DANGIN RABI HAUSA NOVEL

Iya ce ta sa Ali Shagali a gaba Yana Zaune kamar TV a gabanta ta zura Masa ido tana far far da idonta Wai a dole fari take Masa na soyayya sabo da jiya ya Bata kudi dubu Uku,Kamar sabon kamun hauka,Ali Shagali yace a gaskiya Ni na gaji Iyan Rumaila Haba tun kina kallo na da marmari har sai kin koma kallon Muni na,tun safe da hantsi kin hanani fita Kuma kince ba kwanciya ba tsaiwa sai dai na zauna a gabanki kiyi ta kallo na,tun kina ganin kyawuna ai sai kiga Muni na,Nima Kuma tun Ina kallon kyanki gashi kin jawo na gano Sam Baki da kyan Hanci Haka Hanci kamar gajeren wando shi yasa aka ce Rumaila babanta Tayo shi yasa ita kyakyawa, Haba Iya ga gashin girarki daya tafi daya tsayi Taya akayi Haka? Iya fuska ta Bata tare da cewa to Kai kyan ne da kai? Dan ka samu ma nace Zan maka kauna yau dama Kai ba Dan goyo bane Kuma wallahi zaka dawo da daddare ne tashi kasan inda dare yayi maka,me shayi yace Alhmdllh na gode Ni Kam na gaji da kaunar Nan gaba daya, Abun hauka ne? yo idan Haka ake kauna har abada ma na Yi ta,ai ko auren bazan Yi ba,kin zaunar Dani Kamar talbijin sai wani fikil fikil kike min da Ido ke ga Abu Kamar an Dan yanka da Reza,da Allah ki samo sabon salo wannan Bai Yi ba,idan an girma Dan Allah Iya asan an girma wannan ai shashanci ne tsohuwa dake me ya rage Miki yanzu,me kike Nema a duniya,da budurwa ce tayi min sai nafi ganin birgewa Amma....Iya Tace to Dan tijara Kai kamar kwallon Mangoro,dan Kauye ai dama Kai Dan gargajiya ne,baka San komai ba sai jahilci,Ni Dana Yi aure har a birni na San takan wayewa,Me shayi yace naji ya fice Yana cewa na tafi gona,Iya tace aikin kenan Dan gona Kawai abinda ka sani kenan ya za a shuka dawa da masara in Allah ya yarda sai sun daina tsada sun karye a kasuwa muga ta tsiya ku Fadi rasha rasha,ai kuwa ba kya Sha Miya da kifi ba,Kuma ba kudin da Zan Baki babu Kuma saki ko Uwata Zaki zaga wallahi Iya kina Nan Dole kici gaba da dafawa yarana tatsotse.
AsmaBaffa
????????????????
DANGIN RABI
????????????????
KARSHEN
FREE PAGE
DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.
NA KUDI NE
GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE
ACCOUNT NUMBER
0175487861,ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK
MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER DA ZAKU TURA
08033933642
‘YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER
+227 90 79 59 39
36-40
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne masu Sharhi na ko wanne Group Ina matukar Godiya,Wanda ban bawa pages ba kuyi min afwa idan kun samu damar siya sai mu hade a paid Group????????
Me shayi ba a Dade ba ya girbe masararsa a gona yaci riba sosai ba karamin kudi ya samu ba,Ya bawa matansa dubu goma goma,zo kaga Murna wajen Iya,Iya ta Irga kudin Nan yafi sau goma tana irgawa tana cewa Alhmdllh ga Allah ya Gama bani arzi ga arzin 'ya'ya ga na kudi,ga yara ga boza wohoho Rumaila kin cuci kanki,Ana ta Yi ba ke,Ga Iya arzikinta yazo Allah ya Buda min,tunda Iya ta samu wannan kudin shike Nan sai Yanga da gadara kana magana zata ce me nake Nema a wajen wani,Waya ma daina dagawa tayi idan za a Kira ta sau dubu baza ta daga ba Wai Bata da lokaci ta Zama Busy,Lokacin Me Shayi Yana ganin Soyayya sai gasar kyautata Masa sukeyi Iya da kishiyarta.
Yau da cikin dare Zazzabi ne me zafi ya lullubeni da shi na kwana ko Sallar Asuba da kyar nayi ba tare da na iya karanta Azkhar ba,Ina kwance Ina Rawar Sanyi na dukunkune a cikin bargo,Umma taga har 11am Lokacin Fu'ad yazo sunyi Sallama ya wuce Office Amma ban fito ba,Bedroom Dina ta Shiga taji Ina Nishi tare da Rawar sanyi,Umma tazo gefen Bed Dina tare da taba gefen fuskata da Bayan Hannunta taji zafi rau,Tace zazzabi kike Yi Amma baza ki fada min ba? Paracetamol ta bani na Sha tana cewa nasan bazai wuce lalurar ciki ba,idan Kuma Baki warke ba sai Samha tazo ta duba ki,Nace Aunty Samha dama Likita ce? A e mana cewar Umma,Bayan Nasha na kwanta ban samu sauki ba sai wurin Sallar La'asar sannan Zazzabin ya sauka na fara gumi,Wanka da Brush na sakeyi tare da gabatar da Sallar Azhar da La'asar,Shiryawa nayi cikin wani 3qurt Tight legins me Kalar jikin Tyga,Ya dameni sosai Shape Dina ya fito dama gani da fadin mazaunai da tudu sosai nafi kiba a nan gaba daya,Riga me siririn Hannu Iyakacinta kugu na peach color,Gashina na gyara na fito Zan Ebo abinci na dawo dakina, Ina fitowa Fu'ad da wani abokinsa suka shigo su biyu suna tafawa, Fu'ad ne a gaba ban so Suka shigo ba,da sauri na shige kitchen Amma sun Riga da sun ganni,Abokin Fu'ad Mujaheed zaiyi magana a kaina Fu'ad yace shuru tare da daura yatsansa a saman jajajyen lips dinsa,Bana son zubar da aji nasan abinda zaka ce Bari na Kira Umma Ku gaisa ya furta tare da wucewa Dakina irin Umma zai Kira,Hijab Dina ya gani a saman bed
Dakko shi yayi harda linkewa sosai ya Shiga nemo bakar Leda a room din Nawa,ya birkito min kayan sawa ta a sip duk ya zubo da su kasa, Bangaren Inner wears yaje a shirye suke ya Watso su kasa farrr, Pant daya ya dauka ya kalla tare da tabe Baki ya jefar Yana yarfe hannu Wai kyankyami,Haka ya ya sa kafa ya dauke Bra da take kusa da kafarsa yayi chilli da ita ta daki bango ta fada can Haka yayi watsa watsa da kayan,sai a Drawer ya ga ledoji ya dakko ya saka Hijab din a ciki ya fito,Ni kuwa kunya tasa na kasa fitowa daga kitchen, Mujaheed abokinsa ya kalla yace tana zuwa Umman,Kitchen Direct ya leko ta kofa Ina jikin Fridge a tsaye Ina cin abinci na,Ledar da hijab ke ciki ya jefo min a fuska ta ya fice abinsa tare da haurawa sama ya Kira Umma ta fito Suka gaisa da Mujaheed sannan Mujaheed yace Umma na wuce,Dama ka Dade da zuwa Hala? Ae Umma a Garden Muka tsaya mun Dade,Ana ta shirye shiyen bikin? Yace ae Umma Yana Sosa Kai,mashaallah Allah ya kaimu ai gwara Mujaheed kayi aurenka da wuri,yace Umma so nake na bude musu hanya,Suna Dariya Umma Tace ka kyauta,Bayan ya tafi Hijab Dina na saka tare da fitowa,Na ga Fu'ad da Umma suna kallo suna Hira,Sannu kin tashi kenan Rumaila? Nace ae Umma naji sauki sosai ma,Haka ake so Allah ya Karo sauki nace Ameen,Bai kulani ba na wuce da Hijab Dina,Ina shiga naga Barnar da ya min Kamar nayi kuka,Sai Dana Gama cin abinci sannan na gyara kayan da dakin baki daya.
Tasalluwa tare da Baba Jummai suna kitchen suna Aiki suna Hira,Tasalluwa ta kalli Jummai Tace Oh Jummai Allah ya taimakeki da Yarinyar Rumaila ta kwace ki a hannun Yan fashi da tuni Dan Momy Fu'ad ya sadu da ke,Baba Jummai tayi Dariya Tace ke dai Bari tarko na ya Gama Kama bera,Rabo na da harkar Nan tun Mijina Yawale Yana da Rai,Baba Jummai ta share hawayenta taci gaba da cewa ai Ni lokacin murna nayi a Raina tsinanniyar Yarinyar tazo da siririyar murya Wai Oga na fanshe ta ayi Dani Yar Iska shi yasa na tsaneta,ke Tasalluwa na samu Kamar Fu'ad ya Tara Dani ai na Gama ganin Daren lailatul khadari ai wallahi da Allah yasa ya sadu Dani to Ana gamawa Zan roki Allah ya dauki Raina sabo da me nake Nema a duniya na Gama samu,Ni fa idan Nan gaba Ina da sauran shekara ashirin a duniya to da za bani Fu'ad ya sadu Dani Zan yarda Allah ya karbe sauran shekaruna du, Amma Yar iskar Yarinyar Nan me Kalar Lamsa tazo wani ayi da ita na fanshe ki ita a dole ta CeCe ni ji nake kamar na kashe ta Wallahi,shi Kuma Shuumin tana cewa ta fanshe Ni Baki ga murna ba wallahi,abin ya bani mamaki Bai San ma ya fara murmushi ba Ina kallon Dan mayyar,Dariya Tasalluwa ke Yi Tace gaskiya Ban taba ganin Tsohuwa irinki ba Baba Jummai wajen shekarunki 65 Amma kina son wannan harka Kuma da yaro me tashe Haba,Baba Jummai Tace sirri na na fada Miki Tasalluwa karki min tijara ni ko a da Harija ce daga Ni har Mijina Yawale Haka muke Kuma ke kin San ba a daina son abin Nan sai idan ba yanda za kayi,Tasalluwa da mamaki take kallon Baba Jummai,Tace kalle Ni da kyau Ni fa Dan bakusan wace Ni ba ne kawai kallo na kuke Yi,Tasalluwa Tace Kamar ya? Baba Jummai tace a son maza nake nufi Kuma matasa da ace kudi gareni to kullum a Hotel za'a na kawo min matasa Yan Shila Ina biyansu,Bakya tsoron Allah? Tasalluwa ta tambaya,Hmm Aljanna ta me Rabo ce idan Allah yaso ya bani sai ki Hana cewar Baba Jummai,Tasalluwa share zancen tayi Jin abin yafi karfin ta.
Samha Amaryar Abbi ita Umma ta Nemo ta dinga dubani tana da kirki ba laifi har cewa tayi ya kamata itama naje gidanta na Danyi kwana biyu nace zanje Inshaallah.
Bayan Kwana Uku na warke fes Dani Umma Tace na shirya muje Babban Asibiti a gwada cikin Nan Nawa a gani ko akwai ko da matsala ne, wani katafaren asibiti Muka je da Umma private Hospital ne,Babban Likita muka gani Dr David,Wasu gwaje gwaje ya min na sosai Bayan Umma ta fada Masa labarin cikin da komai, Bayan yayi duk Test dinsa ya tabbatar bani da wani ciki ko daya,mamaki ya hanani magana nace wallahi Umma Asibitin Dana ke zuwa Ana min gwaji Kuma Basu taba cewa bani da shi ba,Umma Tace na fada Mata Asibitin na Bata labari,Tace dama wannan Fu'ad ya kaiki Amma Baki taba fada min ba? Murmushi nayi na kareshi nace No Ni Nace Ina so,Karya kike Yi,Da gaske Umma Dan Allah karki Masa fada baida laifi,Kallo na Umma tayi yanda nake ta faman Bata Hakuri,Tace shike Nan ai kunfi kusa muje gida.
Nace Umma a shawara mu sake zuwa wasu Asibitin kamar biyu a sake Test a gani,Umma Tace kinyi magana a Nan muje,da kanta tayi Driving Runtumemiyar motarta Ruwan Toka Muka je wani me tsada shima an gwada babu komai,Haka Wani ma sun gwada babu,Umma Tace dama Asibitin Kauye me Suka iya babu Good Doctors ba kayan Aiki,Sai murna mukeyi,Umma tun kafin mu koma gida ta sanarwa Abbi da Fu’ad tare da su Nene,Ni Kuma Nan take na Kira Iya ta yafi sau goma Bata daga ba tunda taga New number gashi tayi kudi Bata da lokacin waya da kowa,Affa na kira,bugu daya ya daga na gaishe shi Ina ji Yana ta Maganar matansa nace Affa? Yace Ina jinki sai akayi Yaya? Ko bariki ce tayi dadi anyi kudi mu taho da kawaye na mu hada party? ai kuwa da kinga chashewa,Nace a’a Affa Allah ya tsare Ni da bariki,dama fada maka zanyi an min gwaji a birni bani da ciki,Nan take ya tintsire da dariya yace Ke Ni fa na tsuguna na haife ki,kin zubar da ciki Zaki Raina min hankali kafin nayi magana ya kashe wayarsa,Kiran duniya kin dagawa yayi dole na hakura.
Cikin Dare naci sa'a Iya ta daga Wayar tana Jin muryata Tace Zan daga Miki nono ba nace kar in sake Jin muryarki ba ko ganinki bana kauna,Hawaye ya zubo min nace Iya wallahi anyi gwaji a Nan birni asibiti me tsada ance bani da wani ciki,Iya Tace cab Amma kin iya rainin Wayo kiyi laulayin a gaba na ayi gwaji karki manta asibiti uku na kaiki har birni akace kina da ciki yanzu kin zubar da ciki zaki dawo ki Sharo min karya,Wallahi kika sake kirana ban yafe ba yawwa kije can kiyi barikinki inda kika saba,Wayarta ta kashe ta barni Ina kallon Wayar,Haka dukkan Yan gidan Yan matan da su Momy da Yan aiki cewa sukayi karya ne Umma ce tasa aka zubar min da cikin shi yasa ma na dinga cuta Amma yanzu anzo Ana musu karya sai Dariya sukeyi suna cewa daga ciki an koma kisan Kai.
Abbi kuwa yafi kowa murna sabo da Haka Yan Uwansa ya Tara Mata da maza tare da Yan gidan Muna Zaune yace yanzu zai saka ranar Auren Rumaila da Fu'ad,Murna nakeyi sosai a Raina a fili ban nuna ba,Abbi yace Fu'ad bazan muku auren dole ba kana son Rumaila? Sai yace a fara tambayarta tukun,Abbi yace Rumaila kin amince da Fu'ad Kai na daga alamar ae,To Kai Fu'ad fa? Nan take yace ban amince ba,Ni Abbi ban shirya Aure ba yanzu a kyale Ni Zan kawo da kaina,Umma,Abbi da duk me kaunar Rumaila sai da gwiwar kowa tayi sanyi Umma ranta ya baci tayi tunanin son Rumaila tuni ya Shiga zuciyar Danta Fu'ad Ashe ba Haka bane sam,Da Sauri Islam yace Ni Ina sonta wallahi Abbi,Abbi yace kinji Rumaila kina sonsa? Nan take nace Abbi Ni bance bana sonsa ba Amma ka Dan bani lokaci mu fahimci juna Yana zuwa zance wajena Muna Hira kamar kowanne saurayi da budurwa idan har komai ya min Zan bashi dama ya turo magatansa,Abbi yayi Dariya har Nene yace to Rumaila Allah ya zaba Mafi alkhairi...Momy ce Tace wallahi ban yarda ba,ba a Isa ba,sai da aka zubar Mata da ciki za ayi wa Dana Wayo,Danta ya Mata ciki yace Baya so an zubar ance ta auri Dana to ko sama da kasa zata hade bazan yarda ba,Ya zaka Yi da maganarka da kace shi zai aure ta tunda ya amsa da Kansa shi ya Mata ciki,ya zaka dawo da magana baya ko su yarana ba mutane bane?sabo da ga Dan mowa ko,Mama Tace karki yarda wlh,Samha kuwa Tace ai ba cewa akayi zata Aure shi ba an bashi dama ya nemeta ya dinga zuwa zance, Kuma kun San gaskiya wlh Fu'ad bazai iya yiwa wata ciki ba Haba Dan Allah,Yi Mana shuru munafuka,Abbi ne ya daka musu tsawa yace Islam shi yace Yana sonta Kuma Indai sun daidai ta aure ba fashi sai idan Islam ne da Kansa yace baya so ya fasa ko ita Rumaila Ni Kuma bazan wa kowa auren dole ba Alkawari nane shi yasa na bawa kowa zabi,ai shi Fu'ad ciki ya Mata sai ya aure ta shine gaskiya,Abbi yace bazan musu dole ba suzo Ana ta zargin juna Abu ya lalace na sake shawara ne tare da Yan Uwana da yardarsu nayi Haka,Umma Tace ai Fu'ad shi ya amsa da Kansa yayi Mata ciki sai a bashi ita dole shine gaskiya idan anyi Haka an zalunci Rumaila anyi son Kai, Fu'ad yace na Rantse da Allah Umma bani nayi Mata ciki ba ko Qur'ani Zan dafa ban San zance ba,Islam Dan a bashi Ni Rumaila sai yace Abbi Boye muku nayi gaskiya Ni nayi cikin,aka dauki Salati gaba daya,Ni Kuma nace na Rantse da Allah ba Islam bane Ya Fu'ad shine Abbi,Abbi Kansa ya kulle yace to magana ta Kare Kawai Islam zai na zuwa zance wajenki idan yayi Miki kice a turo magabata Rumaila,Nace to Abbi,Kin amince ko Fu'ad din kike so? Nace Abbi dama Ni ba son Fu'ad nakeyi ba Dan Umma nace Ina sonsa Amma ko kadan ban taba jin kaunarsa ba Kuma har abada bana Jin Zan iya sonsa ko da wasa gwara dai Islam din dama can tamu yazo daya,Aniyarki ta biki shegiya annamimiya cewar Momy, Fu'ad yace Abbi karka bawa Islam Yarinyar Nan Ina bada shawara yaro ne bazai iya rike aure ba,ga shi da son matan masifa kowa ya gani sonta yake Yi,kar yazo ya cutar musu da yarinya a barta tayi karatu Nan da wasu shekaru,Kanin Abbi Muhammadu yace Bama son Shishigi da Iyayi,kace baka so Ina ruwanka da duk Wanda ma za a bawa? Haka Abbi ya sallami kowa Dama nasan yanda ake son Fu'ad fiye da kowa baza a iya Masa dole ba,mutumin da sai abinda yace sai abinda yaga dama yakeyi,Umma ce Kawai ta daina kula shi tayi fushi da shi,ko yazo gaishe ta Bata amsawa,ni kuwa ko a fuska ban taba nuna Masa naji haushi ko wani Abu ba,sabo da Ni ba komai ke tsaya min a Rai ba,Kuma nasan maza Nawa ne suke amfani da Yaran mutane suna lalatasu Kuma baza su aure su ba,bare Ni da yace karya ne Kuma yanzu an gani ba ciki.
Ya Shiga damuwa Umma Bata kulashi,a Palo Ni kadai ya samu Ina karatun Haddar Alqur'ani,Bayan Na amsa sallamarsa Sannu da zuwa na Masa ya amsa da fara'a tare da Zama a kujera Ina kasa,yace Ina Umma? Tana sama na bashi amsa,yace kinga a kanki take fushi Dani ko? Nace ka Bata hakuri,na Bata Taki hakura kije Dan Allah ki rokar min ita,Nace Nawa za biya Ni? Sai ma na Baki kudi? Nace ae Mana Zan ma Aiki a banza Ka haife Ni ne ko sassaka Ni kayi? Kallo na yayi yanda na kalle shi na iya fada Masa Haka,yace Zan siya Miki waya sabuwa ta zamani,nace wacce Iri? Yace Tecno,nace lebra ce Ni ai nafi karfin Tecno,Infnix fa? Nace ruwan dare kenan,Okay Samsung? A Samsung din Yar Nawa? na tambaya,yace Yar dubu dari,nace Kara sama dai Malam baka ganni bane yanzu yanda na koma First class,yace Dubu dari da Hamsim tayi? Nace cike Hamsin din Mana,yace ki dinga Jin tausayi na yarinya nace Allah sai dai ta dari biyu cif yace to Yana turo Baki yace Kamar wata budurwa ta,nace me kace Zan fasa gaba daya?murmushi yayi yace Zan siyo kije ki fara aikin tana kulani Zan Baki Wayar,Ai kuwa naje na iske Umma a Bedroom,Nace Umma Sannu da Hutawa Tace Yawwa Rumaila,Nace Umma ga Ya Fu'ad can yazo,Bata Rai Umma tayi Tace wlh Baki da zuciya Rumaila mutum yace baya sonki Amma har kiyi maganarsa? Nace to Umma Wai ba ya wuce ba,Dan Allah kiyi Hakuri ki dinga Masa magana komai ya wuce Umma ko so kike Yi sabo da fushinki Allah ya jefa Masa wata masifar Kuma? Addua zakiyi Masa,matar mutun kabarinsa idan Mijina ne Zaki gani Umma bazan auri kowa ba sai shi,Hmm ke Kam Rumaila Allah ya Baki wata irin zuciya,Dariya nayi nace Dan Allah Umma kiyi hakuri,na Dade Ina rokon Umma sannan ta yarda,da gudu na fita Ina murna naci sabuwar waya,wata me Aiki na tura part dinsa nace kice Fu'ad yazo inji Ummansa,Ai kuwa tana fada Masa yasan nayi aikin da sauri ya zura jallabiyya ya taho,Yana shigowa Ina murna na nuna Masa sama da yatsa,Murmushi yayi tare da kashe min Ido daya ya wuce da sauri,Kamar barawo Haka ya shigo sakadaf sakadaf,A Gaban Umma ya tsuguna Tace tashi ma Malam nasan Baki kuka hada da Rumaila,zaiyi magana Tace wallahi karma ka fara karya na sani da Rumaila kuka hada Baki.
Dariya yayi tare da daura Kansa a saman cinyar Umma yace Umma na Dan Allah kiyi hakuri,ai ka Bata min sabo da Allah Yarinyar kirki zaka Bari ta subuce maka,Umma wallahi Ni cikin ne Kawai idan na tuna take bani haushi Kiyi Hakuri,naji tashi to ka tafi na hakura Amma ka sani Dan Rumaila na hakura,na gode Umma Bari nayi wanka na dawo mu Sha Hira,Umma Tace uhm naji jeka.
Da murna ya sauko ya fita,Zuwa dare sai gashi a palon Umma Hannunsa dauke da waya Sabuwa dal Samsung ta dubu Dari da Tamanin,A Gaban Umma ya bani,na washe Baki tare da sa Hannu Biyu na karba Ina zuba godiya,Umma Tace mene hadinka da Rumaila zaka siya Mata waya? Yace sabo da kin yafe min sabo da ita,Ai Islam ya dace ya Siya Mata ba Kai ba, ke Rumaila bashi wayarsa na siya Miki,Kallon Umma nayi na marairaice nace Dan Allah Umma na karba Dan Allah Umma,Umma Tace ki bashi wayarsa nace, Fu'ad yace Please Umma,Umma Tace Dalla rufe min Baki bashi wayarsa marar zuciya,Mikewa nayi kamar zanyi kuka nace Dan Allah Umma....ki bashi nace ta daka min tsawa,wayarsa na Mika Masa yace bazan karba ba Ni bana kyauta na karba Kuma,Umma Tace sai ka karbi abarka,nace Umma ki kyale shi bazai karba ba kinji ya fada da bakinsa ba a maida hannnun kyauta baya Umma a duba abin nan,Muna Haka sai ga Islam yaji abinda ke faruwa yace Dan Samsung Zan siya Miki ko ta Nawa ce, Fu'ad ya kalle shi da sauri ya Bata Rai yace Kai baka da kunya ko? To ka siya Mata ka gani idan ta Isa ta rike wayarka,wlh zaka Yi asara sai na farfasa ta gwara ma ka Kama kanka,Islam yace Dama wajenki nazo taso muje Garden,Baza ta zo ba Fu'ad ya furta da bala'i,nace sai naje gani Nan,Da Wayar na tafi na ajiye a dakina na saka Hijab na bishi zamu fita, Fu'ad yace Ke na juyo yace na daina kulaki daga yau kije ki gani din,Kafa na daga tare da buga skert Dina nace Sawa....Muje Islam me sunan dadi,duk gidan Nan babu me suna me dadin naka kafi kowa, Fu'ad yace Zaki dawo ne sai na ballaki Kuma daga can ki wuce wajen Momy ki koma wajenta.
Muna tafiya ya zauna yana fesar da iskar bakinsa Yana ta faman yamutsa lallausan gashin Kansa me yawa,Yana ta Tsaki,Umma tana Masa magana Amma Ina Bai San ma me take cewa ba hankalinsa ya Lula wani wajen,Wai uban me kake tunani? Mikewa yayi zumbur tsaye ya koma ya zauna sai Kuma ya tashi yace Umma sai da safe,Karfa ka sake naji ka kula Yaran Nan wlh,yace to Umma ya tafi,Garden ya wuce Direct ya hango Rumaila da Islam suna ta sheka dariya,takaici ya kama Fu'ad ya juya ya Kira Tasalluwa,Tasal yake fada Mata Wai shi bazai iya cewa Tasalluwa ba yayi Masa Kauyenci,da sauri ta zo yace Jeki Garden kice Rumaila taje Inji Umma zancen ya Isa Haka a hakura a tashi dare yayi,Islam yace Anya Umma ce ba Fu'ad ba? Tasalluwa Tace Umma ce gaskiya.
Yanda ya fada Haka Tasalluwa tazo ta fada Mana Tace Kuma Inji Umma,Dole na koma nayi tunanin gaske ne,tunda Fu’ad yaga Mun fara shiri da Islam sai ya Hana Kansa sakewa ya daina fita ya matse min lamba ko ya yaga Zan fita sai ya Koro Ni gida,Umma ta Masa fada yaki ji.
Can Barin Islam Kuma Momy Tace wallahi bazai aure Ni ba,Su Fadila sai zuga Islam sukeyi za a bashi me cikin shege farkar Fu'ad,tun Islam Bai yarda ba har ya fara Yadda yace zai sa Ido idan ya ganmu tare da Fu'ad zai fadawa Abbi ya fasa.
Yau Sunday Ina kwance sai ga Suhailat da gudu Yar gidan Anty Samha tazo da Kaya a Jakarta ta fado jiki na,dake mun Saba tana so na Tace Anty Wai kije Inji Mummy dinmu tana Kofar gida a cikin motarta sako zata Baki,Umma tana ji Tace Jeki kiji maybe yau Bata son shuguwa sauri takeyi,Dama nayi wanka naci kwalliyata cikin Riga da skert na lace ya min kyau matuka Dark green ne da pink,Dan siririn Mayafi na yafa na fita,na hango wata arniyar mota nasan dama tana hawa motoci,Ina zuwa na Balle murfin motar na Shiga nace Salamu'alaykum Anty Samha,Kofar naji an kulle garam ansa luck da sauri na kalli Driver sai Naga Ya Fu'ad ne,Sai da gabana ya fadi,Ya Fu'ad lafiya? Murmushinsa me tsada ya sakar min,wani yarrrr naji tsigar jikina ta tashi, nace lfy Ya? Shawara Zan Baki,Nace ta me Kuma? Karki auri Islam yaro ne bazai iya rike ki ba,Nace Ni Haka nake sonsa,Zan fasa Miki Baki ke Baki da kunya Zaki ce kina son wani a gaba na? Na Isa ne na Balaga na furta Ina murguda Masa Baki, Muna Haka Karaf sai ga Islam har ya wuce mu a tasa motar ta Gaban Glass ya hango tabbas mune,Islam ransa ya baci Yaja kwafa yace ko Dan na kuntawawa Fu'ad sai na auri Yarinyar Nan karshe Kuma Nima sai na wulakantata tunda Yar Iska ce,a ransa ya kulle irin wahalar da Zan Sha a hannunsa idan na Aure shi,da Kuma yanda zai kuntatawa Fu'ad.
Sai wurin Isha ya Bude min mota na fice abina,Ina fita Muka hadu da Islam ya kalleni shekeke a ransa yace karuwar gida,a fili yace yaushe Zan turo? Nace ko yaushe,hararata yayi a boye yace kin Amince? Nace ae ka turo,wata zuciyar tasa tana gargadinsa kar ya kuntata min Yana so na ba karya,Yana ta tunani har ya manta yace zai aureni ya rikeni tsakani da Allah,Allah sarki Islam mantawa yayi da komai yaci gaba da Nuna min soyayya Yana Yi min dinkuna ba karamin kashe min kudi yake Yi ba,Ni Kuma Sam bana sonsa da aure, Fu'ad shine kullum a Raina shine burina,Amma Ina kallo Abbi da Kansa tare da Yan Uwansa suka min wakilci tare da zuwa har kauyenmu wajen Affa,Affa yace kwandala bazai kashe ba suje ya bar musu Ni gaba daya,Abbi Haka Suka dawo aka saka ranar Aure na da Islam Nan da wata biyu,Islam sai murna yake yi,Ni kuwa kullum a bakin ciki nake,da dare nayi kuka na koshi,sai Shirye shirye akeyi tsakanin Umma da su Nene da Abbi,sai Islam dake doki Yana Murna,Momy Kam Tace wallahi tana Nan akan bakanta Babu Wanda ya Isa yasa Danta ya auri karuwar yayansa.
Fu'ad kuwa an daina ganinsa ma a gidan sai jefi jefi gaba daya baya hayyacinsa,Umma ta tambayeshi yace ba komai,Su Rabi suna Jin Labari Rabi ta kwala Ihu ta Dira tsalle tare da cewa karya ne Ina Raye Rumaila ta auri Dan gayu dangina karya ne,Ni ba a aureni ba a auri Rumaila karya ne,Kawai sai ganin Rabi nayi da Saude sunzo gidan da Ledar kayansu da yawa,Ga biki ya taho,Umma ta sa kullum sai naje gidan gyaran jiki,Ni ba son abin nakeyi ba.
Kullum Momy da su Khaleesat a Zagina suke ga su Rabi sun Karu,ga Son Fu'ad ya min yawa,ga matsalar dake tsakanina da Iyaye na,Naje makaranta na dawo karfe biyu,Momy a Compound ta tare Ni tare da cin kwala ta tana girgizani tana masifa da bala'i,Can Garden Kuma Abbi ya kawo masu karatun Qur'ani suna tayi zasu Yi sauka Wai Allah yasa ayi biki lafiya a Gama lafiya,Karatun da nake juyowa shi yasa naji kaina ya Sara Nan take na Kurma Ihu Aljanun da bani da su suka tashi,Ina girgiza na yage Hijab Dina na jefar na suri Momy Kamar tsinke nayi jifa da ita kanta ya daki jikin mota ta zube kasa sumammiya,idona yayi jajir Ina Ihu jikina Yana rawa,matan gida da Yan aiki Suka dauki ihu,Mazan gidan Suka yo kaina,Umma ta fito da Sauri, Fu'ad kuwa cikin Malam masu karatu ya taho da babban malamin,Islam ya fito da gudu,Ina ganin Malamin na Fadi kasa Ina birgima Ina wani irin Nishi,yatsan kafata ya rike babba ya shiga rero karatun Qur'ani,Wani Ihun nakeyi Ina birgima,Daga can malamin yace Kai waye?
Aljanin dake jikina ya fara magana Yana cewa sunana Salahu,Laifi tayi Mana me girma,Dan me zata kwara Mana ruwan zafi muna kwance muna Hutawa a makwararar gidansu,nazo Bara gidansu ta kwala min kwano tare da korata shi yasa Ni Kuma na shigeta na rigada na aureta Kuma wallahi sai Naga karshenta bazan taba fita ba.
Malamin yace yaushe ta zuba muku ruwan zafin? Aljanin yace tana shekara goma sun dafa taliya sun Tace Bata Bari ruwan ya huce ba ta zubo Mana Muna kwance dama Yan Adam Mata da yawa suna Mana Haka Basu San wajen hutawarmu bane sai Kawai su dinga sheko ruwan zafi Basu Bari ya huce,Nazo Ina Bara a gidansu na fito a siffar mutum yaro ta karbi kwanon ta kwala min a kaina shi yasa nace sai Naga karshenta Kuma wallahi bazan barta ba,duk Wanda ya aure ta ya auri masifa har danginsa ta Zama tawa,Nine na Sadu da ita,Islam najin Haka ransa ya baci kishi ya taso Masa yace Malam yanzu ko an daki Rumaila wa aka duka? Malam yace Aljani ka daka,Zumbur na Mike da Muryar Aljani nace au fada zakayi da Ifritu to Bismillah,Islam kishin Aljani ya sadu da matar da zai aura Fu'ad Yana rike shi Yana Karfa ka dake ta Islam,Malam Yana Kai Islam saurara Amma Islam Iya karfinsa ya samu ya zage ya Kai min Uban naushi sai da na tashi sama Zan fado kasa Fu'ad yayi sauri Allah yasa kusa da shi na taho Zan Fadi ya cafeni a jikinsa,Lokacin da Islam ya Kai min duk tunaninsa Aljani ya daka lokacin Kuma Aljani tuni yayi tafiyarsa ya barni aci ubana,Ina faduwa Aljanin ya dawo jikina ya shige abinsa yayi luf yasan Wanda ya aureni ya aurarwa Kansa masifa,Ni kuwa Suma nayi jini ta Hanci ta Baki,Dan rashin Imani su Khaleesat murna sukeyi,Suka kwashi mamansu sukayi asibiti,Islam ko ta kaina baibi ba yayi tafiyarsa wajen Momy dinsa Yana Bata Hakuri Yana cewa na fasa aurenta Momy bazan auri Aljana ba,Momy data Suma Nan take ta wartsake tana Jin dadi.
Abbi Yana dawowa Islam yaje yace ya fasa aurena,Abbi ya kada ya Raya Amma yace Sam baya so na yanzu,Ni kuwa Ina can Tuni Fu'ad yayi Hospital Dani Yana ta shara gudu,agajin gaggawa aka bani,Abbi ya bimu Asibiti daga baya shi da Umma,ba abinda likitoci Basu Yi ba akan na farfado Amma babu alama,Umma tana kuka Tace Kaine duk ka jawo wannan abin Fu'ad da ka amince da tashin hankali Bai samu Rumaila har aljanunta sun tashi ba, Fu'ad Hawaye ya zubo Masa karon farko yace Umma wallahi Ina sonta,Abbi ya kalle shi yace shashan banza,na fasa aurawa kowa Rumaila ko ta warke ta samo wani Mijin da kanta ta kawo, Fu'ad yace Please Abbi Zan haukace,Abbi yace ka Dade baka hauka ce ba ka dage ka nemi soyayayyarta,tana sona Abbi,Inji uban wa? Sai ka Bari na gani da Ido na, Fu'ad yace to zaka gani Abbi, Umma Tace Dan Allah karku damemu da wata Soyayya Rumaila tana wani Hali kana ji Doctor yace sai tayi kwana biyu ko Uku Bata farfado ba Kuma zata iya wucewa Kiyama, Fu'ad yace Wlh idan ta mutu sai na daure Islam har abada ya dakar min Mata
Abbi Yana takaici yace rufe min Baki.
Karshen Free page.
AsmaBaffa
[7/13, 8:42 AM] Sis Asma: ????????????????
DANGIN RABI
????????????????
NA KUDI NE
DUK WACCE TA FITAR MIN DA NOVEL DINA ZUWA WASU GROUPS ALLAH YA ISA BAN YAFE BA, A MADADINA DA DUK WACCE TA SIYA TSAKANI DA ALLAH AKA CI AMANAR FANS DA WRITER NI ASMABAFFA AKA FITAR MIN TO
ALLAH YA ISA
KUMA DUK WACCE TA GANSHI TA KARA TURA SHI ZUWA WASU GROUPS DA WANDA TA GANI BATA SIYA BA TA KARANTA KUMA TASAN NA KUDI NE AMANA AKA CI BAN YAFE BA,
SABO DA DUK WACCE TA SIYA BA IYA KUDI BANE SAI DA AKA AJIYE YARJEJENIYA KAN BAZA TA FITAR BA,TASAN DOKA TA KARYA,KO ADMINS MASU SON BIRGE MEMBERS NA GROUPS NASU SAI SU SIYA SU DINGA TURA MUSU,KU SANI AKWAI CIWO DA HAUSHI KUMA BAMU YAFE BA WALLAHI.
DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.
41-45
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
Maman Dee
Fatimamusasamaru
Balkisu
Mmn Saddeeq
Dr Zainab Abdullahi
Maryam Yamai Aliyu
A zaune Fu'ad yake gefen gadon da nake kwance ya tsura min Ido Kamar zai Hadiye Ni,sai yau ya taba min kallon tsaf a Nan ya gano lallai ba karamin kyau ne Dani ba, Allah yayi baiwa a Nan haka ya furta a ransa,a hankali ya furta Allah ya tashi kafadu Yar gidan Iyanta,Umma Tace me kake cewa? Istigifari nayi ya furta Kawai,Sallah ma da kyar ake tashin Fu'ad yaje yayi,har dare Yayi Umma Tace to ya kamata ka hakura Haka kaje gida sai gobe ka dawo,abinci Kuma su Tasalluwa zasu kawo da komai munyi waya, Fu'ad yace kije dai Gida ke Umma ai Ni ke nake Shirin fadawa ki tafi gida Har na Kira Driver zai maida ki gida,Kaga ban son shirme Ina ka taba ganin Namiji yayi jinyar mace? Gashi Zaki fara gani Umma,Abbi ne ya shigo da kayan shaye shaye na Lemuka da Fruits yace Kai Fu'ad taho mu tafi,Zaiyi magana Abbi ya daka Masa tsawa tashi nace baka da kunya ko? Kabi ka Raina mutane,Mikewa yayi Yana turo jajayen labbansa Yana tafiya Yana kallon inda nake a kwance Haka yabi Abbi dole Suka fita,Key din mota Abbi ya Mika Masa gashi ka tuka, Fu'ad ya kalli Abbi yace Ashe Allah yaji kan mu Allah Zan Shiga cikin Trailer Abbi gwara ka tuka Kawai idan Kuma kana so mu tashi gobe a kabari to na tuka mota,Abbi Baki Bude yace Bani mukulli tunda Kai ka haukace ma naga alama.
Tunda Abbi yake tuki Yana ta yiwa Fu'ad hirar business da zai tafi Italy,Uhm... Kawai Fu'ad yake Iya bada amsa har ga Allah hankalinsa baya jikinsa,Yana wajen Rumaila har Suka koma gida Haka ya fita ya manta ko motar Bai rufe murfin ba yayi gaba abinsa sai Abbi ne ya Rufe Masa,Islam ne ya tari Fu'ad yace Yaya Fu'ad ya jikin Rumaila? Harara Fu'ad ya watsa Masa ba tare da ya bashi amsa ba ya shige part dinsa, Baba Jummai ce ta taho da gudu tana Murna a ranta Dan munafunci tana cewa shike Nan nasan ma Rumaila ta mutu ko Dan Momy Fu'ad?,ai nasan dukan da Tasha da kyar zata tashi baza ma ta tashi ba,Allah sarki gobe Muna da babbar janaza, Fu'ad ya kalle ta yace kece dai Zaki mutu tsohuwar banza ya banko kofarsa ya Rufe ya bar Baba Jummai tsaye a bakin kofa tana jinjina rashin mutuncin Fu'ad.
Tunda Fu'ad ya shige part dinsa Wanka yayi tare da dauro Alwala yazo ya gabatar da Sallar Isha tare da nafilfili Yana ta min Addua Allah ya bani lafiya sai wurin 1am ya samu ya kwanta a saman gadonsa cike da tunanin halin da nake ciki da Kuma rayuwa ta a gidansu ta Shiga dawo Masa tun farkon ganina a gidansu,tunowa yayi ranar da ya fara gani munzo daga Kauye yana rungume Yan Uwansa na wara Hannaye Ina cewa muma ayi Mana,Dariya ce ta kwace Masa ya murmusa Yana cewa Allah sarki da na sani nayi mata,part dinsa Dana gyara Masa yace sai na maida Masa kurarsa ya tuno,Juyi yayi a saman lallausan bed dinsa yace Ban kyauta ba,Haka ya dinga tunano Rayuwata a gidansu wani wajen yayi Dariya wani wajen ya tausaya min har yazo lokacin Dana fadawa Abbi na amince Ina sonsa,shi Kuma yace Bai shirya ba,Nan take yasa Hannayensa biyu ya Shiga yamutsa gashin Kansa me santsi yaja tsaki Yana Jin haushin Kansa,ranar da kyar ya samu bacci ya dauke shi.
Da sassafe Yana Idar da Sallar Asuba tare da Azhkar wanka yayi ya shirya tsaf cikin jallabiya Brown Yana bulbula kamshi tun da sauran duhu duhu a gari ya shiga mota ya bar gidan sai asibiti,lokacin Umma ta Idar da Sallah tana Azhar Kawai sai Sallamarsa taji ya shigo,da mamaki Tace Fu'ad kaine? Ae Umma Ina kwana ya me jiki? Lfy Alhmdllh ta amsa tana cewa Wai Kai Fu'ad meke damunka ne?ko gari Bai Gama wayewa ba,Shuru yayi ya nemi waje a gefen gadon da nake kwance ya zauna,sai da ya tabbatar Ina numfashi sannan ya samu bacci ya fara daukansa sai gyangyadi yakeyi a zaune Umma Tace karka fadawa maralafiya a kanta ka karasata kana gyangyadi tashi ga Empty Bed can kayi baccinka a can,Bedsheet Umma ta shimfida masa a gadon da ba kowa dake private Hospital ne Kamar wani Hotel sabo da kyau ko Ina Yan kamshi da sheki,Kwanciya yayi kamar marar lafiya sai bacci ya kwasheshi,Likita ne ya shigo Yana shigowa yayi tunanin Fu'ad wani patient aka kawo yace ya akayi aka hada patient biyu a room daya Hajiya kina kallo baza kiyi magana ba,ki sanarwa masu kula da su,Umma Tace Dana ne fa tare muke Doctor Bai Jima da zuwa ba bacci ne ya dauke shi baka kula sosai ba Fu'ad ne fa, lokacin Doctor ya lura yayi Dariya sannan yace ai ban sani ba Ashe Oga ne,Murmushi Umma tayi,Doctor ya Isa kaina ya dubani tare da zare min Drip ya min wata Allura ya fita.
Bacci Fu'ad yake Yi sosai wanda sai da ya gaji Dan Kansa wurin 12pm sannan ya tashi lokacin an kawo abinci iri iri,Masallacin dake Hospital din yaje yayi Sallah sannan ya dawo Umma ce ta takura Masa sai yaci,Haka ya zabi abinda zai Iya ci yaci,Basu Dade da Gama ci ba Na fara motsi a hankali na motsa tare da Bude idanuwa na a hankali Ina bin dakin da kallo,Basu san na farka ba sai da suka ji Nace Salamu'alaykum Umma sannan suka juyo da sauri tare da rige rigen zuwa ida nake,ban San me ya faru da Ni ba Ina iya tuna Lokacin da Islam ya Naushe Ni sabo da lokacin hankali na Yana jikina,Kafin nayi tunanin komai Umma ta Kama Ni na tashi toilet ta raka Ni Brush nayi sosai tare da yin wanka na fito Fu'ad ya tafi Kiran Doctor,Har Umma ta bani wata doguwar Riga me siririn Hannu Yar kanti Bata da nauyi,Bayan na saka nace Yunwa Umma,Abincin ta zuba min tuwon danyar shinkafa miyar Egusi ga farfesun kaji a gefe,Ina Ci ya Fu'ad suka shigo tare da Likita,Doctor yace lallai jiki yayi kyau,Ya tambayeni Ina ke min ciwo nace Babu lafiya nake jina,Kawai wajen makoshi na Inda Islam ya nausa ke min ciwo, Wasu magungunan ya ru buta Mana, Fu'ad ya karba yaje ya siyo ya dawo lokacin na Gama cin abincina na wanke Baki na,Umma Tace to Alhmdllh Rumaila Bari naje gida nayi abinda zanyi ga Fu'ad Nan zuwa Yamma Zan dawo,To Umma na furta Ina Wasa da yatsu na gaba daya kunyar Fu'ad ce ta hanani sakewa,mugun kwarjini yake min ga kamshi ya gama tafiya da Imani na,a hankali nace Islam Allah bazan yafe Masa ba,ace Mijin da mace zata aura tun Ina budurwa Yana dukana Haka Ina ga anyi aure sai kace a film din China,wani kongfu ya min sai kace ya samu Jettly,Umma tana hada Kaya Tace kiyi hakuri shima bada saninsa yayi ba.
Kayan Dana cire Dana abinci Umma ta tattara ta kwashe Driver ya dauketa Suka tafi,daga Ni sai Fu'ad,ko kallon inda nake baya Yi sai latsa wayarsa yakeyi Yana murmushi shi kadai Ni Kam Kallonsa nake Yi kamar Zan cinye shi Haka nake ji,Uwar kallo Daina kallo na Haka,naji ya furta ba tare da ya kalle Ni ba,da sauri na dauke kaina gefe Amma ban San Sanda na sake dawowa da kaina dai dai ba Ina ta Kallonsa,Ki Fadi soyayyarki ki daina Bata lokacinki,Murmushi nayi nace ai Ni sai Islam,da Alama Baki San meke faruwa ba ai tuni Islam ya fasa,Da Sauri nace dan Allah da gaske ya fadawa Abbi ya fasa? Fu'ad yace da gaske,Dariyar farin ciki ce ta kwace min nace siyo Mana Lemuka muyi partyn Murna yanzu,Gasu Nan Abbi ya kawo kala kala,To a jera su,Empty Bed din da yayi bacci a Kai ya jawo Gaban mu ya shirya Lemuka da ruwa kusan kala goma,yace saura abin ci,Waya ya Kira tare da yin Order Abinci na Yan gayu,15mnt sai gashi an kawo abinci kala Uku masu shegen dadi na turawa Nan ma na jera su Muka zauna a gefen bed daya gadon Yana Gabanmu da kayan ci da Sha.
Abbi ne ya turo kofa yaga abinda Muka shirya Mun saka a Gabanmu,da sauri Fu'ad ya shiga cewa Happy Birthday to you,ku Kuma lafiya wannan tarkacen fa? Ina Ina na fara uhm....B... Birthday na ne yau,Allah ya kyauta ya jikin? Abbi ya tambaya,da sauki Alhmdllh,Ina wayancewa Ina kwashe Lemuka da sauran kayan ci,kwana biyu nayi a Hospital aka sallamemu,Duk abinda ya faru lokacin da Aljanuna suka tashi akwai a Wayar Khaleesat ta dauka a waya har dukan da nayiwa Momy,a garden suna Zaune da Safna sai Momy,Khaleesat Tace Momy kinga komai na Yarinyar Nan akwai a wayata da shi zamuyi amfani mu Kira Mata Yan Sanda,Kamowa tayi ta nu na musu,Momy tace kinga yanda tayi cilli Dani kamar Buhun auduga lallai Yarinyar sai ta ci malafar Ubanta har yanzu kugu na ciwo yake Yi saura kadan Lakata ta tsinke,Suna zancen Fu'ad yazo ta wajen Yana jinsu,Sai ya share tare da kwalawa Khaleesat Kira,Da Sauri ta nufi Inda yake,muga wayarki Zan dauki number Fadila,Bata kawo komai ba ta Mika Masa,Yana karba ya lalubo video din data dauka Ina Aljanu ya tura a wayarsa sannan ya goge na Wayarta gaba daya tare da Mika Mata Wayarta,harda tambaya kaga number din? Ae Kawai ya furta ya wuce abinsa,Ina zaune a Palo Ina kallo sannan ga littafin English a gaba na na Gama Assignment Dina,Yana shigowa saman 2seater ya zauna tare da yin wani Zama kana kallo kasan kudi ya ratsa shi,Muryarsa na tsinta yace zo ki ga wani Abu, Carbin dake Hannuna na ajiye naje inda yake zaune ,zauna ya furta,gefensa na zauna ya danno min video din da na daki Momy,Ina kallo na zaro Ido har Adduar da Malam yayi min da Maganar Aljanin,Ina kallon Dukan da nayiwa Momy na kyalkyale da Dariya tare da tafawa kaina nace Wow Wallahi na godewa kaina,Weldone Rumaila Weldone ,Sabo da murna ban San Sanda na sakalo hannu na a wuyan Fu'ad Rabin jikina gaba daya a jikinsa,na shako shi sosai tare da lankwaso wuyansa Ina ta dariyar dukan Momy da nayi.
Duf nayi ganin yanda Malam yake min Ruqiyya suna magana da Aljanin dake jikina naji tsaf duk Abinda Aljanin ke furtawa,Tashi nayi da sauri Raina a bace na dauki carbi na tare da Zama na kalli gabas na Shiga Jan carbi Ina cewa Allah ya Isa Aljani Salahu,Allah ya Isa Salahu,Allah ya Isa Salahu Haka nake ta fada Ina Jan carbi, Fu'ad Dariya ce ta kamashi yace karki damu Yan Mata zanyi manage da ragowar Salahu,Duk da ya rigani Jin dadin wajen ya za ayi,Ashe Dan Iskan Nan ne ya fito Miki a suffata ya cuceni duk ya Bata min suna a wajen mutane,Kai Nima nace Allah ya Isa Aljani Salahu,Dariya nakeyi nace munafuki harda laulayi na dinga sheka amai da yawu,To Kira Iya a fada Mata ko ta hakura ta yafe miki cewar Fu'ad,Nace tsaya na Gama jawa Aljani Allah Isa ko cikin carbi ce,Ki lallaba shi kina ji yace duk Wanda ya aure ki ya auri masifa,Ni kuwa Haka zanyi ta maza a daura Dani mu Kara Dani da shi,Wayata na dakko na lalubo number Iya tare da kiranta,naci sa'a naji ta daga sabo da kar ta kashe idan taji muryata,ban Mata bayani yanda zata Gane ba kawai nace Iya Salahu
Ne ya min ciki,Kya fito ma ki Fadi gaskiya ai sai kije wajen Salahun ya aureki,ba mutum bane Iya Aljani ne,Karyarki tayi yawa Ni Zaki dinga rainawa hankali kince babu ciki yanzu kin dawo kince Salahu ne,Tsaki Iya ta ja tare da kashe Wayarta Ina cewa Iya ki tsaya kiji Amma Ina.
Baba Jummai ce ta shigo tana Galla min Harara ta ganni kusa da Fu'ad Tace Ashe kin dawo Baki mutu ba,ai nayi tunanin wannan dukan da kika Sha sai dai ki farka a lahira,Nace to kwana na Bai Kare ba sai ki kashe Ni da kanki,kar dai ki min rashin kunya dama Sannu nazo na Dan Miki Kuma tunda ke fitsararriya ce na fasa tayi tafiyarta,Nace Lallai tsohuwar Nan duk mutuncin da na Mata Bata gani ba Ina kallon take takenta tun da dadewa haushi na take ji, Fu'ad yace kyaleta Watarana korarta zanyi da kaina daga aiki,yawwa kayi Mata sanadi abincinta ya Kare.
Bayan Sallar Isha Ina kitchen Fu'ad ya shugo sanye cikin Riga Armless sky da wandonsa dogo yayi kyau sosai,Kamshinsa yasa nasan yazo Amma ban juyo ba,Hannayensa ya ware Kamar zai rungume Ni harda tsayawa daf da Ni kamar zai rungumeni ta baya,A hankali yace kamar na rungumeta a haka,da sauri na juyo naji kamar Yana magana kafin na Kai ga juyowa cikin zafin nama ya juya tuni ya kalli kofa kamar Bai San Dani ba,Aiki na naci gaba da Yi,Jelar gashi na ya taba da yatsansa Guda daya yanda bazan ji ba, Hips Dina ya kalla tare da cije lebensa na kasa,kafin na juyo sai Naga ya juya Yana latsa waya kamar Bai ganni ba.
Sake matsowa yayi daf Dani nayi sauri na juyo Dan na kamashi Amma sai na hade da jikina da nashi, da sauri ya matsa gefe harda masifa tun dazu kike so sai kin rungume Ni na matsa kin matso na matsa kin matso Haba dole sai kin Sa na dauki zunubi me yasa kike so nane da yawa Haka? Ance ki fadi gaskiya kinki,Baki na saki Ina Jin sharrin da ya Yi min, Palo ya koma ya kwanta Kamar Wasa bacci yayi gaba da shi dama sarkin bacci ne,Fitowa nayi dauke da plate din Fruits,a gefe na ajiye plate din a hankali Ina Sanda na karaso gabansa tare da tsugunawa a saitin fuskarsa Ina Kare Masa kallo Ina wani murmushi,Gashinsa na taba kadan a Raina na furta laushi,wuyansa na karewa kallo wani lumi lumi a hankali na shafa wajen,a hankali ya bude idonsa Wanda cike yake da bacci,na kalle shi da kunya nace tururuwa ce take maka yawo a wuya shine na cire maka,Idanuwansa ya maida ya rufe yace maida min da tururuwata dadin yawonta nake ji a wuyana,ya Riga ya ganeni,naci gaba da Masa tafiyar tsutsa Ina cewa tururuwa ki sauka idan ta maka Kashi a wuya ba ruwana,Umma ce ta shigo da Sauri na koma cewa ka tashi na yanka Fruits din tun dazu nake ta tashinka,Umma ta harareni Tace kya Gama gulmarki marar zuciya, shi kuwa harda yin shuru Wai yaci gaba da baccinsa.
Iya a zaune take saman kujera a tsakar gidansu sai fushi takeyi Taki kula kowa ko Baki ne suka shigo Bata musu magana,Ali Shagali ne ya shigo Iya ta bishi daki Tace Ni fa na fada maka ko Tv ko saki,Nima kayan kallo nake so ka siyo min,bani da kudi bani da inda zan samo su,idan na siya Miki Kayan kallo ita abokiyar zamanki Kuma tayi ya?dole sai na siya muku tare,to ba kayi kudi ba Ni Kawai ba ruwana Malam TV Kawai,Me shayi bakin cikin Halayen Iya sun dame shi yace Jeki gida sai neme ki kin dame Ni na gaji,naji Kuma Zan tafi gidanka din banza mene ciki Banda talauci, me kake da shi,Naji kije sai na nemeki,Zaka zo neman Nawa ne wlh baza ka ganni ba,Iya kayanta ta kwasa da yawa kishiyarta tana kallo tana ta Mata Dariya,Iya Tace kin wa Uwarki Dariya,Uwarki me Dambu ita kika yiwa Dariya ba Ni ba,me Shayi Iya ta gallawa Harara ta fisge dubu daya a hannunsa wacce ya fito da ita zai Aiki yaro ya siyo musu kifi soyayye zasu ci abinci Amma Iya ta fisge kudin tace sai dai ka dakko wata tayi tafiyarta gidanta ko gidan yayanta Malam Haruna bata nufa ba,gidanta Wanda ya kusa ruftowa Nan Iya ta koma da kayanta.
Baba Jummai ce ta fito kitchen dinsu na masu Aiki tana cewa Tasalluwa kije bangaren Umma kiga Yan Wutar Sakata suna can suna ta bariki a bainar mutane Rumaila da Fu'ad,ai gwara su da ke tunda ke ma cewa kika Yi Hotel Zaki Kama idan kina da kudi Daki permanent ki samu Ana kawo Miki gayu kina biyansu kudi,ba gwara su dake ba cewar Tasalluwa Baba Jummai Tace ke dama Tasalluwa ai munafuka ce Wai ke ta Allah ko? Zaki gani,Ana Haka sai ga Fadila Niki Niki da Kaya tare da Rabi,Ni na manta ma Rabi tana Abuja Ashe gidan Fadila aka tura Rabi ta tayata aikace aikace,sai ga Fadila ta rike Rabi tam ta shigo tana rusa kuka,Itama Rabi tana kuka ko me ya faru oho,Momy dasu Safna sune Suka fara damkar Rabi tare da rufe Rabi da duka Tim Tim Rabi tana Ihun kuka tana bada Hakuri,Momy Tace kin kashewa 'yata Aure shegiya bakar jaraba,gashi Nan kin jawo ya saketa biki ko shekara ba a ayi ba har an sako ta ji kake tas...tas Ana ta kashe Rabi da Mari,sai da suka yiwa Rabi dukan kawo wuka sannan suka fatalo ta tsakar gida tare da kayanta, Bangaren Nene tayi tana rusa kuka,Nene Tace lafiya me ya faru? Rabi tayi mukus tambayar duniya Rabi Taki fada sai Momy ce tazo Tace ai baza ta fada ba munafukar banza Wai Haka Kawai ta fashe da kuka Tace Mijin Fadila ya mata fyade,shi kuma ransa ya baci yace ta kawo wata tayi masa sharri sabo da Haka ya saki Fadila su tattara su bar masa gida,Nene Tace Subhannallahi ke Rabi ya Haka? Rabi tana shesheka Tace na Rantse da Allah Fyade ya min lokacin ta tafi unguwa gidan biki ya bani lemo na Sha shike Nan nayi bacci sai Farkawa nayi na ganni a dakinsa ya min Fyade,kwana Uku Ina fada Mata ta bincika sai tayi son zuciya Tace Zanwa mijinta sharri......Rabi ta sake rushewa da kuka,Sanda taga kullum sai nayi kuka shine ta tambaye shi ko da gaske ne shine yace ya sake ta anyi masa Sharri.
Ni Wallahi da na sani bazan taba zuwa birnin Nan ba gaba daya tsinannu ne na cuci kaina,dama zuwa nayi Nima na samu wani Saurayin a gidan Nan ya aure Ni kamar yanda Rumaila ta samu Ina bakin ciki ace ba Ni bace za a aura tunda nice ma Yar Uwar gidan Nan Momy tace naje na dinga Taya Fadila Aiki,dama tunda naje mijinta sai yayi ta kallon duwawuna Yana mintsina min Ido daya,ko idan tana daki sai ya fito inda nake yayi ta shafa min kafata,dama wallahi kwarto yarki ta aura Kuma ba Dan Allah ya aure ta ba Dan ya biya bukatarsa ne gashi Nan idan da Dan Allah ne ai bazai saketa ba,Kuma wallahi Alo tsiya Alo Danja wallahi sai kin biya Diyyar fyaden da aka min ai kece kika jawo,Rabi ta furta tana nuna Momy da yatsa.
Momy Tace kashe ki akayi da Zan Biya Diyya,Diyyar Ubanki Zan Biya?kwadayi da bakincin Rumaila shi ya kawoki ga shi kin jawa kanki Hassadarki ta jawo Miki,Rabi ranta ya baci dama Rabi Bata da kunya ko digo ga masifa,kirji ta turo gaba ta hade kirkinta Dana Momy sabo da Momy ba tsayi Rabi akwai tsayi shi yasa ta jijjiga kirjin Momy da nata Tace Sanda kika moreni Harda turani nayiwa yarki bauta Ubanki kika bani?ko kin taba min kyauta? To wallahi bazan koma Kauye ba ko ciki na samu sai na haife muku a Nan matsiyata,Momy Baki Bude take kallon Rabi,Mama ta shigo da Iyayinta Tace to mutan Kauye ga kwadayi wa ya kawo ki? Rabi Tace Uwarki ta Zamfara ta kawo Ni,Mama ta zaro Ido ta tuno Rumaila duk abinda suke Mata Bata taba zaginsu ba,Amma Rabi zagi Kamar ta samu yara kanana Haka take zura musu son Ranta,yarinya Karama ta zazzage su ko sun rama Basu fanshe ba,Shigowa nayi na iske su a Haka Rabi tana ta zaginsu,Wani Bowl na roba da cokali na dakko a kitchen na fito Ina kadawa Ina Waka ku chasu arna ku chasu ku chasu ba Mai Raba ku Ina ta dariya,Su Momy Suka ja jiki Suka koma bangarensu da mamakin yanda Rabi ta zage su,Nene Kuwa Kora ta tayi tana Baki da kunya ko Rumaila,Kiran Abbi Nene tayi ta sanar masa a waya,Wani yaronsa ya turo da wuri ya dauki Rabi zuwa Asibiti akayi bincike Allah yasa ba komai a tare da ita sannan Likitan ya samu dai ya Mata Allurai Wanda zasu wanke mahaifarta koma mene zaiyi waje gudun kar a samu matsala,sai lokacin Hankalin Rabi ya kwanta,Amma duk da Haka Bata kulani Kuma duk gidan Nan Bata kula kowa sai Nene sai Abbi.
Shi Kam Abbi Mijin Fadila yake ta Kira a waya Amma yaki dagawa ma bare ayi wata magana.
Ina zaune a Garden Ina karatu sai ga Fadila ta taho da sauri ta buya tana waya da mijinta tana rokonsa tana cewa Dan Allah kayi Hakuri Honey,kasan Ina sonka wallahi Zan gyara Zan dinga baka kulawa na daina abinda nake yi,kaga makiya suna ta min Dariya yanda ka sake Ni da wuri sabo da Allah ace ko shekara banyi ba ka sake Ni,Mijin yace Ina ruwa na wanne irin fada ne ban Miki ba sai da kika jefa Ni a masifa na murkushe Yar mutane nayi Mata Fyade a banza kin cuceni,Fadila Tace Honey ka dubi girman Allah na rufa maka asiri har yanzu naki yarda na Fadi cewar Kaine kayi Mata Fyade,Yarinyar ma an kaita asibiti anyi Mata wankin Mahaifa Bata da komai naka,yanzu Ni Zan gyara, sau Nawa kake so kullum ka dinga Sex Dani? Mijin yace Sau biyar sau hudu sannan idan zanyi baccin Rana dole ki kwanta kusa Dani ko baza kiyi bacci ba dole sai kin kwanta a jikina,Sannan kafin nayi bacci ki dinga lashe min kunnuwa na, Ina Jin komai ina ta boye dariyata ban San Sanda na saketa ba,Ashe duk Wayar da Fadila takeyi tayi shuka a idon makwarwa Ina ji ita tunaninta sirri takeyi,da sauri ta kalli inda nake daf da ita ga waya a Hands Free,nace ke Fadila Ashe maye kika aura harda lasar kunne? Duk a jikin nasa a rasa inda Zaki dinga lasa sai kunnuwa,Zanci Uwarki wallahi Ashe kina Nan munafuka,to Ni na kawo ki kece Baki ganni ba hankalinki Yana can kina ta zubar da ajikinki kina bin Namiji ya dawo da ke,dama laifin da kikeyi kenan? Bakya bashi kayan Aiki kin jawo yayiwa Rabi Fyade Ashe Hariji ne,Oh kalle shi a Riga Kamar salihi Ashe Terror ne,Kai na cikin waya kayi Hakuri har Bayan keyarka duk zata dinga You turn daga kunne zuwa keya tana lashe maka, Allah yasa ba kurajen aski ko Almajiran keya a kasan keyar taka,Fadila kaina ta yo zata dukeni na Mike da Littafi na nayi ciki,Lokacin akace Abbi Yana Kiran kowa na gidan a palon da ake Family meeting,Ina Jin Haka nace na kusa Zama Amaryar Fu'ad shike Nan Aure na ya taho ai taron Abbi baya wuce hada Aure,har kwalliya nayi nasa Kaya masu kyau Wani material doguwar riga dark Brown nayi kyau karshe,tare da Umma muka Shiga palon,Ina ta washe Baki na kalli Islam na daga masa Hannu nace baka da Rabo a gidan duniya sai dai ka Tara a lahira,ba Wanda ya Gane me nake nufi,Tsallake kowa nayi na koma kusa da Fu'ad na zauna nace yawwa a Nan zanfi iya bada amsa.
Rabi ta harareni da su Momy,Fadila Tace wallahi sai na Kai kararki bari Abbi ya shugo,Rabi Tace Ni Kuma zanyi tonon silili ba,nace Ni Kuma Zan tona Miki asiri ba kin San halina,Umma ce ta harareni nayi shuru idan na kalli Rabi sai na kyalkyale da Dariya kasa kasa,Kamar abin arziki nace Rabi Ashe Sharing kukayi Kuma? Rabi Tace ke kika San wani Shiyare(Sharing)Ni Zaki Nunawa Boko yaushe kika daina cin zogale da Rama har Zaki Raina min wayo,Abbi ne ya shigo da Sallama muryata tafi ta kowa fitowa wajen amsa Sallama,nace ko watan gobe ne ko watan jibi ne bikin nawa oho,Allah yasa asa bikin watan daf da babbar Sallah naje nayi ta suya a dakin Mijina,nasan ma Sa ko Raguna Biyar zai yanka min tunda da kudi, Fu'ad Yana ji Ina magana Kamar kunkuni nakeyi Bai Jin me nake cewa,Ai kuwa da Sa ne Za'a fi samun nama me yawa,Umma a Bata Cinya daya,Na aika da Cinya biyu wajen Affa can Kauye,Iyata na Bata hakarkarin sa,Sauran Kuma ya ishe mu sai Wanda za a bawa talakawa su tsotsa Suma,nace Kai Sa daya yayi kadan Ina lna laifin Sa da Rago biyu,Abbi ne yace wace ne take ta kunkuni sai humhumhum...Kawai muke ji ayi shuru zanyi magana,Shuru nayi tare da nutsuwa sosai.
Sharhi fans Dan Allah
AsmaBaffa.
[7/13, 8:42 AM] Sis Asma: ????????????????
DANGIN RABI
????????????????
NA KUDI NE
DAN DARAJAR ALLAH FANS KARKU FITAR DA NOVEL DIN NAN DAN ALLAH.
DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.
51-55
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
Maman Saddeeq
Ilham
Mrs Chief Ban
Ina zaune bakin Bed Ina tuna halin Rabi data canja kamar ba ita b Rabi itama tabi layin su Momy Dan Rashin zuciya Bata saurari bikin ba musamman data ji Ana labarin gidan da Fu'ad ya kera kamar gidan wani Senator yafi ma na wasu Senate din,Har da me kula da Compound Garden da komai na gidan,mace Kuma Guda daya Dattijuwa me kwazo Umma tace za a kawo min Bayan wasu satikai zata dinga tayani aikace aikacen gida sabo da girman gidan,Motocin Fu'ad wajen Guda biyar masu tsada,Ni kaina na Matsu na tashi na zaga na kalli gidan,Amma ance kar na tashi sai ango yazo,a fili nace Ni fa na gaji har yanzu yaki shigowa wallahi Nan da 30mnt idan Bai zo ba kallo na Zan tafi na kyale shi,Duk da Haka shuru Ina ta jira,Har Zan tashi sai naji Ana ta kulle gida nace maybe shi kadai ne sabo da yanzu maza da yawa sun daina Shiga dakin Amarya da abokai,da Sauri na koma na zauna tare da lullube kaina da Mayafi me sharara.
Da Sallama ya shigo na amsa Sabo da Ni ko kuka banyi ba to kukan me zanyi dama ba a gida nake ba na rigada na bar Gaban Iya bare nace zanyi kukan rabuwa da ita,Ta cikin Mayafi na nake ta Kallonsa ya hadu shaddar ta Masa kyau wata ruwan kunun kanwa Inji Yan garinmu,Tsayawa yayi yaki Zama nace ka zauna mana,Ina Kallonsa Yana hararata,Ledar take away dake Hannunsa ya ajiye min,nace Wai baza ka cire min lullubin ba Kai baka koyi yanda akeyi ba,kiyi ta Zama a lullube karki Bude,nace to Dama Kara nayi Dan kar ace nayi rashin kunya Amma Allah na gani lullubin ya dameni nasa hannu na cire tare da ninkewa na ajiye a sip Ina cewa Umma tayi min fadan tattali,Murmushi yayi yace Allah yasa kiyi Aiki da fadan,gashi nayi ma na Adana mayafina da wata ce da tuni a Kan gadon zata jefar da shi,Sai lokacin ya zauna a gefen Bed din ya tsura min ido,ban kulashi ba na jawo akwatunan Lefe na tare da Bude su gaba daya Ina kallon kayan da aka zuba min,Wani lace na dakko na daga shi Sama tare da tambayarsa Yaya kaga wannan ka Iya zabe Dan Birni, Shadda na dakko Tasha dinki nace ka iya zabe ya ka hango Ni a ciki? Fu'ad sai lokacin yayi magana yace Muni zakiyi,kayan bacci na Shiga dubawa nace,sai da yaga wata gantalalliyar Riga Sharara kamar net yace wannan zata Miki kyau,Ido na zaro nace dama Haka kake? Ina ganinka ba ruwanka Ashe Kai kafi kowa ma,ai gwara Kawai kace na kwanta tsirara banga amfanin ta ba,jambaki na dakko pink nace wannan fa a dinga shafa maka? Da Sauri yace ae wannan dai dai lasa ne, Ina Dariya nace tunda aka lashi kunnuwa ma Ina ga lips ai shi a cinye shi kawai.
Kayi Aiki wajen siyen kayan Nan,da Kansa Akwatunan ya rufe ya maida inda suke yace Alwala za muyi Sallah,nace daga ita sai cin kaza na sani,Daga Kazar fa? ya tambayeni,nace Salahu ya Gama Yi maka wajen an wuce Nan wajen sai dai bacci Kawai,Hararar Wasa ya min tare da furta Alwala fa, ba musu na Shiga toilet nayi Alwala na fito shi Kam Yana da Alwalarsa, Sallah ya ja mu Nafeela raka'a biyu tare da adduoi,Muna Idarwa ya tashi ya tafi ya barni,na jira shi har na gaji sai Kawai na jawo kaji na da kayan ci iri iri Dana Sha,naci na koshi na maida sauran kitchen,wanka nayi da brush na fito na shafa body lotion Dina,Kamar yanda Umma ta koya min shafa farin miski a gaba na,banson kamshin me Kalar Ruwa nafi son me Kalar Madara kamshinsa yafi min dadi,kadan nayi amfani da shi sai sauran turaruka na Jan Hankalin me gida,Ni Kawai sawa nayi sabo da Umma Tace na dinga amfani da su ba don miji na saka ba sabo da kuruciya da yarinta da tayi min yawa,ga karancin wayewa duk da na waye Amma har yanzu ban Gama karasa gogewa ba,sai dai a jikina da kwalliya tare da iya sa Kaya, na Gama gogewa anan shima Dan Ina da kyau ne ga jiki na me kyau gani fara sai kaga Kamar a birni na taso duk abinda na saka kyau nake Yi.
Rigar bacci na zaba Yar karama da kyar ta wuce Mazaunai na,me siririn Hannu jikinta me santsi silk ce me fito da sura gata Yellow me adon flower Maroon,nayi kyau matuka,Powder na Dan shafa sama sama tare da lipgloss,gashi na na taje na gyara shi sosai Yana kamshi sosai, Fu'ad Yana bedroom dinsa hadadde kafin ya shigo sunci abinci tare da friends dinsa shi yasa yayi wanka ya shirya cikin kayan baccin sa Sky blue and white marasa nauyi,wandon 3qtr da Riga me gajeren Hannu,Sai kamshi yake bulbulawa,Hadari ne ya taso aka fara walkiya da tsawa Nan take ruwa ya kece, Fu'ad kofarsa ya Bude zai dawo dakina ko ya kirani na dawo dakinsa Kawai kafin ya fito yaji kafarsa an rike ta Gam,ji yayi Kamar an sa Igiya an daure Masa kafafu,karfi yasa dole sai ya fisge kafarsa Yana fisga ya Fadi a kasa Tim,Ni kuwa jinsa shuru yasa na fito zuwa dakinsa na ganshi a kwance a kasa,da sauri na Shiga dakin lna cewa lafiya ya Fu'ad? Kallo ya bini da shi yanda na Gama tafiya da Imaninsa,Nace Wai lafiya kayi shuru,Hannunsa na rike tare da Mikewa tsaye na jashi sai ya tashi Kuma da Kansa ya koma saman Gadonsa ya kwanta Yana murmushi yace kwanciya Kawai nayi,Nima ban kawo komai ba nace Kuma a Kofar daki?, Kai ya daga min Yana cewa hauro saman bed din,Hannayena biyu na saka a saman gadon sai da Rabin jikina ya hau gadon Kawai naji Suuuuu an janyeni na koma baya tare da fadawa kasa,Mikewa nayi nace kut kaga jiri nakeyi, Fu'ad yasan Kan lamarin ya kama Dariya yace taho mu kwanta,tashi nayi na koma naji an rike min kafafu Kam,Kuka na saki nace wayyo kafafuwana, Fu'ad yace Nima Haka aka Yi min zanje Dakinki,Nace rike Hannu na ka jawo Ni, Fu'ad yace Haka Kawai naje a karya min hannu ba ruwana,Dan Allah ka jawo Ni na furta na hada uban Zufa,Hannu Fu'ad yasa tare da riko Hannu na Yana ja yaji kamar ya jawo katon Dutse,ya jawo da karfi aka dada Masa uban duka a Bayan hannunsa sai da fatar wajen tayi ja,Ya sake Ni da sauri yace saura kadan na karye Salahu yazo ba ruwana sai dai ki kwana a kasa ko ki koma bedroom dinki, Pillow da bargo ya jefo min,Ina shimfidawa na kwanta sai naji an sake min kafa na dawo normal, Fu'ad pillow dinsa ya dakko ya dawo da Kansa saitin kaina Yana sama Ina kasa.
Nace Salahu yana gari, ai idan ya hanani tabaki Bai Isa ya hanani kallonki ba cewar Fu'ad,nace ae kalleni na turo Masa fuskata gaba,yace Ke ba fuskarki nake nufi ba,jikinki nake nufi ki cire rigar na kalla,kunya nake ji Ni gaskiya,shike Nan na daina kulaki ya furta,rigar na cire kafin Fu'ad ya kalleni ba Kaya an tsokane Masa ido,Kara ya saki ya Danne fuskarsa da pillow Yana cewa ki saka rigarki,Nayi sauri na saka Ina ta Masa dariya,Ba Wanda ya sake magana Shuru Mukayi sai Adduar bacci da Mukayi Fu'ad shi ya fara bacci sannan nima ya kwashe Ni,ga gajiyar biki,Da Asuba Fu'ad Bai kulani ba Yana tsoro kar azo ya Kuma shiga masifa a banza,jikin bed ya bubbuga na tashi,Ina tashi ya wuce masallaci,Ni kuwa Dakina na koma,Bayan nayi Sallah da Azkhar tare da Kai kukana zuwa ga Allah,bacci na koma shima Fu'ad Haka.
Sai Bayan 11am Naji Door bell,lokacin na tashi nayi wanka na cakare cikin atamfa ta ruwan Toka da Baki,Riga da skert dinkin ya kamani daf,nayi dauri na zamani Ina kamshi na fito tare da sakkowa daga matakalar bene,Ina budewa naga Naila da kwandon Abinci daga Umma,Hararata tayi da Gadara Tace Ina Dan Uwana? Nima da Gadara Ina yatsina fuska kamar naga kashi Nace Baki Iya gaisuwa ba? Kamar ba Tarbiyyar Umma ba,Nifa yanzu na zama yayarki ki taka a Sannu,Bangajeni tayi ta wuce Karaf a Kan Idon Fu'ad daya fito yasha wanka cikin wani Danyen yadi, ya kalli Kanwarsa Naila yace Baki da kunya Ashe Zaki iya Bangajeni tunda kika bangaje Rumaila,Ai Rumaila ba Kai bace Yaya Kuma Ni na tsaneta ya zata min rashin kunya Bayan na girme ta,in banda ma kaddara ta Isa ta Hada ko hanya da Kai tana Yar matsiya.......Tasssss kake ji Fu'ad ya gasawa Naila Mari,wani Marin ya kawo Mata ta taka da gudu tare da Bude kofa tana kuka,Na jefa Mata gyalenta nace ki taka a Sannu yayarki ce Ni yanzu,karki ganni yarinya kice Zaki dinga kawo min Raini,Kofar na rufe na juyo cike da murmushi na kalli Fu'ad Nace ka birgeni daka kwadawa Naila Mari Kamar Ni ta zageni Ina matar yayansu,Basket din ya karba a Hannu na tare da ajiyewa a saman Dining, Fu'ad Ya min kyau da yawa,juyowa yayi da Niyyar min magana,ba zato na Rungume Shi a jikina,yace tab lallai Salahunki yayi tafiya,Dariya Mukayi gaba daya na dago da kaina Muna kallon juna nace ko ya tafi China ko India Oho,Fu'ad yace bacci yake Yi Bai tashi ba,Yana can yayi nauyin bacci,nace wani shegen yace kar yayi bacci da wuri ya tsaya takura Mana ai gashi Nan ya kasa tashi da wuri,Kamar daga Sama muka ji ance kyaleku nayi,Bamu ga Wanda ya fada ba,Kallon juna Mukayi, Fu'ad yace Ni dai gaskiya na fara tsoronki Kuma
A hankali ya rankwafo da kansa Muna facing juna Muna sakarwa juna murmushi,Saman tsinin Hancina yasa Harshensa ya Dan lasa tare da manna Masa Kiss,Nace Kai Kuma da Hanci ka fara? Ganin kamar Ina so yayi kissing Dina sai ya fasa da tsokana yace ban Iya abinda kike so ba,Ina a jikinsa na fara shagwaba Ina juya idanuna nace ka Iya mana,ke ai kin taba Yi da Salahu Ni kuwa saurayi nake Virgin ban San komai ba,Wanda ka sani Allah ya toshe maka Basira ka manta gaba daya ka yarda? Dariya yayi yace a'a bance ba,idan na manta ai kece a ruwa,Ina da Salahu,Fuska ya Bata sosai kishi ya kamashi,ganin ransa ya baci nace I'm so Sorry,Karya Salahu yakeyi ba abinda yayi,ta ya kika San ba abinda yayi dake? Bayan kince har Jini kin gani da kyar kika iya tafiya zakice baiyi komai ba,ganin da gaske yakeyin kishin nasa nace Zobon Aljanu ne fa ya zuba a gadon ba jini bane, murmushi yayi kadan,kankame shi na sake Yi,Saman kujerar Dining ya daura Ni,cike da Shagwaba nace Ni a cinyarka zan zauna,Yace a'a akwai matsala,wacce matsala Kai da ba ruwanka da mata Me zaka ji gani Yar yarinya,Damunsa nayi sai na zauna a cinyarsa yace leko to ki gani,Cinyarsa na leka na gani Hajiya Babba ta Mike,Kunya naji nace gaf take da yin Amai tayi fushi Wallahi Allah ya Bata Hakuri,plate da cups na kawo da sauran kayan bukata da kaina nayi Serving nasa sai kallo yake Bina da shi,Idonsa duk ya canja, Ni kuwa nasan na birge har wani Kara Iyayi nake yi,Tea cups dinsa na dauka na Dan kurba nace Uhm naka yafi dadi na janye nasa na tura Masa Nawa ,Slize Bread na Bude tare da saka Masa tsokar Naman kaza a ciki na rufe na bashi a Baki da kaina Yana ci Nima Ina ci,Kazar na yago na sa Masa a Baki ya fara ci na Mike tare da hayewa Saman Table din kumatunsa na rike da Hannaye Biyu nace to bani naci Ina magana da wani salo,mamaki ya Gama kashe Fu'ad ta ya nasan wannan soyayyar, shi yasa ya kasa komai Yana kallona Ina abinda naga dama Ina bashi mamaki,a ransa yace tun ba a yi nisa ba kenan Nan gaba abin sai ya fi Haka,yarinya sai nuna min take yi ta fini wayewa,zanyi maganinta,Bari fada na ya Kare da Aljaninta.
Sai da muka Gama cin abincin na kwashe komai tare da gyara gidan a Nan Nasha kallon gidan kamar Zan Suma sabo da murna, Fu'ad Yana Palo Yana kallon News ya kwanta ga waya Yana latsawa na sake karewa Palon kallon nace Karya kakeyi Yahuza Kafinta wane Kai,Allah ya tsallakar Dani hawa gadonka, Fu'ad yace kin takurawa Yahuza ki kyale bawan Allah tunda Bai Miki Kayan dakin ba, Murmushi nayi Bayan na Gama Aiki na ko Ina ya sake daukan sheki da kamshi ga Ac tana kada Raba,Kitchen na shiga Ina duba kayan Abinci,bangaren Curry na duba Naga Babu wata kala da nake gani Umma tana yawan Amfani da shi,wayata na Shiga latsawa na Kira Wayar Umma Ina fitowa daga Kitchen,Gaisawa Mukayi da Umma nace Umma Babu Curry din Nan me Kan Zakara,Girkin Rana zanyi karki kawo Mana abinci,Dariya Umma tayi Tace yanzu Rumaila akan Curry daya shine sai an kawo Zaki iya girki,Kuma ba me Kan Zakara ake cewa ba Wannan bokon kuwa Ana ganewa,da sauri nace Umma Chicken fragrance ko? Ba Umma ba har Fu'ad Dariya yayi,yace ance Miki turare ne?Zan Aiko Miki da shi,To Umma mun gode na Furta tare da nanatawa Umma me Kan Dan Zakara na kashe Wayar.
Iya an samu kudi sai ga Iya Tace Allah ya Mana Arziki ta kirawo masu ginin Bulon Siminti aka rushe ginin kasa aka Gina Daki biyu manya tare da katanga me tsayi ta zagaye gidan sai kitchen da Toilet ta sumulmule ko Ina na gidan harda paint Milk color,duk kudin da Iya ke samu Tarawa takeyi gashi tayi gida me kyau harda Dan siyo kayan kitchen masu Dan Araha,Daki daya ta sa Masa carpet Maroon da katifa katuwa,daya dakinta Kuma aka zuba Furniture na talaka dai dai kauye.
Ko da Me shayi yazo Biko na Uku cewa tayi duk me so na sai dai ya dinga zuwa gidana idan na gaji da mutum na sake shi ma'ana na koreshi tare da jefo Masa jakar kayansa,Shi Kuma me shayi Yana son Iya Amma Haka yace shi Kuma bazan Iya Zama a gidan mace ba ya rubuta Mata takardar saki,Iya harda murna Tace ka taimakeni wallahi dama ji nake wani kababa Igiyoyinka duk sun daureni sun hanani walawa yanzu ka kwance ni Alhmdllh.
Bayan Iya ta gama Idda, wata kawarta Dake Aiki gidan masu kudi a Kano itace ta bawa Iya Shawara tazo gidan da take Aiki suna Neman Dattijuwa mace,Iya Tace dakata Hajiya Mero Nawa suke biya a wata? Mero Tace dubu Uku,Iya Tace cab ai gwara na zauna a Nan naci gaba da kiwon kajin Hausa ko na fara surfe da daka,Hajiya Mero Tace to akwai Wanda ake biyan dubu Biyar duk wata? Iya Tace Dama dama,Amma kin San Banda Hakuri duk wacce ta takani ba kyaleta zanyi ba,Hajiya Mero Tace Babu ma Wanda zai shiga gonarki ai su masu kudi basa shiga safgar wani,Iya ta Bude Baki Tace to Kuma kinji wata sabuwa Kuma kice wulakanta mu za ayi,ace baza a Shiga harkar mutum ba ai wulakanci ya tabbata,Hajiya Mero ta kalli Iya Tace gobe Zan tafi idan kinga Zaki je to,Iya Tace Zan gwada idan ba dadi na dawo kauyen mu.
Washe gari Haka Iya tabi kawarta Hajiya Mero Birnin Kano gidan wani sanata zata Yi Aiki a can,Tunda Suka shiga Gidan Iya Tace Ashshahadu'allailahaillahu,Hajiya Mero Kudi Kudi,Billahillazi bani ba Kauye naga wajen Zama,Me gidan ne ya fito Yana takama motoci sun jere zai Shiga ya fita Iya Tace Mero Ina sonsa,Hajiya Mero Tace Iya ki Raba kanki wallahi ko Kallonsa kika Yi sai Hajiya matarsa ta koreki,Iya Tace ita din Banza wallahi sai na gwada sa'a ta,Ta karkashin kasa zanbi Mero,ki fara murna Mero daga yau ki Zama kawar matar Alhaji Sanata,Mero ta Bude baki Tace na Shiga Uku Iya Zaki kawo karshen abinci na a gidan nan,Wallahi sai dai abincinki ya Kare Mero Amma kin kawo Iya matar Sanata ta biyu.
Momy zaune take Tasha wanka ta kalli Safna tace ku shirya kuje ku gano Mana gidan shegiyar kauyen Nan mu gani duk Kaunar da ake Mata me aka zuba Mata,Rabi dake zaune Tace harda Ni za a je Dan Allah na gano lungu da sako,Khaleesat,Safna,Rabi da Farida wacce ta dawo daga Sudan ta gama karatu,Shiri sukayi tare da shiga mota Driver ya ja su,munafuncin Rabi yasa taci gaba a wajen su Mama.
5pm Nasha wata Shadda dinkin manyan Mata na kasar Senegal Dark Brown, Fu'ad cikin kana Nan Kaya marasa nauyi farare ya zuba kyau sai sheki yakeyi har Yanzu Salahu Bai zo ba tunda tun safe Ina Rike Fu'ad Kuma lfy.
A zaune yake yayi zaman manyan yara masu tashen kudi da ji da Kai,A gefensa na zauna ganin Yana Sha min kamshi sai na share shi ban kula shi ba,Kallona yayi ganin ban Masa magana ba duk surutu na sai yace kinyi kyau,na gode na Furta,Kwantar Dani yayi a jikinsa nayi matashi da cinyarsa kaina Yana samanta,Karar Bell Muka ji Kofar a Bude take nace Yes come In,Rabi Tace turawa anyi Boko,Kofar Suka Bude da wani Gadara Suka shigo Sallama sukayi ganin Fu'ad Yana wajen sun San ba Wasa,Yanda nake a kwance nayi matashi da cinyarsa ban ko motsa ba ganin sune nasan wulakanci ya kawo su.
Ku zauna na Furta tare da Mikewa na kawo musu abin sha Dana ci Fu'ad Suka gaisar Ni kuwa Basu gaishe Ni ba Nima ban ce Muka komai ba sai Hararata sukeyi,nace ga ruwa Nan Kainuwa dashen Allah ta kawo musu ku Sha,Khaleesat tayi Tsaki, na sake cewa ya dai kamata kuci Girkin Antynku guda, Fu'ad yace bana son tsokana fa,nace to baka gani har gidana Suka zo suna hararata,Ke wallahi watch your tongue munyi kanwa ta biyu dake cewar Khaleesat,Zanyi magana Fu'ad ya min tsawa ban son hayaniya ke ma biye musu zakiyi kina Babba Zaki zubar da girman na ki ai Aunty Bata fada,Farida Tace ai da ka kyaleta mun zaneta,Tashi sukayi ba Izni ba komai Suka dinga Shiga lungu da sako suna kallo,duk takaici ya kamasu sunga yanda aka kashe min dukiya,Rabi ta fito Tace a dai dinga tunawa da tsohuwa a Kauye,Nayi shuru na kyaleta sabo da Fu'ad ya hanani magana.
Fu’ad ne yace to Ku wuce gida ban son tashin hankali karku jawo naci mutuncinku a banza ku tafi tun Muna mu biyu,Binsu muka yi a baya Ni da shi Zan Rufe kofa Safna ta dungureni sukayi waje,Nace sai na rama Fu’ad ya rike Ni Ina ta wutsil wutsil sai na kwace na Rama Amma Fu’ad ya rike Ni tam,Sai da ya tabbatar sun tafi sannan ya sake Ni,fushi nayi gaba daya na koma Dakina na kwanta,Zuwa yayi ya iskeni nayi kwanciyata Kuma naki kulashi.
Palon Hajiya su Iya Suka Shiga,sun Dade a zaune Iya tana cewa me kudi ya huta kalli gida Dan Allah,Hajiya ce ta fito ta Sha wanka,Hajiya Mero ta gaishe ta Amma Iya tace Hajiya Ina bakuwarki nazo gidanki Ni bazan gaishe ki ba a ka'ida kece Zaki gaishe Ni,Iya Tace Iyye....Ke Mero wace wannan? Hajiya Mero cike da kunya tace sabuwar me Aiki ce, Iya Tace Ki gyara lafazinki Mero ba Yar Aiki ba dai me neman na Halali,Yar Aiki ai Kamar me Bauta kenan,Hajiya tace Kai Mero bazan Iya da wannan ba a kawo wata wannan baza a fada Mata taji ba...kafin ta rufe Baki Iya tace yarki ce Ni ko Haifa ta kika Yi da Zaki fada min naji? Da girma na da yarana kice Zaki juya ni,Yarana kin San Nawa ne?,ke kuwa kwata kwata Baki fi shekara 40 ba,Mero ta dinga dungurar Iya Wai tayi shuru,Iya Tace ke Kyaleni ba shurun da zanyi gaskiya ce dole na fada,Mazajen Dana aura ma Basu juyani ba bare wata ke matar Sanata wacce Nima da Zan dage Nan da wata daya sai dai Kiji na Aure Sanatan naki, Zuciyata Bata mutu ba Hajiya.
Fu'ad ganin Ina fushi sai yace zo muje muyi game,Ina son Tv game da sauri na Mike Ina murna muka koma Bedroom dinsa a kasa Muka zauna da Handle Muna fara game Kawai Sai dai Fu'ad yaga Handle din ya kwala Masa duka a goshinsa,Kuma da hannunsa zai ga ya goce ya koma Goshinsa ya kwalawa Kansa da Kansa a Goshi,yace Salahu ya tashi a bacci karki sake zuwa kusa Dani cewar Fu'ad, Ba shiri ya jefar da Handle,Ina ta dariya Yana Jin haushi na Muka bar game dole,Goshinsa na mulmula Masa Ina bashi Hakuri.
AsmaBaffa
[7/13, 8:42 AM] Sis Asma: ????????????????
DANGIN RABI
????????????????
NA KUDI NE
DAN GIRMAN ALLAH FANS KU RIKE AMANA KARKU FITAR DA NOVEL DIN NAN ZUWA WASU GROUPS KYAUTA,WACCE TA FITAR BAZA MU YAFE BA,A RIKE AMANA DAN ALLAH.
DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.
46-50
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
Frozen Feast kn
Fatin Hana
Ummun Arfat
Nafee
Yar Baiwa
Maryam Muhammad
Zainab Sabo
Abbi ne ya kalle kowa yace ku saurara kuji abin Nan naku ya Ishe Ni yayi yawa musamman Bangaren Mama da Momy duk kunbi kun raba min kan Iyali,Baki idan Suka zo gidan Nan sai an raba kansu to wallahi na gaji Nan gaba Zan yanke mummunan hukunci a kanku,Mama Tace dama ai Haka zaka ce tunda mu ba a kaunar mu Amma Rumaila itace gaba daya ke hada fadan ,ita duk abinda sukeyi ita da Fu'ad ba a gani sai mu sabo da Bamu da yanci a wajenka,Fadila Tace ba abinda sukeyi sai iskanci a gidan Nan,ai fadan da na muku daban yanzu Kuma zancen Rumaila kukeyi ita da Fu'ad cewar Abbi,Ai sune suke abin fada Momy ta furta,Nan take Abbi yace to Na hada Rumaila da Fu'ad aure Nan da wata daya ko biyu za ayi biki kowa ya huta, Fu'ad yace Abbi wata dayan dai mu mun shirya,Islam yace Ni Kuma fa Abbi na samu wata me zafi,Abbi yace Zamu je ayi bincike sai a Kai kudi Inshaallah,nasiha Abbi yayiwa kowa Amma su Momy Basu dauka ba,Rabi Tace Ni ba ayi zance na ba ya kamata Nima a kwato min hakki na anyi magana Kawai Akan Yar gwal Rumaila,Sanda kika koma layin Su Momy har suka kaiki gidan Fadila na sani? Abbi ya tambaya,kin zauna Hassada gashi kinga abarki a kanki,ai itama Rumaila barikinta Kawai takeyi a gidan Nan cewar Fadila,Nima Rumaila nace Kamar yanda mijinki yayi Raping Rabi ba,Nayi niyyar rufa Miki asiri Amma na fasa,tunda Ni kadai kuka sawa Ido a gidan nan.
Abbi Bari na baka labari yanda akayi Raping Rabi,Umma ce ta kyafta min Ido Wai kar na fada,nace Abbi kaga Wai kar na fada Inji Umma,Abbi yayi murmushi yace Fadi Rumaila,Zan sake magana Umma ta harareni,Abbi kaga sai Harara ta takeyi Wai bazan fada ba,Abbi yace Fadi Mana ke Umman Naila ba ruwanki,nace tunda aka Kai Fadila gidan miji Abbi dama ko shimfida basa hadawa,ba irin nasihar da mijinta Bai Mata ba Taki ji,shi Kuma da ba Wani tsoron Allah ne da shi ba sai yayiwa Rabi Fyade,Fadila tana ta rufa Masa asiri shi yasa Tace Rabi karya take yiwa mijinta,Rabi tana Jin Haka Tace Kuma har kallon Yan bariki yake min Yana kashe Ido daya,na karbe zance da cewa ita tana can tana hauma haumarta Bata gane Halayen mijinta ba sai dai tayi wanka ta fice yawo da kawayenta,shi kuma yaga Rabi Yar Dagwai Dagwai shi yasa ya samu ya Girgije da Rabi,Abbi yace to a Ina ke kika ji labari? Nace a gabana Fadila tayi waya ta buya tunaninta ba kowa Ashe Ina wajen,Kuma ta rufawa mijinta asiri Wai Bai aikata ba, Abbi yace to a Nan ba abinda zance ke Fadila idan ma kin boye gaskiya Allah Yana kallonku ke da mijinki Kuma Nan gaba sai kinyi Dana sani,Rabi kuwa Halinki ya kaiki fadawa wannan yanayi Ni dai naja kunen ku nayi muku Nasiha Wanda duk yaki ji ba ruwana,Wannan shine na karshe da Zan muku fada ,Indai akan Rumaila ne kuke wannan tashin hankali to zanyi Mata aure ta bar Nan gidan,Mama Baki ta tabe Tace yafi dai ayi can baza asa Allah ya jarabce mu ba da masifu Ana aikin Yan wuta a gidan Nan,aje a hada jini da Aljani cewar Momy,Allah ya ganar da ku Umma ta furta.
An saka ranar bikinmu Amma Fu'ad baya fara'a bare murna ganin Haka Nima sai na daidai ta sahu na bana nuna Ina son Auren,Bayan Kwana biyu Abbi har kauyen mu yaje ya sanar musu Affa yace shi fa ba ruwansa,Dole duk wani Abu na Al'ada Abbi ne wakili na Yan Uwansa Kuma suke wakiltar Fu'ad, Umma tuni take ta gyarani,Ina dawowa daga makaranta sai gidan gyaran jiki,Haka Umma da Nene Suka shirya har kauyenmu wajen Iya Suka Nema aka ce ai tayi yaji tana gidanta.
Gidan aka rakasu da fara’a ta tarbesu tare da shimfida musu tabarma Bayan sun gaisa,Iya taga kudi sai kallonsu take faman Yi tana zare Ido a ranta tana cewa Ina ma nice wannan Hajiyar,Umma Tace nasan Baki sanmu ba mune wacce Rumaila yarki ke wajenmu,Umma ta hangame Baki Tace Yan Uwan su Rabi ko? Nene Tace ae Haka ne,Iya taga kudi ta manta ma da laifin Rumaila sai Tace Allah sarki Ina kuka bar Rumaila ta? Umma Tace ai Rumaila tana Nan lafiya ta samu Miji ma,Me kudi ta samu? Iya tayi saurin furtawa? Umma Tace Dana ne ai,Tace Ashe Adduar tawa Allah Rumaila ya bawa,Allah me girma duk laifin da Rumaila tayi Masa sai ya Bata kudin Ni Kuma da nake ta Adduar sai ban samu ba,Umma Tace ai ke da Rumaila duk daya ne,karki Yi sabo dai ikon Allah ne,Iya Tace duk dadin Inuwar gemu ai Bata Kai ya makogwaro ba,Umma Tace dama zuwa Mukayi mu fada Miki bikin Rumaila Kuma mu baki labarin cikinta ki yafe Mata,dake masu kudi ne sai Iya Tace Ina jinku,Umma ta Bata labarin komai,Amma sai Iya Tace ban yarda ba Amma sabo da kudin da kuke dashi kun birgeni sabo da kudin na yafe Mata ayi aure lfy Ni dai bada Ni ba,kudin aure da aka Kai Kuma a kawo min Ni uwar ‘ya nice Nasha wahala na haife ta,sabo da tunda na samu cikin Rumaila nake cikin bala’i da cuta,tunda na haife ta sai da ta kwana tana kuka ban runtsa ba ranar da tazo duniya,ga shegen tsotson Nono kwana takeyi tsotson duk abincin da na ci ita ke shanye shi a nono,na rame na kekashe,ta fara hakori tana kashin hakori idan ta feso Kashi tun daga bangon daki sai ya Dire da daya bangon,Ni kenan a wanki da ruwa na zama agwagwar dole,Hakori ya fito idan tana Shan nono ta cijeni yafi a Irga,sannan yanzu zata Yi aure Kuma ace kudin aurenta ma ban gani ba sai dai labari,a kawo min kudi kuje kuyi bikinku lfy.