Al-Ajab

Asirin Wani Malamin Makaranta Wanda Sha’awarsa Ke Tashi Duk Lokacin Da Yaji Muryar Dalibarsa Ya Tonu

Wata daliba a Najeriya ta bayyana irin halin da dalibai mata ke shiga na fuskantar cin zarafi na lalata daga malamansu da nufin ba su damar cin jarrabawa ko wani ci-gaba a karatunsu.

 

Dalibar ta bayyana wa BBC irin yadda wani malaminta a jami’a ta ce ya ci zarafinta da neman ya yi lalata da ita da alkawarin taimaka mata a karatunta, inda ta ce ya bayyana mata cewa muryarta tana tayar masa da sha’awa;

 

‘’Ni wannan abin ya faru da ni farko a University inda wani malamina ya yi harassing dina by saying that irin voice dina was sexy, yana tayar masa da sha’awa kuma yana so na taimake shi na kashe mai kishirwarnan, shi ma zai taimake ni ta hanyar sawa na ci dukkanin courses dina a makaranta.’’

 

Dalibar wadda ba a bayyana sunanta ba da kuma inda take domin kare sirri da mutuncinta ta gaya wa BBC cewa, wannan ta’ada ta yadda malamai ke neman dalibai tana faruwa kusan a dukkanin matakai na manyan makaruntun gaba da sakandire a Najeriya, ba wai sai jami’a ba.

 

Ta ce saboda ko ita ma sheda ce domin ya faru da ita a matakai uku na manyan makarantun gaba da sakandire, kama ‘’daga university, college of health, federal college da kuma Polytechnics, saboda haka mutum ba zai iya cewa takamaimai ga inda abin ke faruwa ba yana faruwa kusan a ko’ina’’ in ji ta.

 

Matashiyar ta ce dalibai mata na fuskantar wannan matsala wasu ma ba su san yadda za su yi ba domin suna samun kansu a yanayi na cutar damuwa saboda ba wanda zai taimake su.

 

Ta kara da cewa wasu matan sun rasa budurcinsu wasu sun rasa mutuncinsu da kimarsu a matsayinsu na ‘ya’ya mata duk ta dalilin wannan ta’ada da malaman makaranta ke neman dalibansu.

 

Dalibar ta kuma kara da cewa abin yana faruwa ba sau daya ba ba sau biyu ba ba kuma za a iya ware wani rukuni na mata a ce a kansu kawai yake faruwa ba, yana faruwa ne a makarantun gaba da sakandire.

 

Inda ta ce ‘yan mata da dama da ke manyan makarantu, a kashi dari kusan kashi saba’in sun gamu da wannan matsala.

 

 

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button