Uncategorized

YAU DA GOBE 33&34

 YAU DA GOBE ????

????????????????????????????????????????


Wannan shafin nakine halak malak my k’awar Amana.. mmn nurul huda????


????️33&34

…..wani irin mugun kallo yake binta dashi” cikin fushi yanufota”

Yyinda sumayya takejin gabanta na dukan Tara Tara”amma saita dake tana tsaye inma dukanta zaiyi kawai ta arce..

      Kafin ya iso sallamar Dr Nasir tadaki dodon kunnen ta…wata ajiyar zuciya sumayya tasaki had’e da k’aka’ro murmushi”ta amsa tana kallonshi Yana rik’e da hannun meena.”

     Wani haushi Dr safana yaji sbd Dr Nasir yakatse Masa abinda yyi niyar Mata”amma ganin Yana tare da matarsa dole yad’aga mishi”

     Fuskar

sa yasaki yana kallon meena dake k’ok’arin Zama da matashin cikinta”yace gsky madam munyi fushi”murmushi tayi had’e da Zama hannunta cikin na Nasir” tace tuba mukeyi”kasan laifin abokinkane ko?”Ina wuninku?”cewar zarah tana k’ok’arin fita”lfy qlau zarah yasu ummi?”cewar Dr Nasir”duk suna lfy”anty sumayya na wuce Saida safe!

Sumayya tace tun yanzun?”zarah tace eh tana fita”

     Sumayya ta  zauna kusada Dr safana tana musu sannu da zuwa…Dr Nasir kuwa ad’age yake kallon Dr safana sbd yasan k’arfin haline yake wannan fara’ar….kallo d’aya yamasa yagano ransa ab’ace yake…kallonsa yyi yace abokina yanaga Sumayyar kamar Bata murna damu ko mukomane?”

    Harararsa Dr safana yyi had’e da kamo hannun sumayya ya rungumota jikinsa Yana cewa kinji sharrin da abokina ke Miki ko?”

   Meena tace k’ila shiyaga hakan.nidai Banga komaiba.

Sumayya ta wani marairai murya had’e da aza hannunta kan nashi tace my lion!amma yakamata ace ba zuwan dare zasuyi manaba”

Haba Kisha kuriminki zatazo Miki yini”cewar Dr nasir..sumayya na murmushi tace Allah yasa to…ta yunk’ura ta tashi dg jikin safana ta wuce kitchen”drinks d ruwa da cups sai dambun kaji ta zubo a tray tazo ta ajiye agabansu.

   kafin ta zuba a cups ta mik’a musu…Mina tace sorry dambun ne yafi biyawa Raina..Dr Nasir yace oh wannan baby Yana samunke k’wak’wa wlh…

     Sumayya na dariya ta aza Mata bowl d’in dambun naman  acinyarta”kafin ta saci kallon safana yadank’ara Mata wata uwar harara”Dr Nasir na lura dasu”dama yasan abinda yafaru yanzun pretending d’insu ne…

      Amma fa sai yaga sunmishi kyau” fira sukeyi jefi jefi” har 9:30 tayi” Dr Nasir yamik’e tsaye Yana cewa meena” sweet heart yakamata mutafi gd ko?” Turo Baki tayi had’e da cewa nifa anan Zan kwana…dariyar rainin hankali  yasaki,kafin yace gaki g masu gidan…yo miye aciki inta kwana ko kuwa baby??” Dr safana ya fad’a Yana kallon sumayya” sumayya tace k’warai kuwa” meena tace rufan asiri tsokanarku nakeyi”gashi samin number d’inki ma ruk’a zumunci… sumayya n murmushi t karb’i wayar, tasaka Mata.

Kafin su fito”sumayya da Dr safana nabayansu suyi musu rakkiya.

     Tun kafin sutashi motar sumayya tayi musu sallama ta juya…maimakon t wuce part nasu” saita wuce part d’insu ummi…


Dr Nasir yadubi meena yace my dear pls bani 10 minit…ohk tace “shikuma yafito Yana kallon safana”

     Jansa yyi gefe suka tsaya”Dr Nasir yace wlh kaji tsoron Allah! had’e rai yyi yace kqmar Yaya kenan Mai tsoron Allah??”

Dr Nasir yace gsky dg Kai har ita duka kun iya pretending”wlh nazata komai ya wuce kun shirya kanku!danaga ka rungumota Ashe ba haka bane?”naga ka harare….look mlm dena wannan maganar”yanzun haka tamun laifin da saita gwammace dama bata aureniba….akqn hukuncin dazan mata..nan yasanar Masa komai…

Hhhhhhhhh????????Kai amma wlh tamun daidai!cewar Dr Nasir Yana rik’e ciki sbd dariya…


Tsqki Dr safana yyi had’e da cewa d’an iska kawai”


Eh naji”amma wlh wlh!!muddin kamata wani Abu saina gayawa ummi kaji na rantse!Wai meyasa bakajin shawara ne?


Drsafana yace Mekake nufi da fad’in hakan?”

     Bansaniba wlh sumayya bak’aramin hakuri takeyi dakaiba”sannan dukda kana karba’an hankkink’a agunta hakan be hanaka musguna mataba!

   Wani banzan kallo yamasa had’e da cewa k’arya kakeyi Ni bbu….kaidai ke k’aryar sbd ninazuba maka k’wayoyi a drinks kaji mugun feeling..sannan

Ina jiye maka ranar nadama wlh…Kuma kaji menace ko?ai meena nada number d’inta Zan karb’a na tambayi sumayya”muddin kamata wani Abu wlh duk zaman dakukeyi saina sanarwa da ummi…tsaki Dr safana yaja yyi tafiyarsa”Dr Nasir ya wuce yashige mota…


Directly part d’in ummi ya wuce yamata Saida safe….Yana shiga kawai yasami sumayya da zarah nacin indomie”ummi na kishingide kan kujera”can ciki yyi sallama”Yana Zama..wani mugun tsoro sumayya taji…batadai dubesaba kanta a k’asa”

Ummi tace yauwa babana muje nabaka sak’o…to ummi yafad’a Yana tashi yabi bayanta.

     Saidai yadda yaga fuskarta a’daure gabansa yafad’i”Yama gama yadda sumayya tafad’a ma ummi k’ila zai hukuntata…ka zauna kayi tsaye kana tunani…Zama yyi kan carpet”

Meyasa taurin kanka yyi yawane?”ummi kiyi hakuri Dan Allah”nifa bance zanmata komai ba kawai dai…ohk k’ila wata muguntar kamata yasa ta gudo ko?”to matar rufin asiri Allah yabaka!

Ni batace min  komaiba.tadai zo yanzun Muna kallo ta gaidani “nace lfy taxo da dare tace kafitane”ajiyar zuciya yasaki aboye”

    cikin fad’a ummi tace duk wulak’ancin dakake Mata zarah tasanar mun”sbd kanayi agabanta sbd bakasan mutuncin matarka ba ko?”Kuma wlh bance kayiwa zarah komaiba sbd gsky ta fad’a”abinda kakeyiwa sumayya in zarah ko y’arka akayimawa zakaji dad’i?”ince zainab antinku sbd miji da danginsa na wulak’antata akan bata haihuwa harda Kai ake magana akan araba auren…to wlh ka kiyayeni karka Bari damarka ta wuce”ita Kuma wacce ka k’wallafa ranka akanta”kaje ka aureta insun baka dama”ga fili ga Mai doki”sai ince Allah yabada sa’a”amma wlh wlh!!kaji narantse nasake jin makamancin haka dakaina zansaka kasaketa Kuma anan gdn zata cigaba da Zama!ma’ana nizan rik’eta”kasan Kuma hakan Yana daidai dasamun sab’ani tsakaninka da abbanku…. sannan wane ciwo ke damunta  dayasa Bata iya zaman kirki ko yanzun na lura da ita??”duk’ar da Kai yyi k’asa Yana sosa k’eya yace ummm ciwon basir ne yataso Mata”

     Hmmmm Allah ko?”to Bari kaji !inma baka jemata ta sauk’i wlh ka kula karkaje kajima ta ciwo kaji abinda nagamaka?”

Kansa aduk’e yace eh..tashi kabani waje.kaje kutafi”saura kamata wani abun….cike da jin kunya ya Mik’e yafita..Yana fitowa yasami sumayya ita kad’ai zaune aparlourn”

Batare daya kalletaba yace kitashi muje bbu abinda Zan Miki!har cikin ranta Bata yardaba”tunda yazo yace ga tsaka ta shigo d’akin ta”Ashe Kuma ba haka bane!

    Tashi tayi jikinta asanyaye ta bi bayansa”saidai kasancewar yafita dogon tak’i yasa ko hangosa batayi.

  Cikin fargaba ta shiga parlourn”Yana zaune kan kujera”ki wuce kidafamun indomie da serdine kafin nafito wanka”ki wanke hannunki kafin kifara sbd kina wannan k’azantar (period) batace komaiba ta wuce kitchen”alaokacin har10 ta wuce”

    Cikin 20 minit ta Gama ta ajiye mishi atsakkiyar carpet .ta ajiye drinks kafin ta wuce d’akin ta..

Wanka tayi had’e da addua ta kwanta…



*Washe gari*

Babu laifi taji jikinta normal bbu zafin nan ko rashin zama..tana jera break fast yafito cikin Shirin zuwa office”Zama yyi Yana Shan k’amshi”duk abinda yadace ta had’a mishi taturo gabansa”kafin tace Ina kwana?

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button