WUTSIYAR RAKUMI 59 & 60

*_????WUTSIYAR RAƘUMI!!……????_*
_(Tai nesa da ƙasa)_
*_Bilyn Abdull ce????????_*
_Duk yanda rayuwa takai ga tsawo wataran sai ɗan adam ya fahimci taƙaitacciyace daga garesa,
bazaki/bazaka tabbatar da hakanba saika buɗi ido kaga tawagar mala’iku a kanka sunzo amsar ruhinka, kafin wani lokaci ka jika a wannan gidan na wucin gadi (kabari) kafin randa kowanne bawa zai tabbatar da gidansa na gaskiya, wutace ko aljanna????? ALLAH ne kawai masanin wannan sirrin????????????_
*_NO. 59 & 60_*
…………..Rayuwa taci gaba da tafiya, soyayya tsakanin Ummukulsoom da Amaan ba’a cewa komai, ga ƴar babynsu Noor-ur-Rahman ƴar gatan Affahn ta, yayinda a ɓangaren aiki su dukansu suketa sake samun ɗaukaka da ƙarin girmansu saboda ƙyawawan zukatansu, tuni Ummukulsoom ta kafa ƙungiya a ƙauyen ɗilau, wadda taketama mata hidima wajen basu jari da buɗe musu wani ɗan lokaci na fahimtar dasu ilimin addini dana zamani, tun maza na noƙewa har suka fara sakin jiki da makarantar saboda canji da suke gani ga matansu.
Ga iyaye sun dage wajen barin yaransu mata su cigaba da karatu mai zurfi, dan Ummukulsoom tazama madubin dake haska ɗilau da kewayenta, ita ba ahalinta kawaine ke amfana da alkairinta ba, ta kowace kamar yanda kowa yake nata a birni da karkara.
*_BAYAN WASU SHEKARU_*
Ƙyaƙykyawar budurwa ce tsaye ƴar kululluɓa haka takema wani ɗan matashin saurayi da bazai gaza shekaru ashin da biyu ba magana, amma ya miskile fuska yaƙi ya kulata sai faman danna waya yakeyi, cikin fushi ta tallare masa ƙeya tana juyawa cikin falon gidan ranta a ɓace harda hawaye.
Dattijon da bazai gaza shekaru 60 ba yana zaune cikin kujera yana duba littafin Fiqhu ya ɗago manyan idanusa farare tas yana kallonta, “Noorin Affah miya faru kuma?”.
Zama tai kusa dashi tana sake matso hawaye, “Affah kaga Noorul-Ayn ko, na masa magana yazo na aikesa ya amso min abu wajen yaya Ahmad amma ya shareni yanata game a waya bai kulani ba”.
Yanda take hawaye sai tausayinta ya kama Amaan, yarinyar tanada haƙuri, musamman akan shegen miskilancin ɗan uwanta Mahmud da suke kira (Noorul Ayn) danshi nasa kalar miskilancin ma da banne shida Amatul-kareem.
“To ya isa haka share hawayenki, banace kidaina masa kuka ba shi ƙaninki ne? Jeki kiramin shi”.
Tashi Nuoor-ur-rahman tayi ta fita tana goge kwallarta, a inda tabar Noorul-Ayn anan ta iskeshi zaune ko motsi baiyiba, ta dalla masa harara tana faɗin, “Kazo Affah na kira, miskilin banza kawai”.
Nanma bai tanka mataba, miƙewa kawai yay ya nufo falon.
Noorul-Ayn ya zauna a ƙasa saitin ƙafar Amaan da tunda ya shigo yake kallonsa, su kansu da suka haifi Noorul-Ayn bazasu iya tuna yaushe sukaga hakoransa a waje ba yana dariya, haka yake kullu yaumin fuska a cinkushe, kuma babu abinda akai masa, magana kuwa sai yaji bala’in Ammi (Ummukulsoom) yake yinta a gidan, dan ita batai masa da sauki, ca take bazata iya da wannan banzar halayyarba, taci wahalar ubansa taci tashi.
“Noorul-Ayn mina gaya maka ranar akan Noor-ur-Rahman?”.
Shiru yay bai tanka ba, kuma ga maganar a maƙoshinsa amma bakinsa ya kasa furtawa, Ummukulsoom data shigo falon a gajiye batare dasun lura da itaba ta dakama Noorul-Ayn tsawa, “Wai kai dan uwarka ba magana ake dakaiba ne?”.
Duk kallonta sukai, yayinda Noorul-Ayn ya janye idonsa a kanta yana fisgo magana da ƙyar yace, “Affah kayi haƙuri, itace ta isheni da hayaniya aka, ai tasan dai zanje ɗin”.
Zama Ummukulsoom tai kusa da Amaan tana harar Noorul-Ayn dake magana a hankali kamar mai ciwon baki, yayin da Noor-ur-rahman taje ta kawo mata ruwa mai sanyi.
Amaan ya jinjina kai kawai, lamarin Noorul-Ayn sai dai addu’a kawai, “Amma data maka maganar idan bakaso ta dameka basai ka tashi ka tafi ba, banason raina na gaba, ka shiga hankalinka a gidannan, inba hakaba wlhy gidan Uncle Bassam zaka wuce gobennan, danshi ba ɗaukar wannan iskancin naka zaiyiba, mutum saikace wani kurma ko gunki……”
“Ya isa haka ayi hakuri Ammi” Amaan ya faɗa a hankali yana riƙe hannunta, dan yitake kamar zata make Noorul-Ayn. Itama Noor-ur-rahman duk sai tausayin ƙanin nata ya kamata, ta kama hannunsa suka fita kuma tana lallaɓasa, dama haka suke, kullum babu fashi saisunyi faɗa, dan ita hakurine da ita, batason kuma shariyar da Noorul-Ayn ke mata sam, ko hirarnan da zakaga anayi da kane ita bata samu suyi, sai dai ita da Amatul-islam, itakuma yarinyace, sune ƴan biyun da Ummukulsoom ta haifa bayan haihuwar Noorul-Ayn ɗin da kusan shekara goma sha ɗaya, harma sun fidda rai da haihuwa saikuma ga cikin su, ta haifosu tagwaye sukaci sunan Ummi da na Maman Ummukulsoom wato Hassana, amma sai ake musu alkunya da *Amatul-islam & Amatul-kareem*, to itama Amatul-kareem ɗin haka take miskila ta bugawa a jarida, duk sun kwaso Amaan ɗin.
Su Noor-ur-Rahman na fita Amaan ya kalli Ummukulsoom yana murmushi, “Beauty kinga kin gama faɗan sunkuma haɗe kansu, kodai wanine ya kunnomin ke wajen aiki zaki huce haushin kan yarona?”.
Murmushi tayi tana kwantowa gefen hannunsa, “Aini wannan hali naku sai ku wlhy Zunnur, gashi nan Noorul-Ayn yazo ya takaku ya shanye, ALLAH miskilancin yaronnan yana bani takaici shida Amatul-kareem, da ana cirewa dana biya ko nawane an rabasu dashi nikam”.
Lumshe idanunsa yay ya buɗe yana murmushi, tare da sumbatarta a goshi, “Sai dai aita haƙuri damu Noorulain ɗina, muma ba’a san rammu baneba”.
“Uyimmm, amma kuka iya share mutane, haƙuri nake kawai nima wlhy Sweet fodio” tai maganar tana jan hancinsa.
Gaba ɗayanta ya sanya a jiki yana murmushi, ihun Amatul-Islam ya saka Amaan saurin sakin Ummukulsoom, autoci sun dawo daga School.
Jikinsa ta faɗa tana murnar ganin iyayen nata, yayinda itama Amatul-kareem dake biye da ita fuska babu fara’a ta faɗa jikinsa ya haɗasu ya rungume.
Barin jikinsa sukai suka koma wajen Ummukulsoom itama tai musu oyoyo, saiga Noorul-Ayn da Noir-ur-Rahman sun dawo suma, Noir-ur-Rahman ta jasu ɗakinsu danta cire musu Uniform, shikuma Noorul-Ayn ya wuce kicin zuboma Ummukulsoom abinci data sakashi.
Haka rayuwar gidan take, babu ruwan Ummukulsoom da ƴar aiki tunda yaranta sukai wayo, dukda kasancewar Noorul-Ayn namiji haka take sakashi duk aikin da zata iya saka Noir-ur-Rahman, dan haka yaran suka tashi a hore, babu sangarta ko san jiki, kosu Amatul-Islam dake da shekara 10½ a duniya Ummukulsoom sakasu aiki take.
Ta kuma zama babbar mace, tayi ƙiba sosai, yanda ta ƙara girman jiki haka ta kara girman daraja a idon duniya, tazama abar alfahari a kauyenta da ahalinta dama mata, dan tuni ƙungiyar data kafa tagama tsiro da yaɗo, wanda manyan mata ke cikinta suna hidimtawa matan karkara da yara, musamman yaran da ake bautarwa ta hanyoyi daban-daban, tariga ta zama tauraruwa ta mata da yankinta na arewa, sunanta yakai tsqiko a ƙungiyar lauyoyi da har takai ana shakkar karawa da ita akan shari’a, hatta da alƙalan shakkarta suke, dan ita duk yanda gaskiya take saita kwalƙwalota.
Rayuwar gidansu abin sha’awa itada mijinta Usman Mahmud Usman Ajiwa, da ayanzu haka ya zama babban mutum shima, mai riƙe da muƙamin Lieutenant general na soji, duk inda matarsa ta sanya kafa hannunsa na ciki da addu’arsa, yana taimakonta da karfin aljihu dana shawarwari da dabaru, yayinda suke zuba soyayyarsu da bata tsufa sam, sai daifa halin na nan daram bai canjaba ga Amaan, ga karin Amatul-Kareem da Noorul-Ayn da suka sake samu, a yanzu haka auren Ahmad da Noir-ur-Rahman watanni kaɗan ya rage.
Abotarsu da Attahir kam ai saima abinda yay gaba, dan suna nan gam-gam.
Hakama tsakanin Ummukulsoom da Bily da Aziza, harma dasu Suhailat da suka dunƙule yanzu, ko ƙungiyarnanma atare suke jagorancinta.
Ɓangaren Basiru kam zuwa yanzu Alhmdllh, dukda yazama gurgu dai ALLAH ya sama jarin kayan miyar da Ummukulsoom ta bashi albarka, harma ya auri wata yarinya dagacan wani ƙauye, itama dai tanada lalurar shanyewar ƙafa, dan karya zauna haka babansa ya nema masa aurenta, annan cikin gidan aka gina musu ɗaki ɗaya suke zaune, yanzu haka yaransu biyu, Amal ma yarinyarsa ta wajen Lubna tana zuwa lokaci-lokaci kamar yanda Ummukulsoom ta roƙa.