BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO 65

Cikar burina shine ganin irin wannan ranar

tare da ke gimbiyar mata, kece sirrin ruhuna, nima

inajin raɗaɗi fiye da wanda na gani a cikin ƙwayar

idanunki. I’m sorry! ranarki tana zuwa_*.

Ta haɗiye yawu da ƙyar, da sake maimata

karatun kamar mai bita, dan yayisa ne da yaren

maley ta tabbatar batayi kuskuren karantawa ba.

Zaune takai dan ƙafarta ta kasa ɗaukarta. Ta

cigaba da zaro sauran abinda ke cikin akwatin.

Akwai kashi-kashi na ribbons ɗinta, ta gane

hakanne saboda matuƙar son da takema wasu,

wasu kuwa ta gansu a hotunanta dake cikin albom

ɗin can tun tana yarinya. Sai wani ɗan abunta mai

kamar kwalba cikinsa da taurari da wata suna

yawo, a tsakiyarsu da alkur’ani a buɗe, idan bata

manta ba Mamie ce ta bata shi as gi! ɗin kammala

haddar alkur’anin ta, amma saita nemesa ta rasa a

daga baya duk da kuwa a side drawer na gadonta

yake. Har kuka tayi na rashinsa, kai tsaye kuma ta

zargi mai aikinsu ce ta fasa amma ta ɓoye. Mamie

ce ta kashe wutar a lokacin ta sake saya mata wani

sai dai yasha banban da wannan ɗin dan haka

taita mitar batason sa har sai da Abie ya shiga

zancen ya lallasheta. Ashe Yaya MM ne ya sacesa.

Ta cigaba da kallon abubuwa da dama nata, kuma

masu muhimmanci a gareta data nemesu ta rasa a

lokuta mabanbanta, wanda a iya tunaninta ta rasa

mai ɗaukar mata su, duk da har su Amrah yaran
aunty mimi tasha zarga. Book ɗin ta ɗauka saboda

ji a ranta shima ya shafeta. A shafin farko sunanta

ne da rubutu kamar haka.

*_Juwairiyya Anaam! kece matar aurena kuma

uwar ƴaƴana da izinin UBANGIJINA. Ni kaɗai aka

haifawa ke, zan kuma rayune domin ke insha

ALLAHU._*

Ta buɗe shafi na biyu zuciyarta na tsitstsinkewa.

_Da ace wani bawa nada damar tsara labarin

rayuwarsa da wanzuwarsa, zan tsara nawane

kawai domin ke kaɗai a wannan duniyar. Ina

roƙon UBANGIJI ke ɗin karki zama a cikin

ƙaddarar abinda ALLAH bazai mallakamin ba,

zuciyata bazata iya ɗauka ba, ya rabbi ka zama

gatana akowane hali_.

Haka ta cigaba da karanta abubuwa daban￾daban akan rayuwarta da tasa daya dinga

rubutawa tamkar labarin littafi. Mafi ƙololuwar

ruɗa tunaninta da saukar da hawayenta shine a

gaɓar da Mommy ta takura masa auren watanta.

Duk wani tashin hankalinsa ya zanashi da fargabar

karta suɓuce masa. Zuwanta Nigeria da sunan

hidimar ƙasa mafi girman sassauci dajin ƙwarin

gwiwar yin biyayya da cusa son Fadwa a ransa

matsayin sadaukarwa ko UBANGIJI zai masa

tukuyci da samun Anaam. Kukanta ya ƙara ƙarfi

jin cewar ya kwanta jiyyane akan jin za’a aurama

waninsa ita ba shi ba, harda barazanar kamuwa da
ciwon hawan jini daya nema shafar lafiyarsa.

“Innalillahi…” ta shiga ambata da kifewa jikin desk

ɗin nasa ta shiga raira kuka, wani al’amari mai

girma na ratsa dukkan magudana da jijiya ta

jikinta. Sai da tai kuka sosai harta gode ALLAH

kafin ta ƙarasa ganin wasu zane-zane da yayi

wanda duk fuskartace ya zana, kai kace tana

tsayene a gabansa yay zanen. Da kyar ta miƙe ta

tattare komai ta maida masa yanda yake ta maida

a drawer ɗin sannan ta fice jikinta a saɓule.

Aysha dake zaune a falo tana aikin nata na

tiktok data koya gun Fadwa ta bita da kallo. Ganin

zata wuce bedroom batare data tanka mata ba ta

riƙo hanunta da sauri. Juyowa tai tana kallonta,

hawaye masu ɗumi na sauka mata a kumatu, sai

kuma ta rungume Ayshan tana saki wani marayan

kuka da ita kanta bata gama tantance na minene

ba.

Hankalin Aysha ya ƙara tashi, ta ɗagota da sauri.

“Ya ALLAH blood wai miya farune? Yaya ne ya miki

wani abu?”.

Kanta ta girgiza mata.

“To minene? Ko dai maganar aurence dai har

yanzu? Da zaman wannan gidan?. Dan ALLAH ki

kwantar da hankalinki Anaam. Ki saurareni a

wannan gaɓar na buɗe miki kanki ta yanda wlhy

sai Yaya Share” ya dawo tafin hanunki ta hanyarsoyayya da bin dokokin ALLAH. Na fahimci rashin

sanin minene kishi da rayuwar gidan malam

bahaushe ke sakaki tafiya a haguggunce a wannan

gidan har Fadwa ke jan akalarki da makirci. Ki

nutsu ki saurareni Please”.

Bataƙi ta Ayshan ba, suka koma suka zauna cikin

hikima da basirar da ALLAH ya bama Aysha. Da

kasancewar ta tashi a rayuwane ta cikin gidan

yawa dama salon kishin Mommy da Aunty Amarya.

Ga karance-karancen littatafan nan na hausa duk

tana taɓawa ta shiga warware mata abubuwa

masu yawan gaske. Anaam irin mutanen nanne

masu saurin haddace abu idan an faɗa musu,

musamman akan abinda ke wahalar da su, ko

wani abu da basa ƙaunar a kaisu ƙasa. Hakan ya

bata matuƙar gudunmawa wajen fahimtar Aysha

daki-daki babu kuskure. Sosai taji daɗin bayanin

dan haka ta rungume Ayshan.

“Na gode blood, nagode, irin godiyar da babu

alƙalamin dazai iya rubutawa. Sai dai ki sani duk

abinda kikaga inayi a gidan nan kamar mara wayo

ba rashin wayo bane sarai ina lure da komai da

binsa daki-daki, sannan akan sani nake aikatawa

saboda wasu dalilai nawa. Idan banyi hakaba shi

kansa bazan gama fahimtar halayyarsaba balle ita.

Tabbas nasan bazan taɓa iya kaiku wayon zama a

irin rayuwar da kuka tashi ba, sai dai koba komai

ina shigowa cikinku nima ina ganin wasuabubuwan. Daliline ya sakani zaɓar yin duk abinda

nakeyi. Sai dai a yanzu kalar rubutun zai sha

banban da kalar takardar. A yanzu lokacina ne,

kisa a ranki lokacin Juwairiyya Usman MD Share”

zai fara a gidan Al-Mustapha Muhammad MD

Share”. Nayi alƙawarin bazanyi abinda zai cutar

da kowa ba, sai dai zan nunama kowa kowacce

mace da ilimin zaman gidan aure UBANGIJI ya

halicceta, kuma ko wacece ita ko’a ina ta tashi zata

rayuwu, ta kuma riƙe kambunta na ɗiya mace. A

kwanakin da nayi biyar a gidan nan, na karanci

abubuwa masu dama a cikinsu, zan kuma fara

sharar fadata da su domin samun damar shimfiɗa

mulkina batare da wani datti ya sha gaban cikar

burina ba”.

“Woow vary interesting my blood. Haka nake

sonki dan ALLAH. Ki haukata mana Yaya Share”, ki

kuma dawo mana da Fadwa hanya tabar bin

karatun su Mommy, ta zama mai ra’ayin kanta”.

Anaam ta ƙyalƙyale da dariya, zuciyarta fes

tamkar an sauke mata dukkan wani nauyi da

ƙuncin da takeji a yau a yanzu yanzu. Basai

amfaɗa ba, da ni da mai karatu duk zamu fahimci

hakan nada nasaba da abinda taci karo da shi

wannda a baya bashi take kallo a fuskar Share”

ba. Sun ƙara tattaunawa sosai akan wasu

abubuwan da dama da Aysha kafin ta miƙe ta

koma sashen Share” domin gyarawa bisashawarar Aysha.

Bata jin daɗin jikinta saboda ɗinkin da akai mata

na sakata jinta tamkar a takure, ga tafiyarta har

yanzu bai zama normal ba kamar da. Amma haka

ta jure a daddafe na rashin sabon da wahala ta

gyara ko’ina na sashen nasa, sauƙin ma babu datti

mai yawa. Sai da ta tabbatar ko’ina ya mata da

kamshi sannan ta rufe ta fito. Baki ta saki tana

kallon yanda Aysha ta ƙara gyara sashenta itama.

Ta saki murmushi da harar Ayshan dake tsaye tana

karanta mata taje tayi wanka ta ɗauki ado dan

Yaya Share” na gab da dawowa. Akwai tsoro

tattare da ita na abunda ya faru, amma gargaɗin

likita akan Share” ya bata ƙwarin gwiwar

tabbatarma kanta babu wani abu tunda ko dai

baya cikin hayyacinsa ai baya nema wani abu daga

garetaba zaren ɗinki na a jikinta. Da wannan

tunanin ta faɗa wanka. Koda ta fito tsareta Aysha

tai wai sai ta mata kwalliya. Badan taso ba dole ta

tsaya kuwa Aysha ta zaneta tsaf dasu jaja leɓe da

barbaɗa kumatu na zamani. Turare kuwa har ji

take yana hawa mata kai dan khumras nata sun

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button