GURBIN IDO

GURBIN IDO 46-50

Wani irin bugu zuciyarta take sanda takai step din qarshe na benan,tana ji kamar ta koma,amma kuma idan tayi hakan bata kyauta ba,kamar ta wofantar da maganar baba tabawa ne,ci gaba tayi da takawa cikin tsoro da fargaba,tana tafiya kamar ba zata kai qofar da zata sadata da ainihin falon ba.

Sanda ta isa qofar sai taja ta tsaya cak,ta runtse idanunta da qarfi,a karo na farko zata fara taka sassansa,batasan da wacce fuska zata kalleshi ba,tsoronsa yana nan fal cikin zuciyarta,tanason baiwa kanta qwarin gwiwa,ta dora hannunta saman handle din,ta runtse idanunta gami da dauke numfashinta sannan ta tura ta sanya kanta.

Daga inda yake zaune miqe da qafafunsa saman table din gabansa idanunsa a rufe yaji an motsa qofar,saidai duk da haka hakan bai sanyashi motsawa ko bude idanunsa ba,a zatonsa unaisa ce,wadda ta gaza haqurin zuwa wajensa da ziyartarsa lokaci lokaci,bayan ya riga daya tabbatar mata gaskiyar abinda ke ranshi gami da bata zabi.

A hankali sassanyan qamshin da ya hanashi sukuni wunin yau,ya kuma wuni dashi cikin jikinsa ya fara cika masa hanci,ya kuma gauraye da sallamarta cikin siririyar muryarta din nan mai dauke da wani amo na musamman,ba tare daya shiryama faruwar hakan ba ya soma bude idanunsa da suka sauya launi saboda mintunan da suka dauka a kulle.

Fes ya sauke idanunsa a kanta,cikin shigar da yawanci shaheedansa ke yinta,shigar da yakan tsokaneta da ita zamanin da suna raye

“I want to see my wife gani na haqiqa….. please madam, remove it” murmushi take jifansa dashi,sannan ta zare din tana fadin

“Am all yours,and belongs to you”.

      Haka kawai ya samu kansa da gaza dauke idanunsa daga kanta,wani abu na masa yawo tsakiyan kai kamar ana yamutsa kwanyarsa,duk da cikin hijab take amma hoton dazu ke masa yawo cikin idanunsa,ya qureta da kallon dashi kansa yasan idan da ace ita din ba halaliyarsa bace ya kauceea koyarwar addini,baisan me ya sanya masa qulafucin kallonta haka ba.

    cikin matuqar juriya da kuma dauriya take bawa kanta confidence,abun dazunke tabata,tana jin kakar qasa ta tsage mata ta shige,ko kuma tayi fiffike ta fice a dakin,ta iso gab dashi kana ta sulale a gabansa ta tsugunna,abinda ya bawa turarenta damar isa gareshi da kyau

“Barka da dare” tayi maganar da wani irin tune,sai ya tashi ya zauna sosai yana sauke sambala sambalan qafafunsa daga saman table din zuwa qasa

“Barka” ya amsata a taqaice,bata tsaya jiran cewarsa ko wani abu ba ta fara fidda warmers din,ya bude baki kaman zaiyi magana kiran jabir ya shigo wayarsa,sai ya maida hankalinsa ga amda wayar,inda ita kuma hakan ya rage mata wani mugun nauyi da takeji an aza mata tun farkon shigowarta falon,rawar da hannayenta keyi suka ragu,ta fidda koma ta kuma yi serving dinsa ta jera komai cikin nutsuwa,sai ta miqe ta fara takawa zata bar falon,cikin ranta cike da fata da addu’ar kada wani abu ya tsaidata.

       Dan binta yayi da kallo kadan yana karantar tafiyartata duk da amsa wayar da yakeyi,tamkar wata me tafiya saman rairayi ko yashi mai laushi,duk da bai iys ganin qafafunta saboda hijabin da ya saukar mata,amma kuma yanayin tafiyarta kawai zai gaya maka qafafunta akan tsari suke,janye idanunsa yayi yana jan dan qaramin tsaki,tsakin da ya bayyanarwa jabir ta cikin wayar

“Lafiya?” Ya tambayeshi a taqaice

“No… it’s not a matter,ina jinka” yayi maganar yana sauke dubansa ga abincin,wanda tuni yaja ra’ayinsa,bai kuma iya gama wayar ba ya zamo a hankali daga saman kujerar,ya sanya spoon din data ajjiye masa ya diba ya fara ci.

     Har cikin ransa yaji nutsuwa da abincin dari bisa dari,dama baba tabawa zabinsa ce akan abinci,don haka duk wani tsohon cinsa ya tashi,yaci abincin sosai fiye da kima,ya kuma kwantar da tsohuwar yunwarsa,haka nan ya dinga jin wata nutsuwa na saukar masa,ba shakka samun abinci gamsashe ma rahama ne,duk wata gajiya da kasala da yake ji fiye da rabinta ta kama gabanta,sai ya samu kuzarin yin aikinsa fiye da dazun,ya sake kunna system dinsa,yaci gaba da nazarin meeting dinsu na dazu wanda tuni PA dinsa yayi documenting komai ya aiko masa,ya dinga cire kusakuran da yayi a dazun,lokaci lokaci yana dan jan tsaki,baisan ya akayi gaba daya dan qanqanin abu irin wannan ya dagula masa lissafi ba,saidai duk da hakan a yanxun ma idan ya tuna sai yaji tsigar jikinsa tadan zuba,yakan dan lumshe idanunsa kadan kana ya bude ya ture komai yaci gaba da aikinsa.

     Binta da kallo baba tabawa tayi lokacin da tayi sallama take shigowa falon,sai taci gaba da kallonta baki bude,har ta iso tana zubewa saman kujera

“Wash” ta furta ba tare da tunanin komai ba,ta fadi kalmar ne saboda yadda taji kamar an bubbuge mata gabbanta,uwa uba kuma gudun zuciyarta daya qaru wanda sai a yanzu take qoqarin sai saita kanta.

     Hijabinta ta zare ba tare data lura da kallon da baba tabawa ke binta dashi ba,ta isa ga fridge ta bude,ta fidda ruwa me sanyi saboda yadda takejin maqoshinta ya bushe sosai,bata buqaci cup ba ta balle murfin ta fara sha a hankali,idanunta na hango mata shi cikin falon nasa da bai fiya haske ba,cikin wata abaya ta maza

“A haka he’s very calm and quiet,amma macijin sari ka noqe ne” ta fadawa kanta da kanta tana cire robar daga bakinta,ta dora ragowar saman fridge din sannan ta juyo.

      Sai a sannan ta lura da kallon da babab take mata,ta kuma tsargu,amma kafin ta tambaya ita ta rigata

“Har me?,wai har kin dawo?” Kai ta gyada mata tana neman wajen zama,hannu tasa ta kama baki,sai kuma ta kada kai

“Nidai nasan ba’a ajewa miji abinci a taho a barshi dashi”

“Aiki yake baba,kuma waya ma yake amsawa,so yana buqatar space,may be wayar ta sirrice” ta fada har zuciyarta,saidai ita baba tabawan ta kalli hakanne da sunan bawa kai kariya kawai

“To Allah ya kyauta” yadda baban tayi sai duk maimunatu taji bata ji dadi ba,saboda itama baban kamar bataji dadin yadda tayin ba,to amma kuma ta yaya zata iya zama dashi a muhalli guda?,ko abincin data kai din kawai tasan karambani tayi da kuma bin umarni,tana da yaqinin zaiyi wuya yacu,ta fahimci kamar yana da jin kansa,izza da kuma qasaita,bai taba neman wani abu daga garesu ba cikin gidan dai dai da ruwan sha kuwa,sai taja wayarta kawai ta kunna data tahau sabon Whatsapp dinta,ta kuma fara da yiwa qawayen nata guda uku sallama.

     Taci sa'a kuwa ta samu afrah a online,cikin mamaki take tambayar da gaske itace,sai suka zarme da hira,wadda ta daukesu lokaci mai tsaho,daga bisani sukayi sallama bayan ta bata labarin latest Korean dramas masu zafi da suka fito.

     Kai tsaye ta wuce Vidmate ta saukesu masu yawan gaske,saidai tana tunanin yadda zata kallesu a nutse ba tare da sun hanata bitar karatuttukanta na makaranta ba.

[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 49

  A kasalance yabar sashen nata zuwa nasa,gaba daya ta sakarwa jikinsa wata irin kasala,ya rasa dalilin da ya sanya duk sanda incident irin haka zai faru tsakaninsu sai haka ta kasance.

       Sam bai kula da wanzuwar mutum a wajen ba,har ya kama stairs zai hau yaji an kirayi sunansa a tausashe,sai ya tsaya cak,ya kuma waiwaya a hankali.

     Unaisa ce tsaye,sanye da wata fatar gown,kanta babu dankwali sai qaramin vail data yafa a kanta me shara shara,idanunta a kansa,tana dubansa cikin wani irin kallo wanda ya nuna yadda tayi laushi har cikin idanunta,qasan ranta tana jin wani irin qaunarsa tana fusgarta,zuwa yanzu takai maqura,hakanam tana jin haqurinta yana neman gazawa,tayi iya matuqar qoqari a irin yadda ta saba rayuwarta,sai ta sake sassauta fuskarta tana fatan ya duneta da idanun tausayi,bata taba kawowa cewa izzarsa miskilancinsa da kuma jin kansa sunkai har haka ba,tayi tunanin a kurkusa zata tagi da imaninsa kamar yadda yake tafiya da imanin duk wani da namiji,fara takowa tayi a hankali,yana biye da ita da idanu,har zuwa sanda yaga tana shirin wuce iyakar da yakega ya kamata ta tsaya

“Stop there” ya fada da muryarnan tasa dake dauke d wani irin amo,ba zato babu kuma tsammani sai jinta yayi ta fada jikinsa gaba daya,ta kuma sanaya hannunta ta qanqameshi da kyau idanunta yana tara qwalla.

“Meye haka?, what’s this?” Ya fada yana yunqurin tureta daga jikinsa,saidai hakan bai samu ba saboda yadda ta sake cukuikuyeshi tana fadin

“Na gaji…..na gaji,am going to kill my self indai ba zaka saurareni ba” furucin nata yayi masa banbarakwai sosai atsakiyan kansa,diyar musulmi ke zance aikata ta’addanci a karan kanta?,bawai don ya damu ko kima ya tsorata da furucinta ba yace

“Okay,okay……sakeni tukunna” kamar ba zata sakeshin ba sai kuma ta sakeshi,ta kuma ja da baya tana dauke qananun qwallar fuskarta,hannyensa ya shiga yarfewa kamar wanda wani abun qi ya tabawa fata,fuskarsa ya sake hadewa ya tsare gida sosai yana dubanta

“Am all ears” ya fada yana goye hannuwansa a qirji,idanunta tadan watsa bangaren sasan maimunatu,ta yaya zatayi irin wannan maganar dashi a waje.irin wannan,by mistake yarinyar tazo guftawa ta jisu?,ta tabbatar idan haka ta faru ajinta ya gaba zubewa a idanunta har abada

“Am not comfortable here……i need privacy” kamar bazai amsata ba,sai kuma ya juya ya soma takawa zuwa saman a nutse cikin takunsan nan na daban,ta bishi da kallo tana jin wani abu yana tsarga mata,kafin daga bisani ta soma bin bayansa,tana qiyasta irin kalmomin da zatayi amfani dasu wajen ganin tasha kansa.

        Suna isa tsakar falon idanuwanta na sake sauka ga hotunan shaheeda,yadda ta tsani mutuwarta haka ta tsani bude idanu taga wadan nan hotunan,asalima tana kishinsu fiye da yadda take jin kishin maimunatu,tunda a yanzun maimunatu bata tsare mata komai ba,bata ma.kallonta a matsayin matsala gareta,saidai tana jin haushin amsa sunan matar mijinta da tayi,harara ta jefi hoton dashi,wanda ja'afar dake qoqarin ganin ya saurareta idanunsa suka shaida masa hakan,wani abu me kama da mamaki ya saukar masa

“Harara?,for what?” Maida idanunsa yayi ga sassan da hoton shaheeda ke maqale,dai dai sanda ya dauke dubansa zuwa ga unaisa,itama dai dai sannan ya dauke idanunta zuwa kansa,sai suka hada idanu,kamar an zare wani abu daga zuciyarta taji,bataso ya ganta ba,amma ita ba wannan ne damuwarta ba,damuwarta ta fidda wadda ke cikin hoton daga zuciyarsa gaba daya,kamar yadda ta five a filin duniya,ita kuma ta maye gurbinta

“Uhmm…..go on” takowa ta soma yi tana sake nufoshi,ta dora dukkan wani yanayi da zai baka tausayi a kan fuskarta,saidai tana zuwa gab dashi ya sake dakatar da ita

“Don’t do it” ya fada calmly gami da yi mata nuni da hannu kan yana saurarenta,bata da wani zabi illa fashewa da kuka harda sheshsheqa,abinda ya bashi mamaki ganin cewa shi din bai aikata mata komai ba,fuska ya hade sosai yana dubanta,sai kuma ya kau da kai yana jan tsaki can qasan ransa

“Bansan meye laifi na,ban kuma san me na aikata maka ba,don kawai nace ina sonka ja’afar?,ta yaya da hakkina a kanka tsahon shekara kusan guda ka takemin kamar bakasan da wannan ba”

“Anzo wajen” ya fada a ransa yana jin tana sake ficewa daga ransa,ta yaya yarinya mai cikakkiyar kunya da nutsuwa zata iya duban idanun da namiji…..duk da kasancewarsa mijinta,amma a matsayin budurwa ta gaya masa hakan?,well…..batayi laifi ba,tunda hakkinta ne kamar yadda ta fada din,amma bayajin koda danneshi akayi zai iya aikatawa,hes not in the mood gaba daya,bayajin wani feelings a yanzu a kanta ko dis.

      Kujerar dake daura dashi ya qarasa ya zauna a hannun kujerar,yaci gaba da dubanta hankali kwance sanda taketa kukanta tana sake qara ma kukan salo a fatan da take na samun nasara a kansa,can qasan zuciyarsa yake qissima ta yadda zai raba kansa da wannan matsalar.....eh.....matsala mana,zuwa yanzun yana jin unaisan ta zame masa matsala,babu abinda take haifar masa banda kwasarwa kansa zunubi,bayan yana da tabbacin abune mai wahala ya iya karbarta cikin rayuwarsa,zuciyarsa wata irin zuciya ce mai wahalar sha'ani

“I already told you,zamanmu abu ne mai wahala da ban hango yiwuwarsa,ni am ready to dismissed you,the choice is yours…..karki sake tara ta da irin wannan shirmen” daga haka ya miqe ya nufi bedroom dinsa,ta yunqura zata bishi,saidai ko kafin ta isa ya maida qofansa ya rufe,ta daga hannu kamar zatayi knocking sai ta sauke,ta fahimci wasu daga cikin halaye da kuma dabi’unsa,idan ta sake tayi knocking masa qofa,batasan me zai biyo baya ba,sai ta juya da gudu gudu tana sauka daga stairs din kuka yana kufce mata,ta gaji gaskiya,ta kuma kai maqura,tana jin ta iso geji,batason kuma ta bata dukkan wani tanadi da tayi masa,zata dauki mataki na gaba itama da takeji har cikin ranta da zuciyarta shine dai dai.

Previous page 1 2 3 4 5Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button