BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO 5

         Washe gari Abie yay shirin komawa. Anam ta zauna taita kuka itafa sai dai su koma tare. Yasan halinta akan kafiya, baiyi da wasa ba yay mata fata-fata, sai su Abba ne da aunty Amarya keta lallashinta da Ya Khalel. Shareff kam duk da yana wajen ko tari baiyiba. Yamaƙi nuna yasan abinda akeyi. Sai da zai buɗema Abie baya zai shiga ne ya harareta. Ƙasa tai da kanta ta sake fashewa da kuka.
        Daddy da yaga hararar Shareff na ƙoƙarin shiga mazaunin driver ya dakatar da shi. “Kaga ku wuce da Mamana tai rakkiyar itama”. Kansa ya duƙar ƙasa fuskarsa na sake tsukewa da satar kallon Mommy. Murya a rissine yace, “Daddy zanje wani wajene fa bayan airport ɗin”.
    “Sai ku tafi tare da ita tama huce kafin ku dawo gida”.
    Sosai takaici ya sake lulluɓesa. Sai dai baice komaiba. Daddy da kansa ya buɗe gefensa ya sakata dan Abie baya ya shiga. Koda suka bar gidan shi da Abie ne kawai keta hirarsu. Itako tai tsit kamar bata a motar, sai ajiyar zuciya take faman saukewa idanunta a lumshe sanyin ac na ratsata. A airport ɗin ma Abie shareta yay har sai da aka fara shelar masu tafiya a jirgin da zaibi sannan yaɗan fara lallashinta da ƙara mata nasiha. Daurewa kawai takeyi, amma ita dai bata ƙaunar zama a ƙasar batare da iyayenta ba. Da ƙyar ya ɓanɓareta a jikinsa domin amsa kira, tana ganin ya shige ta dirƙushe a wajen. Takaici ya saka Shareff buɗe motarsa yay shigewarsa. Jin ya mata key ya sata miƙewa da sauri dan ta tabbatar kaɗan daga aikinsa ya wuce ya barta a wajen.

      Sunbar airport ɗin kaɗan kiran Momy ya shigo masa. Idonsa ya ɗan rumtse kafin ya kai hannu ya ɗaga. “Kana ina?”. Ta faɗa tunkan yay sallama. “Mommy can gidan mana”. Ya faɗa a tausashe. “What! Al-Mustapha kana da hankali kuwa? Da wannan yarinyar kake nufin kaje?! To ina mai tabbatar maka maza ka sakota a napep ta dawo gidan ko ranka ya ɓaci bansan iskanci”. Ɗan jimm yay na sakanni biyu. Sai kuma ya ɗan saki murmushi. “Okay Mommy ba damuwa”. Numfashi ta sauke a hankali da faɗin, “Yauwa ko kaifa. Bana son wannan karon naji abinda bai minba kaga dai yanzu akwai banbanci da da. Ka kula ka bita a yanda take so dan ALLAH”. Nanma murmushin kawai yayi batare da yace komai ba, sai dai har cikin kunnenta tajisa dan haka tai masa sallama ta katse kiran. Wayar ya ajiye shima ya cigaba da tuƙinsa a nutse har suka iso.
       Da sauri ta waro idanu waje ganin inda suka zo, ta dubesa idanunta nayin ƙwal-ƙwal na tahowar kuka. “Yaya! nidai ka kaini gida bazanje wannan gidan ba”.
       Harara ya zuba mata, batare da yace komai ba yay parking a ƙofar gate ɗin. Sanin abinda zatai nan gaba shine roƙonsa ko guduwa ya sashi dubanta, “Haɗiyemin wannan silly hawayen banzan kafin nai miki dukan mutuwa a wajen nan”.
     Babu wasa a zancen nashi, dan haka ta haɗiye sautin kukan sai dai hawayen kam sun kasa tsayawa. Wayarsa data fara tsuwwa ya ɗauka, ganin mai kiran ya sashi ɗagawa da kaita kunne. “Ina waje”. Kawai ya faɗa tare da yanke wayar. Ko mintuna biyar basu gama cikaba Fadwa ta fito cikin yauƙi da yanga. Wando da riga ne a jikinta parkistan ƙirar Egypt. Sosai kalar kayan ya fidda mata ƙyawunta. Musamman yanda ƙaton gilashin data saka ya kusan mamaye rabin fuskar tata da haska farar fatarta. A hankali Anam taja guntun tsoki da ɗan laɓe baki. Sarai Shareff ya jita, sai dai komai baice mataba har Fadwa takusa ƙarasowa garesu.
     “Fita ki koma baya”.
Yanda yay maganar a dake batare da ya kalleta ba ya sata juyowa ta kallesa. “Are you daft?!”.
     Maganar tasa tayi dai-dai da isowar Fadwa jikin motar tana ƙoƙarin buɗe gaban ta shiga dan batai zaton ganinsa da wani ba ma balle wata.  Da sauri Fadwa taja baya saboda yanda Anam ta buɗe murfin a fusace. Saura kaɗan ta bugeta ma ALLAH dai ya taƙaita abun. Ko kallon inda take Anam bataiba tai ƙoƙarin barin wajen maimakon baya daya bata umarnin komawa. Sai dai kuma Fadwa tasha gabanta da sauri….
     “K! K! Dakata k! Ƴar uban wacece a motar mijina?”.
     Ba kowacce hausa Anam ke ganewa ba, dan haka a yanzun ma bata fahimci furucin farko ba hakan yasata kasa haɗa ma’anarsa dana ƙarshe da ƙyau. Amma a yanda Fadwa tai maganar ta tabbata ba’abune mai ƙyau ta faɗa ba. Wani banzan kallo ta watsa mata kawai dajan tsaki ta ratseta zata sake barin wajen. Hannu Fadwa tasa ta fisgota ta maidota baya a wani irin fusace, kasancewarta mutum mai saurin zuciya da son yanke hukunci sai kawai ta ɗaga hannu da nufin zabgama Anam ɗin mari………✍

Tofa babbar magana, wai ɗan sanda yaga gawar soja. Hajiya Fadwa daga ganin sarkin fawa sai miya tai zaƙi. To ku garzayo cikin tafiyar zafafa biyar domin ganin yaya wannan wasan zai kasance????. Dan tabbas akwai cakwakiya, idan nace cakwakiya ina nufin cakwakiya ƴar gaske. Yanda Fadwa take a tsaye Anam ɗin ma ba kanwar lasa bace. Littafine daya ƙunshi abubuwa da yawa. Rikicin zumunci, makirci, son zuciya, kishi, cin amana, kai harma da SARAN ƁOYE. Wasa ne kashi-kashi, dake da players daban-daban. Karku bari ayi babu ku, zafafa dabanne masoya, musamman na wannan ƙarnin da zasu zo muku a cikin zafi na musamman. Karna cikaku ku dai ku garzayo kawai.

_Dan girman ALLAH, dan girman ALLAH, dan girman ALLAH kizo ki mallaki halak ɗinki, idan baki da kuɗin saye ko baki da ra'ayin saye basai kin damu da karantawa ba dan baya cikin wajib. Mai tunanin siya ko mana mugunta ki fitar kiji tsoran ALLAH karki cutar damu bamu cutar dake ba, idan kinyi shirin haka da gayya ko izgilanci a garemu muna roƙon UBANGIJIN al'arshi mai rahama mai jin ƙai, mai sanya alkairi a zukatan dake ƙudurta sharri ya shiryeki ya ganar dake gaskiya ya kuma bamu kariya daga abinda zuciyarki ke ƙulla miki????????????._

KU DAI KU GARZAYO A DAMA DAKU A CIKIN WANNAN ZAZZAFAR TAFIYAR CIKIN SALON NA ZAFAFA BIYAR MASU ZAFIN GASKE.

DUKKA LITTAFAN AKAN NAIRA DUBU DAYA (1k) KACHAL

IDAN KUMA DAYA KIKE SO (300)
BIYU (400)
UKU (500)
HUDU (700)

KARKU BARI A BAKU LABARI, DAN WANNAN SALON NA DABAN NE KUMA TAFIYAR MA TA DABAN CE!

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

HAFSAT UMAR KABIR
ZENITH BANK
2270637070

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

07040727902

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09134848107

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

SAI MUN JIKU MUTANEN AMANA!????????????????????????

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button