi ta hira kulum ammar sai yaje dako ganin ba zai fiddasu ba ya nimi gurin mai sai da kayan fruits da kayan miya suka fara sayarwa yazana yaro agun nan ya na dan samu har mutu min ya kaisa gidansa da ke bayan winti market daki biyi ne daya ciki da falo shida matarsa sai daki daya karami ba ko flasta su ammar ke ciki kulum matarsa sai tasa auta aiki gata da kazanta auta bata iya gani sai ta gyara gurin wanki yaranta tace sai tayi tun auta bata iya ba harta saba ko kadan bata fada ma ammar ba don zai iya cewa su bar gidan ita kuma bata so suyita yawo a titi wataran tayi kuka ta share hawayenta haka tayita hakuri gashi abinci dan kadan take bata kamar na dan yaro karami sai dare ammar ya somata na ma da madara haka sukayita rayuwa kwanaki sun wa watanni sun tafi har sun kai shekara a bauchi ba abunda ya canza sai baki da sukayi da ramakam akwaisa duk da ammar na iya kokarinsa akan auta duk abun da yasan zai mata kyau sai ya sai mata har yasata a wata islamiya dake bayan unguwan tana zuwa, shiko riga mai kyau bai damu da kansa ba wataran har mita take masa kayansa kala uku rak itako ya cikata da kayan ado duk iya samu kudi ma ita yake kashewa hakan yasa sa’dat shiga tashin hankali don mijinta baya kashe mata kudi haka gashi yaron hannunsa yana hidima wa kanwarsa nan take lbr wa makwabciyar ta tace ke sa’adat bazaki ganeba ne haka kurum zai na kashe mata kudi batare da yana latsata ba daki daya fa suke kwana in baki shawara yau ki fito ki lekasi kigani nan suka tafa sukayi shewa hakao akayi daddare ta fito cikin rashin sa a taga ammar a waje yake kwana auta tana ciki sai datayi haka har sau uku awajr take ganinsa sai randa akayi ruwa shine taga ya kwana a daki ko da taleka taga shi yana bakin kofa auta na karshen daki ba haka taso ba amma tsabagen makirci irin nata nan tafara habaici ma auta akan ammar na aikata masha’a da ita ranan tayi kuka amma ta danne bata fada ma ammar ba

 don tasan yana da zuciya sosai haka sukayita rayiwa abunu tausayi.

Abangaren ammar kuwa kasuna tafiya dai2 har yayi customer a kwai wata hajiya datake yawan sayan kayan salad da fruit agunsa da vegetables har sun saba wataran kam yarta take turowa tasaya agunsa hakan dai yaci gaba da dana’arsa, auta ko sai rama take kulum in yasata a gaba yana tambayanta tace bakomai haka zai gaji ya kyaleta.

              * * * * *

Zaune yake a gaban kayan fruits wata bakar HONDA CRV TA cike da nuna isa da gadara take taku tun daga nesa mutane ke kallonta sabida ta tafi dasu ga ta da kyau tafiya take kamar bazata taka kasa ba kai daga ka ganta kasan naira ya zauna ma iyayenta da fatarta sannu a hankali ta tsaya tana kallon yar fruits don ita bataga wanda mum tace tazo gunsa ba har taxo zata juya ta hango wani dogon saurayi fari mai kyau tamkar sharukan kalo daya za kamasa ya tafi da tunanin mace don daga ka gansa kasan baragon namiji bane kuma mijin nuna ma sa’a ne kasa kyafta idonta tayi akansa shiko bai ma san anayi ba wai kunu a wani gida, ko tan tama babu shine Ammar din da mum take sayan kaya a gunsa, woow amma guy din ya hadu matsalar daya ne rashin naira sai da taji wani mai saida fruit na gefen ammar yana cewa hajiya kaya za a baki kafin ta dawo tunaninta a gadaran ce ta isa gun ammar tace aslm ya kk tambaya nake wai wani shi ammar fiska ba yabo ba fallasa yace eh nine ammar din lfy cikin isa tana satan kallonsa tace hajiya Maryam Alkali ne ta aiko ni wacce take sayan kaya a gunka yace ok ina jinki nan tace wai ka hada mata kaya kamar yanda take saya nan Ammar ya hada mata kaya masu kyau ta bude jaka ta dauko kudi ta basa tsabagen kallon da take masa ta yarda posd din ta garin mayar wa jaka bata sani ba sai da ta bar gurin zuciyarta cike da tunani ammar har ta tada motarta ammar yaga poss ya bita amma ina tayi nisa nan ya budr sai yaga ID Card dinta da dunanta Munayshat Alkali nan yaga complement card dinta da address dinta da sauri ya tsari mai mashin ya bi bayanta.

1 To masu karatu danso musan wacece Munayshat? Kuma wacece Hajiya Maryam Alkali?

2 Shin munayshat son Ammar takeyi zai amsa kuwa to ya rayuwan auta zai kasance

Kubiyo Yar gidan JARAWA don jin yanda zata kaya taku a kulum mai kaunarku Yar Mutanen Kardam.

®WISDOM HAUSA WRITERS

Rash Kardam

[7:38PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE

                        By

©Rasheedah .A. Kardam

   

               ®WWA®

                           

Ganin tayi nisa yasa ya bi bayanta da gudu sukeyi da mai mashin amma ta musu nisa sai da sukaje G R A adjacent da government house naga naga sun nufi wani katon kwalta ne a shimfede kafin suka iso kofar wani hadadden gd harda security a kofar ginan tun daga kwanar shiga gidan zaka ga arubuta Hajiya Maryam Alkali house, da manyan zane, nan ya sallami mai mashin ya basa N100 kudin mashi mai gadi suna ganinsa suka tashi nam sukace wajen wa yazo yace gurin wacce tashiga da mota mai gadi yace ka bar gurin nan bazaka shiga ba nan suka fara iskanci ma ammar ransa har ya baci ya juya zai tafi sai daya mai gadin yazo ya tambayesa nan yace wacce ta wuce da mota yanzu baka mai gadi yace ai gidan nan masu tuka mota suna da yawa nan ya sake duba sunan yace Munayshat ok lfy dai ko yace lfy wa za a ce mata nan yace ace Ammar mai kayan fruits nan security ya shiga nan yayi karo da Aunty Mamu a falo ga Kausar a gefenta nan yace Aunty wani ne yazo gun munayshart wai Ammar mai sayarda fruit nan hajiya maryam ta fadada murmushinta ayya ammar lfy daiko yace eh wai abu yakawo ta nan aunty mamu tace kaje ka shigo dashi, kausar mikewa tayi ta nufi kitchen don dauko mult mai sanyi tasha,

Bayan ya koma ya shigo da ammar gasky gdn ya tsaru a kwai naira a gdn sosai don ya hadu iya haduwa da sallama suka shiga cikin falon da yasha blues da yellow da bakin labule ga kujeru luntsuma luntsuma suma colours din blue yasha gyara ga kamshin da yake tashi ya duka ya gaida ta nan yace shaidata mata yarta tazo sayan kaya gashi ta yar da poss dinta nan tayi godiya ta karba hauwa mai aiki ta kira tace ta kawo masa abinci yace ya gode hajiya ta bata rai ammar ae mun zama daya ka dauken tamkar uwa a gunka cikin jin dadi yayi godia hauwa ta kawo masa zobo daman shi ma aboci zobo ne ya sha kayan hadi nan ya dauka ya sha gashi da sanyi nan ya wani lumshe ido alamar jin dadi,

      Kausar ta fito rike da malt a hannunta tun da ta nufo falo ta hangi wani hadadden saurayi ajin karshe ga kyau sai da ta furta woow a zuciyarta nan take taji ya tafi da ita amma jin kai ta danne ta shigo da sallamarta dake ita tana da hankali sosai ta gado halin Aunty Mamu ne gefen mum dinta ta zauna cikin isa tace masa sannu da zuwa yauwa yace a takaice dai2 nan munayshart ta shigo cikin wasu matsatsun kaya riga da wando na English wears tayi kyau sosai don suna da kyau ba laifi sai dai matsalar rashin gashi don sai da ta hada dana doki tun da taga ammar tashiga wani yauki tana karairaya wanda shi bai san tanayi ba ma nan Mamu ta bata poss dinta nan tace la ban lura ba ko da ta bude taga kudinta ba a tabasu ba 80k ne a ciki don harda zonen gwal dinta da yakai 60k aciki kirar dubai sai daukar ido ya keyi nan tace lah mum gsky na da AMANA kiga ga kudi kusan 80k ga zobe na nagode duk da nasan koda bata sukayi banda wasu matsala amma gsky da kanuna naji dadi nan ya mike da nufin tafiya cikin sanyin murya yace hajiya zan tafi tace angode kausar kam kasa motsi tayi sabida zakin muryansa amma dake ita tana da kamun kai ga jan aji shiyasa take buyewa har ya kai kofa Aunty Mamu tace Ammar in bazaka damu ba ina son zan tambayeka cikin ladabi yasoma takowa ya dawo in da ya zauna ya sake zama kansa a kasa ammar dan Allah ina son kafadan gsky waye kai daga ina kake don daga alamar baka dade da fara sayar da fruit ba don na dade ina zuwa gun bana ganinka san nan yanayinka baiyi kama da wahala ba a kwai wani boyayen sirri atare da kai cikin nutsuwa ya daga fuskansa nan suka hada ido da munaysharr da ke wurga masa shu’umin kallo Kausat ma kallonsa ta keyi ajiyar zuciya yayi kafin ya sake sukiyar da kansa cikin nutsuwa ya fara magana.

1 2 3 4 5 6Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button