BAK'A CE 1-END

BAK’A CE Page 41 to 50

Ido Wardugu ya rintse tare da shiga wani tashin hankalin, yana shiga dakinta? (Kalma mai fasara biyu), 

Katseta ya yi ta hanyar fadin” bai baki takarda fara ba?

Kai take girgiza cikin yannayin firgici kafin ta tsaya tsak, 

Mikewa ta yi da gudu ta fada dakinta ta bude akwatinta ta ciro takardar da ta adanawa Mu.azam wace a iya sanninta da shi ita kadai ce takardar da ta taba wani hada su,

Jiki na bari, tana jin kamar ta kifa ta karaso ta mikawa Wardugu takardar inda ya bude ya karanta, 

Tsaf takardar saki ce Mu.azan ya dankarawa yarinyar da suka dauka suka wanke suka bashi, a cikin kasar da bata san kowa ba sai shi, a lokacin da ta shaku da shi, sai wata yar takardar a hade da dayar inda ya rubuta” Agaishat, ki yafe min, ina son ki ba dan bana sonki ba, sai dai hakan da na yi shi ban yi kai tsaye ba. *Ina son ki*,

Dubansa ya kawo kan Agaishat dake tsaye tana jiran karin bayani daga nesa kadan da shi , sai khadija dake kukan gannin rashin dacewar abinda Mu.azam yayi duda kuwa da hakan na iya mata dadi da a lokacin da bata san su waye Wardugu a rayuwar Mu.azam ba, aman a yanzu da ta ga waye Wardugu, ta kuma ga irin halacinsa sai ta ji ta shiga wani yannayi na rashin jin dadin abinda abin kaunarta ya aikata, duba da irin yanda ran Wardugun ya baci sai hankalinta ya kara tashi, 

Murya dake ya ce” fice mu tafi,

Ido ta zaro tana dubansa kafin ta shiga yarfe hannu, murya na rawa ta ce” ina son sa, ina son mijina, ka hashi hakuri ya maidani dakina, ba zan kuma yin abinda na yi ya sakenin ba, ba zan yi ba, Wardugu daga aure sai a sake ni? Me Anna zata ce? Me baba sofo zai ce? Ya zasu yarda da wannan abin? Wardugu ina son sa,

Wardugu ya dan saki hanya ya nuna mata hanya fuskarnan a hade tamkar ya shaketa haka yake ji, dan rashin sannin ciwon kai wai a bashi hakuri, 

Da sauri ta ratsashi ta fice tana waiwayen Khadija dake son ta baiwa Wardugu hakuri aman tana tsoro,

Itama murya na rawa ta ce” Wardugu toh bari na dauko mata hijabinta fan Allah, kafin na je na same shi asibitin,

Ja ya yi ya tsaya, juyowa ya yi yana dubanta kafin ya ce” *Tana da gata fa, itama yar dangi ce, ko bata da kowa a duniya tana da ni, idan kin je asibiti wajen masoyinki! Ki fada masa na gode! Na juya nigeria zan dawo gannin jikinsa in sha Allah, zancen hijab ki bar shi, wannan suturar ta jikintama zan dawo da ita, na haramta mata du wani abinda zai fito daga hannunsa komai kankantarsa! Mu.azam da Ni Wardugu yake magana!*

Haka ya tafi ya bar Khadija tsaye cikin tashin hankali ya shiga motar ya jata a tsoyace yana tukin irin na dazu inda Agaishat ta hade kanta da gwuiwarta ta afka duniyar tashin hankalin da ya fi na kulun, wai ita Agaishat har namiji ya nuna mata hali tun ba.a je ko.ina ba? Ita Agaishat, itace aka dankarawa sakin da ba laifi? Ita agaishat itace zaune a gidan kato da sakinsa a kanta tana wadaga tamkar gidan ubanta? A yau ta karasa yin tir da rashin ilimi, a yau ta ji duniyar ta fice mata a rai, a yanzu da aka ce ya saketa ta ji wani kaunarsa ita kuwa, ta shiga tsaka mai wuya ga Wardugu yaki koda kallonta bale ya nuna mata wani yannayi na tausayawa, ya tafi a bacin ran irin wulakancin da Mu.azam ya yi masa da tunanin yanda zasu kwashe da Ayya, 

………bai koma hotel ba sai da ya je ya samu takardar komawa Niger ta mutun biyu kafin ya juya Hotel da ita!

                   Timiya

Tafiar su Anna tafia ce mai nawa, domin dai ana fitowa daga cikin Timiya saman rakumi ne, gashi Anna sai da ta dauko baba tsofo du kuwa da irin yanda ya kiya aman fir itama ta kiya sai da shi ya saka aka yi dabara aka dora shi amale tun yana tsugune , maza hudu suka tatare har amalen ya mike kafin suma sauran su hau nasu su kama hanya,

Tafia ce mai tsayi idan ba.a gagawa, tafiar sahara ga tarin yan rakia da guzurinsu, dan jariri kuwa a nade a cikin tufafi mai laushi a jikin Anna rata yi masa goyon gaba,

Ana tafiar ne ana tsayawa a baiwa baba Tsofo abinci da ruwa hakan ya sa suka wuni cir kafin su shigo gari 

Dogarai ne suka juya dabrakuman inda su kuwa suka dauki motar sarki daya kwal mai baya bude suka nufi garin Agadez

Ba su su shiga garin ba sai da isha ta yi, suna zuwa direct gidan sarkin suka je 

Bayan an sauko daga salar isha.in ya kara ganawa da sarki, wanda ya bukaci gannin Anna,

Anna na shiga Sarki ya mike yana dubanta, kamar gatanan a fili ta mahaifiyarta, mace mai mutunci da mutunta mutane,

Ba bata lokaci ya hada vidio call da aminin nasa,

Dagawa ya yi yana mai saka gilashinsa na karin gani yana fadin” Sarkin agadez da kansa

Sarki ya amsa yana murmushi mai kayatarwa kafin ya hasko masa Anna dake tsaye 

A zabure ya mike tsaye yana mai……

???????????????? *BAK’A CE* ????????????????

https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp

*☀IDAN RANA TA FITO WRITER’S ASSO????* ____________________________________________

             

*Fad’akar da al’umma tare da nishad’antar da masoya shine fatanmu*????????????????

                            Na

                     *SAJIDA*

                          5️⃣8️⃣

Tuki yake na garari, ba bin doka , ba tsare iyakar gudu da mota a cikin garin paris, wanda hakan ya saka motar police bin bayansa tana mai nunin ya tsaya aman fir ya ki ya tsaya,

Bai zame ko.ina ba sau gidan Mu.azam,

Yana fitowa daga motar police din ta fito da sauri tana mai nuno shi da bindiga da fadin ya tsaya ko ta harbe shi, 

Hakan ya janyo hankalin daidaikun mutanen dake anguwar, wasu na dan lekowa ta takarsu, wasu na fitowa dan ganninnko barawo ne aka biyo har anguwarsu? Ciki kuwa Harda Khadija da ta ji haya hayar ta yi yawa,

Rai bace ya ja ya tsaya ya juyo yana mai saka hannunsa cikin aljihunsa na wandon dake jikinsa hakan ya saka ta kwala karan ya tsaya kar ya kara wani motsi a yanda yake!

Tsayawa wardugu ya yi, dan ya san in ya kara motsin a hakan hukuncin harbi ya hau kansa,

Da gudu ta karasa tana fadin ya daga hannayensa sama,

Kansa ya girgiza da yaren french ya bude baki rai bace ya ce” sunana General Wardugu Marahutt, ki barni na ciro maki shaidar hakan, kar ki saka min hannu a aljihu! 

Ya karasa yana mai kuwa a kanta,

Da sauri ta ja ta tsaya daga niyar caje aljihun nasa ta dan ja baya still dai bata sauke bindigar ba, ta shishiryawa ko ta ware ko ta walare,

Ciro mata baje dinsa ya yi ya mika mata a dake, 

Da sauri ta karba ta karanta, ta ga hoton sama da komai,

Da sauri ta sara masa, domin karatun da wardugu yayi na bashi power a kasashen wajema ba a iya niger kadai ba, dan haka ta bashi hakuri tana mai fada masa ta biyo shi ne daman dan ya taka dokar fice ka.idar gudu a cikin gari 

Karba ya yi ya juyo inda itama ta shiga magana da wayar hannunta tana fadin shikennan kar a turo mata kowa General Wardugu Marahut ne na Niger .

Ko kallon Khadija dake masa magana bai yi ba ya shiga gidan ya karasa ya shiga danna karaurawar dakin ba tare da ya bari ta numfasa ba ya ci gaba da dannawa,

Dirowa ta yi daga bed, kayan baci masu santsi sakaku ne a jikinta dogon wando da riga har gwuiwa, kanta ta kunce shi ya bazu a gadon bayanta sai turaran ruwa da ta shafa a jikinta ta kwonta ta huta bacin da bata yi ba wannan karan haka ya firgitata,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button