BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO 22

(Mi tsohuwar ga ke ƙullawa ne?????????)

    ★ A ɓangaren Fadwa kam maimakon gidanta sai ta nufi gidansu, dan ranta gaba ɗaya a mugun ɓace yake, ta tabbatar idan ta koma gidanta a haka tofa tanayin sallama jibgar Anam ce zata biyo bayanta. Mamah (Gwaggo Halima) batai mamakin ganinta ba, saboda babu jimawa suka gama magana da Gwaggo a waya, sai dai su dukansu babu wanda yay tunanin nan Fadwa ɗin ta taho. Hasalima kiranta take son yi sai gata. Kuka ta fashema Mamah da shi, dan haka ta tsaya tana kallonta kawai.
       “Wlhy Mamah sai dai na dawo nan da zama inhar akace sai ta zauna min gida. Ai dama tun farko haka mukai da shi zan zo nan na zauna har sai ya dawo, amma yana zuwa can gidan aka canja masa tunani, ni na gane Mommy da Gwaggo duk bakinsu ɗay…..”
       “K bana son shashanci, ke ko Fadwa wai sai yaushe ne zakiyi hankali ne? Idan an faɗa miki ki dinga saurara..”
  “Mamah dan baki san abinda ke faruwa bane fa, baƙar yarinyar can ɗiyar wancan mutumin na Malaysia fa aka kawo wai su tayani zama gida ita da Aysha. Na nuna masa ban yarda ba yana neman min azaba da masifarsa. Na faɗama Mommy amma Gwaggo ta nuna wai tanada shiri. Wane shiri gareta? Na fahimci tsohuwar nan bata sona kawai yanzun…”
     “Fadwa!!”
Mamah ta katseta a tsawace. …….✍????

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button