ABBAN SOJOJI BOOK 2 COMPLETE

ABBAN SOJOJI BOOK 2 COMPLETE

A cup biyu ta haɗa musu sannan ta haɗo masu da snacks suka zauna suna sha suna fira, ❤
__________AUNTY BABBA________________

Suna cikin wannan fargabar wayar hafsat ta sake yin ringing, cikin hanzari tunkan tasa hannunta ta ɗauka aunty babba ta riga ta ɗaukar wayar asaman cinyarta, a tunaninta Omar ne amma tana dubawa taga Sunan My Dad ya bayyana, ɗagowa tayi ta kalli hafsat hankali atashe tace “Abbanki ne ke kira, Allah yasa dae ba dawowa zaiyi ba, ya salammm ni bansan meke faruwa dani yau Ba
Hannu hafsat tasa ta kar6i wayar, ta amsa kiran sannan takara a kunnanta tana zabga Sallama,
Janar ishaq ya amasa mata da cewa “Wa’alaikum salam my daughter, ina mommynki take ne, i ave been trying her phone number tana ringing ba’a ɗagawa why”? Ya tambaya yana jiran amsa,
Murya na rawa hafsat tace “am..dama…umm…tabar wayar a ɗaki ne ina ji, saboda ta shiga kitchen,
tayi maganar tana kallon mommyn nata data ke faman dafe zuciya,tana sauraron mai zai ce saboda wayar na a handsfree,.
Genar ishaq yace “shikenan ki sanar da ita cewa cikin week ɗin nan zan dawo insha Allah,”.
“Shikenan daddy Allah ya dawo daku lafiya,” sukayi sallama ta ajiye wayar tana faɗin “Tabɗijan Can akwai matsala fa,”
Aunty babba kuwa miƙewa tayi tana faɗin “Nashiga uku ishaq zai dawo ga zuwan Omar yau, bansan me zan fuskanta ba a wurin kowannan su… ‘.
Muryar hafsat ce ta katse ta da cewa “Amsar fa abayyane take mommy, ke ma kin sani Allah,saki ukun nan sun Wajaba Akan ki muddin Abba yaji abunda kika aikata, saboda wancan karan Ladi mai aikin mu da kika ma bugun mutuwa sai da ya aika ki maiduguri bayan marukan da kika sha awurinsa ina ga waɗan nan bayin Allahn da kika naƙasa har Su biyu, gasky mommy kin shiga Uku, ga kuma ƴa Omar zaizo ni addu’ata Allah yasa Abba kada ya sake ki yabarki kawai da hukuncin Omar na zuwa prison kowa ma ya huta…..
Hankali tashe aunty babba tace”Hafsat prison fa kika ce? So kike akaini can kin gaji dani kenan”?
Rai a6ace hafsat tace “dole nagaji dake mommy, duk ke kika ja mana wannan masifar da muke ciki muna zaman lafiyar mu,’ ta faɗi a ƙuke hada buga tsoki kamar bada uwarta take magana ba,

Jinjina kai aunty babba tayi batare da tace komai ba, adai dai time ɗin dr ya fito daga ɗakin da aka kwantar dasu hosana, jiki na rawa tabishi tana faɗin “dr ya jikin nata ta farfaɗo,”?
dr yace “Alhamdulillah tafarka yanzu haka bacci take yi itama saboda allurar da nayi mata,”
ɗaga hannu tayi tana cewa “Alhamdulillah har naji ɗan sauki, amma dr babu yarda za’ae ciwon fuskarsu ya warke nan take? kumburin ya sa6e, ni dr kodai surgery za’ae musu ne acanza fuskar,’ tayi maganar in serious matter tana kallon shi,
Wani irin kallo dr ɗin ke yi mata yama rasa amsar da zai bata,
wuce wa gaba yayi ya tunkari Office ɗinsa yana cewa “sam Bazaiyiyu ba gsky,ba muyin irin wannan aikin anan, kuma fuskarsu batayi komai ba da za’a canza musu Ba,da alama madam kema kina buƙatar Aduba ki,’ sarai taji abunda dr ɗin yace amma bata ji zafin maganarsa ba, saboda bata cikin natsuwarta a yanzu,

Yini su kayi cikin fargaba ba salla ba salati dama ba ita bace agabansu ba, an saba haɗa salloli ayisu a lokaci guda,Saboda duniya aka sa agaba Ba lahira ba,

gajiya su kayi gaba ɗayansu da zaman asibitin ga uwar yunwa kamar suyi hauka, ga zullimi da fargabar zuwan Omar, ganin har Magrib tayi babu kiran Omar yasa suka fidda tsammani da zuwan shi,
Ƙarshe basu jira dr yayi discharge ɗinsu ba, aunty babba ta ɗauko hosana dake kwance saman gado agalabaice ta sa6o ta a kafaɗarta ta fito da ita, sai cikin mota ta kwantar da ita, Jahad ma tashiga motar baiwar Allah ga zazza6i tana ji, gashi dr yace suna buƙatar jini su duka biyun amma babu yarda zasu yi, rayuwarsu a tagayyare sai yarda akayi dasu,
Shiga motar hafsat tayi mazaunin driver aunty babba na gefenta suka ja motar suka bar asibitin, a time ɗin har dr ya biyo su da sauri sauri don ya dakatar dasu amma ina tuni har sun bar arean asibitin………….
A tsiyace ta shiga da motar cikin gidan tayi parking ɗinta, tana fito wa ta wuce ciki saboda jirin da take ji na yunwa, fitowa itama aunty babba tayi sam bata tsaya taɗauki hosana ba ta shige ciki itama,
Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba ganin sun tafi sunbar hosana kwance sai faman nishi take saki numfashinta na fita daker-daker,
bata son yaya zatayi ba ta ɗauke ta saboda itama babu sauran ƙarfi ajikinta, fitowa tayi daga cikin motar tana faman zubda hawaye, Iya cuta dae an cuci rayuwarsu,
Ganin yarinya tsaye abakin mota yasa wani soja ƙaraso wa yana faɗin “Lafiya dai ƴan mata meke faruwa ne,”
Cikin shessheƙar kuka jahad tace “ƴar uwata ce ciki kwance bata lafiya bansan yarda zan shiga da ita ciki ba,”
Sojan yace “Can I help”? Jahad tace masa “eh” saboda bata da wata mafita da ta wuce hakan,
Buɗe motar yayi ya zura hannunsa ya sungumo hosana dake kwance magashiyyan ya ɗaurata a kafaɗarta ya shige da ita ciki jahad ta bi bayansa,
A saman 3 seater ya kwantar da hosana, jahad tayi masa godiya sannan tasamu wuri daga ƙasa ta zuƙunna fuskarta na dai-dai saitin ta hosana,
Hawayen fuskarta har ɗiɗɗiga suke yi a fuskar hosana, addu’o’i tashiga karantowa tana tofa mata,.
Duk hosana na jinta tana so ta buɗe idonta amma ta kasa saboda kumburar da su kayi, tana so ta buɗe bakinta tayi ma Jahad magana amma tagaza saboda haƙoranta kansu sun raunata sosai don ba’a rasa mai girgiɗi acikinsu, ga la66anta da sukayi suntum sam bata iya motsa su,
Cikin kuka jahad tace”Hosana na sani nasan akwai abunda kike son faɗa mun amma kin kasa, kada ki damu ina jin duk wani raɗaɗi da kike ji azuciyarki, inaji inama ace zan iya ɗauke maki zafin ciwon da kike ji da tuni nayi wlh…….taƙarasa mgnr tare da kifa kanta ajikin hosanna,sun jima a haka wulaƙance babu wanda ya leƙo su, sai daga bisa ni hafsat tafito har tayi wanka da alama ta canza kayan jikinta, doguwar riga ce tasanya har ƙasa, ta ɗaure gashin kanta,
Binsu da kallo tayi gwanin ban tausayi ita kanta duk rashin imaninta yau ta tausaya ma twins ɗin,girgiza kai tayi tare da wuce wa ta nufi kitchen,
Jim kaɗan sai gata ta fito hannunta ɗauke da tray mai girma, Tea set ne ɗauke asaman shi, sai French toast ɗin da ta hado masu dashi da sauran snacks, duk da tasan ma daker zasu iya ci
Bedroom ɗinta ta shigar masu da shi ta ajiye Tray ɗin asaman table ɗin dake a dab da gadonta, Sannan ta fito ta nufe su jin takun tafiyar hafsat yasa jahad ɗagowa daga kwancen da take tana kallonta da rinannun idanuwanta da suka jigata,
Hafsat batayi mata magana ba hannu kawai tasanya ta cicci6i hosana ta ɗaura a kafaɗarta sannan ta wuce izuwa bedroom ɗinta tana cewa jahad “Ki biyo ni,”
Cikin sauri jahad ta tashi tabi su cikin ɗakin, kwantar da hosana tayi asaman shimfiɗeɗen gadonta, sannan ta juyo ta kalli jahad tace “Ga tea nan da snacks nasan kina jin yunwa ki ɗaure ki sha,’
Girgiza kai jahad tayi tana cewa “Bazan iya cin komai ba,
“Soboda me”? Hafsat ta tambaya tana kallonta,
Jahad tace “Sabodo ƴar uwata, bata ci komai ba,idan naci ita kuma fa”?
Shiru hafsat tayi jikinta yaɗanyi sanyi aranta har tana mamakin dama har yanzu akwai ƴan uwa masu ƙaunar junansu haka aduniya? Jinjina kai tayi kafin tace ” kada ki damu, zan ƙara dubata yanzu insha Allah,zata ji sauƙi,”
Shiru kawai jahad tayi,amma fa ba zancen Cin abinci agare ta muddin hosana bata ji sauƙi taci ba itama, sai dae yunwa takashe ta,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23Next page

Leave a Reply

Back to top button