BABU SO HAUSA NOVEL

DARAJAR ‘YA’YANA PART 2

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Darajar Yayana2-03
Posted by ANaM Dorayi on 04:31 PM, 23-Mar-16
Under: DARAJAR ‘YA’YANA
________________NA ___________HALIMA K/MASHI Ta soma kwalla a kwai su, amma sun zo sun kasa kamo barawon.Ya ce, to daga sun zo ne zasu kamo barawo kamar suna da Allahn musuru?Ina ganin ki hakura kawai in ba a kwai wanda kike zargi ba.Ta ce, cikin jaka ta yake a dakin na, ni na tafigidan kawata, mama ta tana shigowa sai kanena sun ce kuma basu ga wanda ya shigo cikin dakin ba.Aliyu ya tabe baki.Shirme kenan, sai ki hakura kawai.Ta mike tana share hawaye, shi ke nan nagode.Sanan ta tafi.,har ya gama shirin sa tsaf zai tafi sai ga wayar commissioner yana neman sa yana isa aka dan ka wani aiki a hannunsa.Dole ya fasa tafiya ba don ranshi ya so ba.Washe gari ranar goma dai dai dawowar shi ke nan daga wurin motsa jikin da yaso xuwajiya hakan bata samu ba sai yau. Waya ta buga daga bakin gate ne, mai gadi ya ce, yallabai bukur jiya ce ta dawo.Cikin damuwa take oga.Dan sanda ya kara da haka ne don don tunanin cewa in ta fito yau ma zai sami kwaleliyar dubu daya tamkar jiya.Aliyu ya ce ka ce mata zan fita ne ta dawo da yamma, bata jin dadin haka ba amma me nema yana tare da samu, don haka sai ta hakura ta tafi.A ranar ta saka hotonta da ainihin sunanta aaccount din da ta bude kuma Aliyu ya amshia botar ta.Da yammancin ranar bata zo ba domin ta dana sabon shairi, sha biyu zuwa karfe dayan dare ta san lokacin da take ganin shi a online ne, don haka sai ta hau.Cikin sa’a yana nan ta soma da tura masa hotonta a inbox, yana ganin hoton ya gane ta.Ya ce, oh, daman ke ce kika yi mun basaja don in karbeki?Ta ce, naga in ba haka nayi ba ba za ka kulani ba.Kuma ina da matsala kai ne nake ganin zaka magance mun.Aliyu ya ce matsalar me?Ta ce, kafin in fada maka matsalar tawa, ka fara kallon hotunan nan.Aliyu ya ce, to.Duk a tunanin sa matsalar ta ta shafi aikin sa ne.Matsalar farko sassan kirjinta ne, haka ta turo gabobi duk tsiraicinta ba inda ta babu inda ta rage.Ya ce me nene ma’anar hakan?Ta ce, ka duba hotunan da kyau?Ya ce, eh.Dama ina so ne ka gani da kyau don in nayi maka saimatsalar tazo da sauki, domin tun ranar da na ganka na haukace da sonka.Ka taimake ni.Aliyu ya rasa me zaice don ta kaici da bakin ciki, sai kawai yayi blocking din ta amma mehotunan da ta turo sun hau cikin hotunanshi.Ya dinga bin su da dai dai yana sharewa, amma da yazo kan na farkon na kirinta sai ya tsaya yana ci gaba da kallon hoton har ma ya kasa goge shi.Cikin daren tunaninsa ya soma gurbacewa, da safe karfe shida wayar bakin gate ta shigo, bai dauka ba don lokacin bacci yana kanshi.Don baiyi wani bacci ba can kuma a bakin gate din shi kanshi mai gadin yana son wanan bakuwar ta samu shiga sabo da ya san in ta fito zai samu wani abu.Ya ce, madan me yasa jiya da yace ki dawo baki dawo ba?Ta lallaba jakarta ta ciro yan dubu guda biyu, gashi kasa kati.Da sauri ya amsa ya tura a aljihu kamar yana tsoron kada wani ya amshe masa, ko kuma ita ta ce ta fasa.Ya shiga zuba mata godiya, ta ce, tunda jiyaya ce na dawo ban dawo ba me zai hana in shiga kawa yanzu?Dan sandan ya zaro ido oga yana da ka’da sai dai in yayi fada zaki fiar da ni?Tayi masa fari da idanunta, kada ka damu inyayi fadan zan wanke ka.Tun da shiga falon ta ke ta kalle kalle, falon nashi ya birgeta duk da cewa ba wani kayanalatu ya zuba ba.Ta zauna kan kujera ta bude jakarta ta dauko hoda da turare ta sake gyarawa.Sanan ta cire rigar sanyin dake jikinta saura singilrti, ta ajiye mayafinta ta gyara gashin dokin dake kanta.Sanan ta dauki wayarta ta soma kiran wayar ne ya tasheshi, wata isaka yaji tana kadawa tamkar za ayi ruwa.Windo ya nufa ya daga labule kamar yanda ya zata, hadari ne, yaji dadin haka ko don yakara mikewa.Wayar ta sake kacamewa da ruri, yana dubawa yaga number yarinyar, tsaki ya ja tare da yin jifa da wayar kan katifar sa.Ya bude kofar nifinsa yaje kicin ya samu abin tabawa, cak ya tsaya sabo da ganin yarinyar gaban shi ya soma faduwa, lokacin da zuciyar shi ke tuno mashi hoton.Yayi karfin halin daure fuska, sanan ya ce, da izinin wa kika shigo min gida?Ta mike ta nufosahi, da izininka masoyi na, ka manta ka ce in dawo jiya? Ban sami dama ba shine na dawo yau.Ya ce, to fita a gidan nan fita, ya nuna mata hanyar waje.Ta zauna a hannun kujerar dake kusa da ita,da ma ka bari mun fahinci juna.Ya juya ya shiga dakinsa a fusace, durowa yaje ya dauko bindiga nufinsa yayi mata barazana.Ya fito da ita ya saita ta, kwashi kayanki ki fita.Hakika gabanta ya fadi don bindiga ko makerinta yana shakarta.Amma duk da haka sai ta jajirce, ta runtse ido hawaye suka soma zuba,zanfi so ka kasheni feye da ka barni a raye amma baka amshi soyayyata ba.Zanyi alfahari in ka kashe ni da kanka, kuma kacewa jami’an tsaro ni na yafe maka ko sun tsinci gawata a gidanka.Aliyu ya ce, muje ki fita ni bana son jin komai daga bakinki.Sun isa bakin falo Ruwa ya tsuge mai karfi wanda hakan ya sa ya kyale ta.Ya shiga daki ya adana bindigar, sanan ya hau katifar sa ya kwanta. Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com Kokuma ku kasance taredamu a facebook https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gurbataciyar zuciyar sa ta shiga kitsa masa wasu
abubuwa, dauko wayar sa yayi yana kallon
hoton da yarinyar ta turo masa.Cikin jikinsa
sanyi yake ratsawa na ruwan dake
sauka.Mujidat turo kofar dakin ta shigo, kasa
magana yayi lokacin da ya waiwayo yaga ta raba
jikinta da tufafi.Yayi ta maza ya daka mata
tsawa, mai makon ta fita sai ta nufo gurinsa da
gudu ta fada masa.Shedaniyar shu’uma ce
yarinyar, don haka bata samu matsala sosai ba
gurin amincewa da gayyatar da tayi masa, zuwa
ga fadawa tafkin zunubin shedan ya sake
kawata abin ga zuciyar Aliyu.
Har yake ganin haram ta shigeshi fiye da
halalinsa.Mujidat ta amince Aliyu ne irin mijin
da take so ta samu.Duk runtsi ba zata barshi
ba, sai da kanwa takar tsami kwannafi ya
kwanta.Aliyu ya shiga jin cewa bai kyau ta ba.Na
dama ta shigeshi, ya mike cikin bakin rai ya nufi
ban daki zuciyar shi yar bakin ciki tana tunanin
shi cewa, wanan wankan da zaiyi anya zai fidda
mai da dattin zunubin daya kwasa?Ya fito ya
same ta kwance, haushinta ya kamashi sosai.Ya
dauki makulli ya bude durowarshi ya ciro kudi
batare da ya irga ba yan dubu dubu sabbi ya
mika mata.Gashi an gama ruwa ki tashi ki tafi
na rokekikar ki sake dawowa gidan nan.Ta
kalleshi cikin damuwa an ce maka neman kudi
nake yi?Ta mike ta soma saka tufafinta, so da
kauna kurun nake nema a gurinka baka da
kudin da zaka iya bani.Ta fice ta dauki jakarta
yana tsaye a tsakiyar falo yana kallonta ta fita
tare da cewa sai ka sake jina.
Ranar Aliyu yajima bai fita ba, na shi ganin
mutane zasu gane abin da ya aikata, kuma sam
baya son ya tuna.Sai istigifari yake yi, in dai
haka mazinata suke ji lallai zina bala’ice, ya
gargadi masu gadinsa lallai kada su sake barinta
ta shiganmasa gida.
Mahaifiyar mujidat yar asalin wani kauye ne a
Ilorin can jahar kwara, an ce dai asalinsu fulani
ne, amma yarbanci suke yi kuma yarbawa suke
kiran kansu.Musulmine su amma musulincin
nasu sai a hankali.
Mahaifiyar Mujidat mai suna Bukolatayi aure da
Mahaifin Mujidad hakimu bayansun haifi yayan
Mujidat dan suna fari kenan, mai suna
Latif.Wanan al’adar yarbawa ce mace taje aure
amma sai ta haihu za a daura, tasu hikimar wai
a gani in mai haihuwa ce.Bayan Latifa sun sami
Sikirat sanan Mujidat, mahaifin su mujidat
direban taxi ne, mahaifiyar su kuma tana da
shago a bakin kasuwa.Tun tasowar Mujidat bata
ji sam yar karya ce da son bobo, tunda ta lura
tana da kyau ai sai ta mai da kyawun nata
tamkar abin kasuwanci. Tun tana shekara tara
ta soma amsar kudi tana fansar da mutuncin ta,
haka ita mahaifiyart fitina gareta ko yau she
tana biye da mata wanan ya sa ko karatun kirki
bata yi ba, tana secondary idanunta sun gama
budewa, manyan mutane suke daukanta.Da
farko iyayanta sunda mu don mahaifiyarta ta
sha yi mata duka sanan tayimata tsarki da
ruwan barkono, amma da ga baya da ta soma
harka da manyan mutane tana kawo musu kudi
sai suka shiga shi mata albarka.Haka nan basu
damu tayi wata bata zo ba in dai zata yi musu
aike.A zuciyar su tafi yan uwanta Latifa da Sikira
wadda take aure a garin Ilorin.Kuma dalilin
ziyarar da ta kawowa anty sikira ta hadu da
Aliyu.Kuma har ta koma gida so da kaunar Aliyu
yasa ta ta dawo Ilorin don samun muradin ta.Jin
kai da jan aji irin na Aliyu shi ne ya sake burge
ta, amma sai gashi tashin farko ta same shi
cikin sauki.Tabbas in ta nace ba da dadewa ba
zai zo hannunta.Karfe tara na dare ta kira
numbar wayan mai gadin gidan Aliyu wanda ta
amsa dan bukatar kanta.Bayan ya daga ta
tambaye shi ka ganeni?Ya ce, a a ban gane ki
ba.Ta ce, sanana Mujidat daga nan cikin gari ni
ce wace na amshi numbar ka jiya bayan na fito
gurin Oga ya ce, ok madam ce ko?Sorry madam
na gane ki, ta ce oganka ya shigo?Ya ce, eh, tun
bakwai yana gida kuma naga alamar ba zai fito
ba, sai dai yayi mun kashedin cewa ko kinzo
kada in barki.Mujidat tayi shiru tana mamaki,
me zai sa ya tsaneta haka?Duk da ta mika masa
kanta kyauta, amma sai tayi wani
murmushi.Indai kissa tana magani to zatayi
mun, ta ceda me gadi in na baka dubu biyar
yaya zan samu in shiga?Yayi shiru yana
nazari.Lallai yana bukatar kudi don yasha kan
matsalarshi da maman Bilikis, amma dubu biyar
yayi masa kadan.Yace madan zan iya dabara in
kin ban dubu goma, zan fadawa Oga cewa
mamana ba lafiya nasan zai barni in tafi.Don
haka ta ba faruwa amma nasan kafin inbar
wurin sai an kawo wasu lokacin ke zaki samu
shiga dan su basu sanki ba.Kuma kafin in tafi
zan lalata wayar cikin gidan, ta ce hakan yayi
zan sameka da kudin in ka kamla komai ka
kirani.Yana kashe wayar yaga Aliyu tsaye a
bayan shi
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Dfarko ya rude sai kuma ya tuna cewa duk sun
yi maganar ne cikin yarensu na yaroba.Aliyu ya
ce, ina ta kiran waya baka daga ba?Ya ce, oga
jikin mama ne ya tashi shine dan uwa na ya
kirani.Aliyu ya ce, jikin ta ya sake tashi?Wani
ciwo ne ke damun ta?Ya ce hawan jini ne, Aliyu
ya sa hannu ya lalubo dubu biyu ya mika mashi
tare da cewa, Allah ya kara sauki. Ya kara da
cewa kaje ba sai ka jira wasu ba, bari nayi waya
su zo.Da murna mai gadi ya fita ya kira mujidat
yace, tayi sauri kafin wasu masu gadin su
zo.Cikin sa;a ta tura kofa ta shiga, haka nan
cikin sa’a ta riske shi a cikin falo zaune da yar
shirt fara irin mai kama jikin nan.Sai gajeren
wando, kalkon labarun kasa yake yi NTA, turo
kofar ne yasa shi waiwayawa, zunbur ya mike
yana nuna mata waje.Fita la’ananiya, ta saki
jakarta ta nufeshi, haba masoyina, ina sonka
sosai tsaya kaji.Ta kai hannu zata taba shi ya ja
baya.Ki fita kawai, ta zauna kan kujera, ba zan
sake barin gidan nan ba ko zaka kashe ni.Ya
biyota ta zagaya ta fada bedroom dinsa.Ya rasa
me zai yi mata, sai kurum ya kira yaransu daga
headquarter, jin haka dama tariga ta tanaji
dabararta.Taciro wayarta ta danna wani hoto ita
da shine suna tsaka da aikata masha’a ta
dauko.Kalli hoton nan ka gani, ina da irinsu da
yawa har na kati na wanke.Aliyu ya fizgi wayar
ya kalla, duk da ya girgiza amma bai nuna mata
ba ya ce, yace amshi wayarki ba kati ba in kin
gadama in kin tashi ki sa shi a kan profile din ki
na fcbk,ko a jikina.Ke ce mace mutuncinki sai
yafi nawa zubewa.Tayi shiru ta rasa me zata ce,
ya ce fita.Ta daga hannuwa biyu, naji naji zan
fita, ta matso gunsa amma ya kamata a ce
kanayiwa mesonka kallon mutunci da kima.Ta
soma kuka, ka tuna ba nice na dorawa kaina
sonka ba, ya kamata ko baka sona saika fada
min magana mai sanyi.Ya runtsa idanu, burinsa
ta fita domin zuciyarshi ta soma
tausayinta.Sanan ga shi dan can gefe yana rada
masa wani abu.Ya bude ida nunshi, shi ke nan
naji ban kyauta ba amma dai yanzu ki fita
kawai, domin ni da ke ba hurumai bane.Ki tuna
da abin da ya faru ni dake she karanjiya laifi ne
babba, kin sani.Ta matso ta kama hannuwansa
ka min afuwa sonka ne ya sani haka.Yanzu ina
jin yunwa ko zaka tai maka min da wani abu in
ci sai in tafi?Ya ce, duba kicin sai dai in bread za
ki ci.A kicin tayi ta zagayawa tana tunanin me
zatayi ne don ta samu ta kwana a gidan.Ta
dauki wuka ta dauko bread wai za ta yanka,
amma sai ta kulle ido ta sharbi yatsanta da
gangan, sanan ta saki kara.Cikin hanzari ya nufi
kicin da ganin yanda jinike zuba ya sa shi shiga
da sauri ya rike ya tsan nata.Kasancewar yana
da yar akwatinshi ta taimakon sai ya gyara mata
ya rufe shi sanan ya ce, muje a maki Allura sai
ki wuce inda kike.Ta soma rawan sanyi wai ba
zata iya tashi ba, barinta da yayi ta dan
warware shi ne ya kawo kwananta a
gidan.Domin tuni shedan ya ribace shi, duk da
yana zargin ta yanka kanta ne dama don kada
ta tafi, tun daga ranar ta zama gidan tamkar
matarsa, wanan ne yasa ko da ya koma gida
sadiya taga canji.
Wata hudu kenan da soma shiga matsalar mu
da ya Aliyu, amma tamkar na shekara biyu, duk
na rame na lalace har bana so inyi baki don
kada suce lafiya?Cikin wata hudu ya zo so hudu
duk karshen wata ke nan kwana dai dai yake yi
ya tafi sam baya kulani in yazo magana fiska a
daure yake min.Ya manta da wani hakki nawa
da yake kanshi, domin nima mutun ce ba ice
ba, ina shan wahala da kewarsa.Darare da yawa
ina zubar da hawaye don kunci da kewa, gashi
yayi mun sabo da yanayin sa na rashin
hakuri.Usman da Anty Abida sune kawai suka
san halin da nake ciki, ko iya da amininiyata
Aisha sunyi juyin duniya amma ban shaidar
musu da ko mai ba.Usman ya ce, duk lokacin
da nake bukatar wani abu bai min ba in
tambaye shi, ni gaskiya ina da jin nauyi.Yau in
na ce gashi gobe in ce gashi ba zai yuwu ba,
abin da kawai na tsana shi ne inga arana babu
makaranta, amma don abin anfani kamar su
abinci ina maneji.Tunanin kama sana’a ya
shigeni, na ce lallai ina bukatar in kama sana’a
don in samu in kare DARAJAR YAYA NA,
wadanda a yanzu sunfahimci tsakanina da
baban su a kwai matsala.Ba kausar ba hatta
Al’amin ya san cewa mahaifinsu ya canza, don
watarana da ya shigo daki ya same ni ina kuka,
sam banji shigowarsa ba sai naji an dafa ni.Nayi
ta maza na share hawaye na na kalle shi da
murmushi, ranshi a dagule ya ce, momy waye
ya saki kuka?Na ce Idona ke ciwo.Ya ce, mama
Abban mu ne ko?Na ce, a a Abbanku bayanan?
Yace, shi ne mana, ya ce ki barshi in na girma
zan maki duk abin da kike so, in kaiki maka, in
sai maki komai.Na rungume shi tare da cewa, to
yarona naji dadi na gode kaji.Ya ce momy ki
daina kuka kin ji?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan fitar Al’amin ne na shiga sabon tunani,
lallai matsala tsakanin miji da mata tana kawo
rabuwar kan yaya, tana tauye yara.Domin zuwa
da nayi open day din su a makaranta nan
malamarsu take yi mun korafin cewa yarinyata
Kausar sam yanzu bata da hazaka kamar
da.Bata da kuzari sam, ta ce kowa ya san
Kausar Aliyu Tutur a makarantar nan ya san ta
da kokari ga surutu, ga wayo.Haka nan duk
wanda ya yi mata bata kyalewa, amma daga
wancen term zuwa wanan tazama tamkar
doluwa ba karatu.Bata iya rama fada, karamin
yaro sai ya doke ta ta tsaya kuka, sanan tsaftar
su ta ragu, a da yaran suke zuwa na daya a
tsafta wanan karon sun koma na biyu.Don haka
kiyi kokari ki canja kila matsalar daga wajenki
ne.Afili na ce, lallai daga gurin mu ne,
matsalarmu zata maida yaranmu baya, dole in
kawo canji duk yanda zanyi gidan mu ya koma
gidan farin ciki kamar da da taimakon
Allah,Wayata na dauko na soma ruga sako
kamarhaka.KALMOMI SUN YI KARANCI
TSAKAKKEN YANAYI, FADIN YI HAKURI KADAI BA
ZAI GAMSAR BA.AMMA DUK DA HAKA INA ME
BAKA HAKURI, BA DAN NAYI LAIFI BA, SAI DAI
INA DARAJA DANGATARMU FIYE DA
SHEKARUNA.DA WANAN SAKO NAKE SAKE BAKA
HAKURI TARE DA AIKO MAKA DA ZUCIYATA KA
AMINCE DASHI DON SAKE DAWO MIN DA
FARINCIKI NA.INA FATAN ZA MU KOMA FIYE DA
DA, ZUMA TA ALY NAYI KEWARKA, INA TSNANIN
SONKA.
Na tura mashi ina tsammanin ganin sako kokira
amma shiru, duk wani tunani ko dabara nayi
amma babu nasara.Wata laraba da yamma su
kausar an koro su kudin islamiya, gashi dama
abincinmu ya kare, nafita hannuna da Nera Dari
na siyo garin rogo da suga.Nufina su sha da
dare, duk da ina tunanin yaya zan sha kansu su
sha gari da dare, sai lokacin da nake dawo wa
yana ba yana a mota direbanshi yana janye da
shi.
na shigo gidan zan Rufe sai naga mutum kamar
daga sama ya nufo gida, gaba na yayi muguwar
faduwa.Sam yanzu bana son ganin shi, don
tsananin tsoron sa nike ji, ko sallama baiyi ba ya
fara da ce mun, daga ina kike?Cikin in ina na ce
sha….shago baje can gurin hadi.Yin me?Na ce,
gari na suwo da suga.Gari?Ya tam baya tare da
zaro ida nu.Na sa dan yatsa na akan le buna na
tare da fadin yi hakuri yara suna ciki.Sai me? Ya
katse ni, na ce sai me in yara suna ciki, wato
sabon salon zubar da mutunci wanan kika samo
ko?Kamar ni a ce matata tana zuwa shago siyan
gari?Na nufi ciki raina a dagule, in ya bamu
abinda zamuci ishashshe ai ba zan fita siyan gari
ba, na raya hakan cikin raina.Kai tsaye daki na
shige na ajiye garin na fada ban daki don gudun
kada yara suji, da gudu suka rungumeshi suna
mashi oyoyo, al’amin da shi da mama, Kausar
tsayawa tayi tana kallon su.Ya dube ta ke
Kausar ba zakiyi min oyoyo ba? Ta ce sannu da
zuwa Abba.Ta juya ta nufi dakin su.Da kallo ya
bita cikin mamaki, me hakan yake nufi?Ta soma
yiwa yaran sa fanfo ne?Ya mike ya nufi dakin ni
kuma jin shiru sai na fito ina shigowa falo najiyo
muryar sa.Kausar ina tambayarki kin yi mun
shiru na ce me nene kike fushi?Sai na jiyo
muryarta tana cewa, Abba ni bana so ka dawo,
sabo da in kana nan kullum cikin fada da momy,
ni bana son tana kuka.Itama ta soma kuka, na
zaro ido cikin mamaki yarinyar,na saurara inji
me zai ce, fatana Allah yasa zancen Kausar
yazama sanadin fahimtar shi.Muryarshi ne ta
katse ni, ok wato uwarku tana kitsa muku
magana a kaina ko? Mamanku ta shirya muku in
nazo ina cutarku ko?Ya sake tambayarta cikin
daga murya, ban san lokacin da na fada dakin
ba ina fadin haba yaya.Yanzu me ya kawo
wanan tunanin?Tayaya za kayi mun wanan
zaton?Na kalli kausar fita.Ta fita na maida kofar
na rufe yana tsaye rai bace yana kallo na.Nayi
kasa da murya tare da tausasa ta, yaya wanan
sauyin da kakawo mana cikin gidan nan wlh ba
sai na kintsawa Kausar ko mai ba.Tana ji tana
gani, duk kokarin da nayi dan cewa basu
fahimta ba amma hakan bai samu ba.Saboda ka
kasa gyarawa, har takai ko a makaranta yaran
sun koma baya.Hawaye suka soma zubo min
masu zafi, na taka na isa inda yake tsaye nafada
jikinshi na kan kame shi.Yaya ka taimaka kayi
hakuri ka zubar da makamanka ka dawo mana
da farincikin mu.Ya ban bareni tare da hankade
ni har sai da na fadi, ya soma magana cikin
ihu.Tayaya kike so in yarda dake cewa bake
bace kike bata ni a wrin yarana ba?Yar wanan
yarinyar da bata gama sanin kanta ba shine har
zata san matsalar wani? To ni dake dasu munsa
hannu tunda kin zabi haka.Shiyasa sam bana
son zuwa garin nan, saboda takaicinki, kin zama
saikace sanda don Rama.
Kullun mahaifiyata tana tuhumata cewa bana
kula da ku, yanzu dan zubar da mutunci wai
kinje shago siyan gari.Na fashe da kuka yaya
yaushe rabon ka ajiye mana abinci?Tun zuwan
da ka tawo da wanan matsalar.Ya daga hannu
rufe min baki, yanzu ina yi maki magana ne a
kan shiga tsakanina da yarana.In zandau komai
ba zan dau wanan ba, ya kamata ki sani.Ya juya
ya fita bayan ya bude kofa.Kuka sosai nayi na
tsawon minti daya, sanan zumbur na mike na
fita.Mama tana kwance a tsakar falo tana ta
tsotsan yatsanta, ita bata san me ke
faruwaba.Ahmad yana zaune kan kujera ya
takure, Kausar na shiga raba ido in gani, can na
hangota gefen kujera ta makure tare da toshe
kunnuwanta, tana nufin bata son jin abinda ake
yi, ga kuka tana yi.Tayi sharkaf da majina,
dakinsa ya shige shikam naje na rumgumo
Kausar nazo na hadasu da Al’amin ina
lallashinsu.Duk da cewa nima hawaye ke
kwaranya a idanuwa na, Al’amin yazo yayi mun
rada a kunne, ki hada shi da Iya kinji Momy ta
rama maki(don duk zatonsu ni iya ta haifa ba
baban su ba) Najasu muka koma dakinsu, na
ce, Kausar Al’amin kuyi hakuri ni da Babanku za
mu koma kamar da, ba da jimawa ba kunji ko?
Kausar ta dago kai, yaushe momy?Na runtsi ido
hawaye na kwaranya na ce, bada jimawa ba
Kausar kinji?Duk suka makaleni, Al’amin yasake
cewa kin hada shi da Iya ne, da sauri na ce a a
ko ku kada ku fada mata, ba na ce muku bata
da lafiya ba?Kuna so in taji da muwa ciwonta ya
tashi?Duk sukayi shiru, nace kuna so ta mutu?
Da sauri suka ce, a’a,na ce to in kun fada mata
zata mutu.Kausar ta ce, bazamu fada ba.Na
share hawayena sanan na kallesu.Muna ciki har
aka kira magariba, na taso su mukayi salla.Tinda
na fito banga Mama ba, nasan tana gurinshi,
suna ciki ko sunfita oho.Na jika musu gari suka
zauna, Allah ya taimakeni suka kama sha.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kausar tana cewa,Momy in nazama babba zan
dinga siyo mana kayan abinci.Al’amin ya ce,
momy ba na rigata ba.Yaya kausar nine
zandinga siyan ma Momy ko mai, na ce to tun
yanzu nagode, Allah ya raya ku, ku girma cikin
aminci da Albarka, suka ce amin.Raina yayi
sanyi yar firar nan da muka yi da ya rana sai
gashi sunyi sallama shi da mama tsam ya tsaya,
ganin suna cin gari.Na lumshe ido na hadiye
takaici na, sannan na ce sannu da zuwa.Bai
amsa ba yayi ciki, kamar in zauna sai kuma na
bishi.Ya aje mama ya zauna bakin gado tare da
dafe kai, na ce, ina maka sannu.Ya dubeni
idanu jajur.Yaya na ke cin gari da dare?Na ce,
to yaya bamu da komai ne.Na dubi mama,
zomuje ki ci gari.Ya daka min tsawa, ki daina
kira min sunan garin nan, ba zataciba.Ko
Inyamuri ya sha gari da daddare? Wanan shine
na karshe in ba haka ba rai zai baci, ban ce kala
ba na juya, cirko cirko nagasu Kausar a
falo.Kausar ta toshe kunne, Al’amin na tsaye
cikin damuwa,nakamasu muka koma na ce su ci
garin amma sai suka ce sun koshi.Kausar ta
kwanto kan cinyata, Al’amin ya kwanta kan
kujera na kwantar da kaina nima a hannun
kujera.Wai ta wace hanya zanbi gidana ya dawo
kamar da?Wa zai ban shawara dan ni ina ganin
tawa basirar ta kare kan haka.Allah ka bani
mafita.Muna nan har aka kira isha’i, na tashi
naje nayi sallah suma sukayi sai ga mama ta
shigo da nama da Holandia, na ce, suci.Al’amin
dai ya ci amma Kausar kin ci tayi waita ta koshi,
na rungumo ta, Kausar kina fishida Abbanki ne?
Tayi shiru, na ce ki fada min.Ta ce, eh momy
shima yanzu ya daina sonmu nace, a a yana
sonmu fushi yake yi in ya huce zai dawo kamar
da.Sai kurum naji ta ce, wane ne yayi masa
laifimomy?Na ce, ni ce, ta ce, bakiyi mashi ko
mai ba, ba ma kullun kina bashi hakuri ba
tunda yaki yayi hakuri ya daina sonmu.Bani da
bakin magana sai shiru ina mamakin Kausar,
yar wanan yarinyar har tana fahimtar abubuwa
kai abin da mamaki sosai.Haka na lallaba su har
sukayi bacci na kulle mana kofa sanan nima na
kwanta na fada kogin tunani.
Wa she gari da wuri na tashi nayi salla da
wanka, sanan nayi musu shirin makaranta, duk
a dakinsu.Nace suje su gaida baban su.Kausar
ta noke tare da daure fuska za ta soma kuka,
na ce, haba Kausar, kuje ku gaida Babanku
mana.Kina so ne ya j haushi irin jiya?Jiya ma kin
ki sakar mashi fuska ne shi yasayayi fada.Ta ce,
to momy yanzu tsoronshi nake ji.Na ce, daina jin
tsoro kinji Kausar, yana sonku.Daga nan ki bashi
hakuri.Ta ce, to.Amma sam fuskarta ba wani
annuri, ina biyeda su har kofar, Al’amin ya
kwankwasa daga ciki yaya ya ce, wanene?Mama
da jin muryarshi sai ta ce, Abba.Ya ce mama.Na
bude kofar suka shiga, yana kwance kan gado
da waya a hannunsa, da Alamu cht ya ke
yi.Kausar ta dan tsaya nesa dasu kanta a
kasa.Al’amin ya zauna bakin gado,Mama ta
hayekan gado, ya rungume mama da Al’amin
sanan ya tashi zaune.Al’amin ya gaida shi,
Mama ma cikin hausarta mara dadi ta gaida
shi.Ya kalli kausar daga inda take.Zo nan.Ta tafi,
ya janyota zuwa jikinshi, ta ce ina kwana?Ya ce,
ba zan amsa ba Kausar har sai kin fada mun
me mamanku ta ce maku nayi, kuke jin haushi
na?Kausar ta ce ba ko mai Abba, Al’amin ya ce
ta ce ne fa muzo mu gaida kai.Ya kalli Kausar,
yanzu kunfi son mamanku fiye dani ko?Al’amin
ya ce, muma ka daina son mu Abba.Ya ce, ok,
haka mamanku ta fada muku?Kausar tayi saurin
cewa momy bata fada mana haka ba, ta ce ne
kawai muje mu gaida ka.Ya dungurewa Kausar
kai yar karama da ke kin iya munafunci, ba zan
kara yi maki tsaraba ba.Ya kalli Al’amin, in ba
ka daukar maganar mamanku zan sai maka
keke kana so?Al’amin ya kama murna ina so
Abba.Ya kalli mama, mama na ke kuma in se
maki motar ki ta wasa ko?Na juya kicin ina kuka,
mutumin nan zai raba mun kan yara, zai kafa
min jam’iya yan partyn shi da nawa.Jin takun
Kausar yasani share hawaye, cikin sheshekar
kuka ta ce, momy kinji Abba zai sayawa su
Al’amin da mama tsaraba ban dani.Na tsugunna
na rungumota jikina ina shafa mata kai, yi
hakuri Abbanku wasa yake yi miki zai siyo miki
kinji?Ta ce, Allah momy da gaske yake yi ba ya
cein fitar masa daga daki ba?Na ce, yi shiru zai
sai maki.Da kyar tayi shiru.Na bata jug na ce,
kije wajen Iya ki ce mata in ta dama koko ta
baku, karfa ki ce mata wani abu ya faru kinji?Ta
ce to.Ta tafi nikuma na zauna a kicin cikin ta
gumi.Kausar ta sami Iya kwance ta gaida ta, ta
ce kausar menene?Ta ce, wai in kin dama koko
ki bamu, iya ta ce shine aka turoki ba Abbanku
ya dawo jiyaba?Me yasa bai rakoki ba?Tayi shiru
Iya ta ce to muje in se maki koko gidan ladi me
koko dan kulluna jiya ya kare, kice mata na ce a
jika maku gero tunda jifa jifa kuna shan kokon,
ban cika son abin siya ba.Sam iya bata fahimci
bamu da komai a gidan bane, tunda lokaci zuwa
lokaci sukanje su amshi kokon.Ta samu masu
kosai sanan ta rakata har kusa da gida.Tanaji
tana fadan turota ita kadai a wanan safiyar, ta
ce da uwarku tana tattalinku amma yanzu duk
ta canza,na rasa me ke damunta.Suna shan
koko da kosai kausar tana fada min sakon Iya,
na jika gero na ce to za a jika,suka gama na
dauki Mama na nufi kaisu makaranta, kusan
wata guda a kafa nake kaisu makaranta, don
mota tuni nayi fakin dinta gefe na rufe ta don
ba mai ba na da kuma kudin siya.Ina dawowa
na tarar da shi da Usman zaune yana
karantowa Usman laifuka na.Na gaida Usman na
shige daki, na hau gado na kwantawa,bawai don
bacci ba ko don hutu, sai don tsabar ta kaici.Can
na jiyo muryarshi yana kira na, ya kalle ni.Kin
san na fada maki ba zan dauka ba ki rabani da
yara na ba.Jiya na shigo gidan nan wai Kausar
tana yin fushi dani yar karamar yarinyar
nan.Al’amin yana fada mun na daina son su,
tayaya zan yarda wanan tunaninsu ne?Usman
ya daga mishi hannu saurara aboki na, ka barni
in gama magana ta don kada kakatse ni.Usman
ya kalleni,Sadiya me yake faruwa ne?Na runtse
ido don ta kaici, yaya Usman duk abin da ya
faru Abban kausar shine sila.Na koro mishi
komai tun daga farkon rigimar har zuwa
yau.Sanan na ce yaya Usman tsakani da Allah
kullun yaran nan suna kallon muna fada, ko
ince daga yazo sai shiga tashin hankali zasutashi
da tarbiya me kyau?Ya ce, a a.Na fada musu
yanda mukayi da malamansu. Ga rashin abinci
wane laifi na masa, ni dai yanxu tunda gani
gashi kurun ya fada min laifi na, wlh zan bashi
hakuri mu koma kamar da yaran mu suma su
sami natsuwa.Usman ya kalli Aliyu, aboki kaji,
sai ka fada mata laifinta don matsalar tazo
karshe.Aliyu yayi mun wani kallo ke dai kawai
baki son zaman lafiya ne, duk ki dauki damuwa
da bakin ciki kisawa kanki.Sau nawa zan fada
maki baki yi mun komai ba?Usman ya ce, to na
rokeka aboki ko mai ya wuce.Ya runtse ido tare
da fadin shi ke nan.Na dube shi nima in sha
Allahu ko mai ya wuce.Usman ya ce,
Alhamdulilla, yanzu sai ka tashi mushiga kasuwa
don nima abincin gida na ya kare.Nan dai suka
fita.A cikin mota Usman ya kalli Aliyu.Aboki ka
canza fa,Aliyu ya kalleshi wacce irin canzawa
nayi?Usman yayi murmushi sanan ya maida
hankalinshi titi.Kayi kiba sanan dabi’un ka sun
canza.Aliyu ya kure Usman da ido, zaiyi magana
kenan wayarsa ta soma ruri, ya ciro ya kurawa
Screen din ido,sha wara yake ya dauka ko ya
yanke,Usman ya kalle shi, daga mana abokina,
Aliyu ya katse kiran sanan ya kalli Usman,daga
jin kira sai kace in daga ba tare da kasan me
kiran ba?Usman ya ce, jami’in tsaro zai ji
shakkar daga kiran koma wanene…….Kiran
yasake shigowa, sai kurun Aliyu ya dagadan
kada Usman ya dago abinda ke faruwa.Ya ce,
yaya?Mujidat ta ce, muryarka nake sonji, nayi
kewarka da yawa, don Allah ka dawo yau.Tana
magana kamar zata yi kuka, salon dake narkar
masa da zuciya,take ya manta da wa yake tare
har ya furta cewa.Kada ki damu gobe kamar
yanzu muna tare,ta ce, to Zaki na sai mun hadu
a internet.Sai da ya salameta sanan ya tuna
yayi baram barama.Ya dubi Usman wanda bai
ce kala ba, ya soma nade tabarmar kunya.Wata
abokiyar aikina ce, muna gabatar da wani
aikine.Usman yayi murmushi sanan ya ce, sau
da dama in mutun ya shiga aikata rashin
gaskiya sai kaga ya zama makaryaci.Ita ko karya
illar ta da kayi so daya kafin ka fitar da kanka
sai kayi kusan sau goma.Aliyu ya kalle shi, me
ya kawo wanan zancen?Usman yayi dariya, ka
tsargu ne?Aliyu ya kalli gefe, intsargu da me
kuma?Usman ya hade rai, tsayar da halayenka
haka nan Aliyu.Ya gangara gefe titi yayi fakin
dazu nake ce maka dabi’unka sun canza ko?
Aliyu ya kalli titi muje zuwa da maganarka, in
wani zai fada mun aboki ba zan yarda ba,
amma gani ina zar ginka cewa kana hulda da
matan?Aliyu ya kalleshi da sauri, haba aboki,
nasancewa zaka iya bada shaida cewa ban
kasance mai shiga lamarin da mata suke ciki ba,
bare har inyi hulda dasu.Usman ya ce to amsa
min wadan nan tambayoyin.Aliyu ya cire hankici,
ya share zufar fuskarsa sanan ya ce, ina
jinka.Usman ya ce, na kira layinka sau uku wata
macece take dagawa.Na farko da dare ne gurin
karfe dayan dare, don in fada maka rasuwar
kanwata, sai kawai wata mace ta daga wai ka
shiga wanka.Na biyu da safe wata jumma’a don
mu gaisa ta ce ka fita gurin masu gadi, na uku
gargadi tayi mun in san lokacin da zan
dingakiranka yanzu kana cikin halin da bazaka
iya daga waya ba.Sai na soma lissafi giya kake
sha da har ba zaka iya daga waya ba, koko
menene?Sanan ita wanan matar yakuke da ita
har zata kasance a inda kake ciki tsakar daren
nan .In zuciyata ta zargeka sai wata ta shaideka
da cewa ba aikin ka bane, abin da bakayi ba
kana yaro ba na zaton cewa zakayi shi da
girmanka.Amma yau da matarka take fadin
yanda ka kaurace mata, sai na amince kana
neman mata, don kai ba me hakurin zama baka
tare da mata bane.Aliyu ya hade rai tare da
duban Usman, me cece shaidar ka ta zahiri?Duk
abin da kafada bai zama shaidar da zaka
amince ina bin mata ba.Ba zan iya zama ba
mace ba, shekaru nawana dauka can baya babu
auren?Usman ya ce kila lokacin baka san
amfanin matan ba,amma ni shawara daya zan
baka, inma zakayi harkar bariki to bai kamata ka
wulakanta matarka ta sunna ba.Aliyu ya ce, dan
Allah mu rufe wanan firar.Usman ya ce kafin
mu rufe sai nayi maka nasiha duk da cewa bani
da tabbas akan zargin da nake yi maka.Na san
mutun yana canzawa kamar yanda wahainiya
take canzawa zuwa duk kalan dataso.Nasihata
gareka in ka canza daga fari zuwa baki don
Allah ka saki wanan layin ka koma dai dai ko
don gudun zunubi, ko don tsoron azabar
Allah.Ko don kare mutuncin yayan mu, ko don
kare lafiyar ka daga cututukan zamani.Sanan
maganar zubewar daraja da kimarka a idon
wayanda suka san kanayi. Aliyu ya runtse ido
cikin in ina yace, muje aboki don Allah.Suna tafe
yana share zufa, lallai zancen Usman ya shige
shi.
Ko mai na abinci zuwa kayan tea sun hada
muna, lokacin da suka dawo ina kwance
kangado ina karanta littafin gidan zahra.Sau da
yawa in ina karanta littatafan Hausa sukan debe
min kewa halin da nake ciki, har na sha cin karo
da irin matsala ta.Sun ajiye min kayan abinci
suka sake ficewa, na fada kichin na shiga girki,
yarama da suka dawo makaranta sai murna
suke sun sami lafiyayen abinci.Yaushe rabon
muyi girki da kifi ko nama, yau gashi har
farfesun kan rago mukayi.Da daddare na fada
ban daki na sake wankana sheka kwalliya duk
tunanina yau za a shalabari.Sai dai muka
kwanciya ya juyya min baya, na gaji hakurina ya
kare don haka na ajiye kunyata na fada masa
cewa, yau ni ina son a faranta min.Ya ce, shi
gaskiya baya jin zai iya wani abu yanzu don duk
a gajiye yake.Nace, haba yaya, nima fa mutunce
kamar kowa, sama da wata hudu ka juya min
baya.Baka tsoron sharrin shaidan?Ya tashi
zaune a fusace, kina nufin zaki bi maza? Iye?
Fadamin zaki bi maza? Nasauka daga kan gadon,
ban ce zanyi zinaba yay, amma zuciya bata da
kashi, in na kasa jurewa fa?Na durkusa kan
gwiwowina, yaya ka taimake ni ka fiddani wanan
yanayin, ka tuna ni ban taba gudunka ba.Ya
mike ya dauki filo.Sai da ya kai bakin kofa
sanan ya ce, ina ganin kina cikin fitunananun
mata bari naje falo in kwana. Rufda ciki na
kwanta a kan gado ina kuka, wani mai kunci
daga bisani na dangana na fada ban daki na
sakarwa kaina ruwan sanyi yayi ta zuba tundaga
tsakiyar kaina.Ban fito ba sai da naji sanyi yana
ratsani, na fita naje kan gado na dukunkune sai
zazzabi da ciwon kai.Haka na kwana har safe da
kyar nayi Sallah na sha magani, sanan na fita
kicin.Shi kam a ranar ya koma kusan karfe biyu
ina kwance ya tsaya kaina wai ni fa zan tafi.Ba
tare da na dago ba, na ce Allah ya tsare, ya
ajiye kudi a gefe na tare da fadin, motarki an
gyara na ce uhm.
Duk da cewa Aliyu yana kirana a waya mu gaisa
yanzu duk abinda muke bukata yana
kamantawa, sai dai ya barni cikin kewa.Haka
nan ko a waya da mun gaisa shi ke nan sai ya
ce in bashi yaranshi suyi magana,ba wata hirar
soyaya ko ta rayuwa bare in sa rai zamu koma
kamar da.Duk da cewa yanzu yaran nan sun
dan saki jikinsu sai dai duk da haka da sun
ganni cikin takura ko damuwa yanzu zakaga
sunyi mun narai narai tamkar zasuyi kuka.Ni dai
a bisa halin da nake ciki gara ace bukatun ya
dai na yi mun ya bani kulawa da soyayya sunfi
mun duk wani abin duniya da zai sai min.Na
hakura ne saboda DARAJAR YAYA NA, sam bana
so in zube su inyi gaba.In ban rike suba naje
can inyi wahalar yayan wasu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana naje kitso inda nake zuwa a can layin
zage-zagi wani gida, gidan haya ne maidauke da
matan aure da dama.A kulun naje gidan ina
karantar abubuwa na rayuwa da dama a gurin
matan gidan.Farko matar dake yi mun kitso, sau
da yawa mijinta in yadawo bata iy sakin kitson
taje gurinsa.Haka zai gaji da zama ya fito ya
dauki bokiti ya ja ruwa yaje yayi wanka.In kuma
da abinci ya ci ya fito in ya ciro kudin cefane ya
bata sai ta amsa a raine, yauma da nazo kitson
hakan ne ta kasance.Ya bata dari biyu ta juyata
sanan ta maida masa tana fadin gaskiya malam
bazata isa ba.Ya ce ba da garin tuwo ba, kuma
naga manja?Ta ce yau kwana uku muna tuwo,
ta kalli yaranta dake gefe suna wasa.Habu kunji
babanku wai yau ma tuwo sai suka rugo da
kansu gaskiya baba yau bazamuci tuwo ba.Ya ce
to me ni dai kudin nan ke nan.Ta ce, ko tuwon
ne ma kudin nan ba isar muzaiyiba, ya ce haba
Tasallah, ba kifi ba nama kice dari biyu baza tayi
miya ba?Ya shura takalminsa yayi gaba.Ta daga
murya sai dai ayi maka ciko kuma kana zuwa
zaka bani kudi na.Yaran suka hau mita, shi
baban nan kullun tuwo.Na kalleta cikin mamaki
sanan na ce, na kusan daina zuwa kitso gurinki,
ta ce zaku tashi ne?Na ce a a na ce nagaji da
yanda kike daukar mijinki ba a bakin ko mai
ba.Dubi yanda kike sa yaranki suna yi ma
mahaifinsu rashin da’a da raini, wanan tarbiya
ke nan?Tayi yar dariya hajiya kenan, Allah hajiya
ba haka bane, ace mutun kullun ba ci gaba, ba
ya neman wata sana’a a caba yake.Na ce, na
lura baki da godiyar Allah ta salla. Ranan fa ina
kallonki da yaranki kuka ce masa kun gaji da
shinkafa, san nan baki sanin mijinki ya dawo ki
bishi daki ba…..
Allah sarki Rayuwar Aure,kowadai da tasa
matsalar,damadai haka Rayuwar take,tanada
manyan matsaloli guda hudu wadanda duka
daya takan haddasa rashin jin dadi daga
bangare daya,Immadai -:
Mijin baya jin dadin zama da matar,misalin
Tasalla me kitso da Mijinta,kokuma…
2:Matar ake zalunta ,Misalin Aliyu da
Sadiya,Kokuma …
3:Suna zaune lafiya a junansu, Amma dangin
matar ba kaunar mijin,shima Wannan Babbar
matsalace a auratayya,Wacce ke Haifar da Babar
Matsal..kokuma…
4 angin mijine basu son Matar, wanda nasan
da yawanku kunfi sanin wanna matsalar,..
Lallai dukanin gidan auren da suka samu kubuta
daga dukkanin matsalolinnan nazama wajibi Su
godewa Allah,akarshe Dukkani gidan Auren dake
da matsalar makamanciyar wadannan Ya Allah
ka kawo musu agaji,mukuma Ya Allah
kahadamu da abokan zama nagari
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Previous page 1 2 3 4 5Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button