NOVELSUncategorized

RAINA KAMA (BOOK 2) 18&19

 ~Book 2~ ????????1819

……………..Na dad’e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad’ai, bansan time d’in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gadon Na nufi Na watsa ruwa.

       Ina tsaka da shafa mai Samha ta shigo, saida tayi sallama nabata izinin shigowa sannan, ledar hannunta Na kalla ina fad’in “mikika samo mana ‘Yar Uncle?”.
          Cikin dariya ta zauna kan sofa tana cewa “kayan dad’i ne Aunty gimbiyarmu, alfarma nazo nema wajenki keda Uncle”.
        Hankalina gaba d’aya Na maido kanta, “Alfarmar mi kuma?”.
         “Aunty gimbiya please ki lalla6a Uncle ya barki muje birthday d’in k’awata Dhibya, ALLAH yarinyarnan tana sonki sosai, kullum hirarki”.
        Nad’an zaro ido  “kai Samha yaza ai naje wani birthday da wannan cikin? kuma kema kinsan bazai bariba tunda Na ‘yammatane”.
        “kai aunty, cikin saikace Wanda yayi wani k’ato, kumafa a cikin gida za’ayi wlhy, iyamu goma ne kawai”.
      “to naji, ALLAH yasa ya bari, mikika kawo mana a ledar?”.
         “yes my sweet aunty, wannan wani sari ne yamin k’yau a wani shagon da muke zuwa siyan kaya, shine nayi alk’awarin siya miki, Uncle Sauban ya cikamin na siya, yanzu Na kar6o please ki gwada muga”.
       Dariya nayi, nace, “inye kaga ‘Yar Uncle Anfara jink’an iyaye, to amma ni ina na iya saka sari?”.
        “kowama koya yayi nidai ki saka muga dan ALLAH”.
       “to shike nan bara na gwada, ALLAH ya saka da alkairi, ina alfahari da d’iyata”.
        Samha ta fita tana dariya, nikuma na warware kayan, masha ALLAH sarin ya had’u gaskiya, farine anmasa kwalliya da pink and silver kad’an-kad’an. Na saka rigar, sai dariya ta kamani, saikace wata bafulatana????????.
        Warware zanin nayi, tofa anan akeyinta, dan ban iya nad’awaba, na tsaya gaban mirror inata gwadawa amma na kasa, dariya ta kamani, yau naga takaina, Samha ta had’ani da aiki.
       Tunda ta fara k’ok’arin d’aura zanin sarin yana tsaye a k’ofa, ya hard’e hannayensa ak’irji kawai yana kallonta, kamar zaiyi dariya saboda yanda taketa murd’e-murd’en d’aurawa.
        A hankali ya taka zuwa inda take, jinai kawai andafa min kafad’u ta baya, na d’ago a tsorace muka had’a ido ta cikin mirror, fuskarsa babu walwala, ya d’agamin gira d’aya, maida idona k’asa nayi, yayinda shikuma ya juyo dani ina fuskantarsa.
        Gwiwarsa d’aya ya saka a k’asa ya dogare d’aya, nidai kallonsa nake mizaiyi?. Batareda ya kalleni ko min magana ba ya zare zanin dake tattare a hannuna, nikam kamar wata sokuwa saina sakar masa.
      Yiyay kamar zai warware zanin, nayi saurin rik’ewa, ya d’ago fararen idanunsa yanamin alamar na saki, ban iya musa masaba na sakar masa.
      Shima sai bai yaye dukaba ya dai-daitashi, ammakina sainaga yana nad’amin, babbar magana Galadima da nad’a sari.
      Dazai saka wanda a ke sokewa a gefen kugu sai yayi dawani salon daya sakani zabira saboda sak’onsa yajemin har kwalwar kai, ya d’ago ya kalleni yana wani miskilin murmushi da d’agamin gira. Sai kawai na lumshe ido dan naji kunya wlhy. Ya mik’e tsaye yana daidaitamin na kafad’ar shima, nidai harya gama ban bud’e idoba. baiyi magana ba ya warware reborn d’in kaina, da sauri na bud’e idon, yanda yawani tsareni da idanu sai nakasa jurewa na maida na rufe.
      Cumb ya d’auka yahau gyaran kai, to nikma naga abinda yafi k’arfina yau d’innan, wai dama guy d’innan ya iya abin mata ne?. Bai barni ba saida ya gama yanda yakeso  dani, ya zubamin ido kawai batareda yace komai ba. nikuma nakasa bud’e idona na kallesa, ahankali yafara busamin iskar bakinsa saman idona, dole nafara marmar da idanu, dainawa yayi, na bud’e idon ahankali a kansa, kuma matsoni yayi muka Zuba juna ido ko k’yaftawa bamayi, gashin dake neman shigarmin ido ya saka d’an yatsa ya matsar, na maida idanun na lumshe ina sauke k’aramar ajiyar zuciya.
       Shima nannauyan numfashi ya sauke kafin yaja da baya, wardrobe d’insa ya nufa, jin yabar wajen saina bud’e idona, duk jikina ya saki, kallo d’aya namasa na d’auke kaina na juya ga mirror Dan naga yanda ya maidani, murmushi nayi ina saka hannu na gyara gashina, nima na yarda da gaske nayi kyau.
     Nakuma d’ago ido da nufin sake kallon kaina sainaganshi a bayana, sark’a ya ziro a ya sakamin tareda gyara zamanta ta zauna sosai a k’irjina, ya janye gashina ta baya yana sak’ala sark’ar, nidai nawa idone, ya gama ya cire d’an kunen dake kunnena ya sakamin na sark’ar, sannan ya mannani da jikinsa yana zagayo hannunsa duk biyu saman matashin cikina, hannuna ya kama yana sakamin bangles, cikin k’asaitacciyar muryarnan tasa yake magana cikin kunnena, “haka dama  sari kema Afirikawa k’yau?”.
      Murmushi nayi, na d’ago idona muna kallon juna ta cikin mirror, haryanzu hannayena na cikin nasa yana saka bangles d’in da guda d’ai-d’ai.
     Ya lumshe idanu yana shanshanar wuyana, jikina yafara rawa, babu shiri na saka hannuna d’aya daya gama saka bangles d’in na shafo gefen kumatunsa, cikin rawar murya nace “please kabari yalla6ai”.
           Batareda ya dainaba cikin sark’ewar harshe yace “mizaisa na daina? yalla6iya”.
        Yanda yake min akan dokin wiya da yanda hannunsa d’aya ke canja salo a jikina sainayi k’ok’arin juyowa garesa, ko hakan zaisa yabari d’in. Ashe dama ma na sake bashi, gaba d’aya yawani rikice kamar ba Galadiman Dana saniba. Hannunsa ya sak’alo kuguna yana kuma matsoni jikinsa sosai, yasaka d’ayan hannun ya tallafo kaina tareda d’ora la66ansa akan nawa.
      Kasa jurewa nayi, na mik’a masa wuya kawai, harda bada gunmawa nima……..
    Tofa munga idi, daga gyaran sari????????????.
            Samha tataho da karsashinta dantaga ko Munaya ta saka, daga nan ta nuna mata yanda zata nad’a zanin sarin, tunda tasan bata iyaba, ko kad’an babu Wanda yaga shigowar Galadima, Dan babu kowa a falon, jakadiya ta tafi asibiti itada Sauban da innarsu munaya, aunty Mimi kuma barci takeyi, Dady kam yanacan baya inda ya maida lambun tunaninsa, itako Samha tana bama Munaya sari takoma d’aki danta bata lokaci ta shirya a tsanake. Sallama d’aya kawai tayi ta turo k’ofar tana kwala kiran “Aunty gimbiyarmu kin saka?”.
        Galadima dayake Neman fara zirmawa yay hanzarin sakin Munaya, da sauri naja baya nima, dan kamar a sama mukaji muryar Samha.
      Itama Samha baya ta koma da sauri gabanta na fad’uwa, Dan ganin Wanda batayi zatoba a d’akin. ALLAH ma yaso bataga komaiba, lokacin datake sako k’afarta a d’akin Galadima ya janye bakinsa yana k’ok’arin matsawane baya.
      Wata uwar harara mai kad’a hanji da hanta ya zubama Samha, hakanne yasakata yin baya da sauri ta koma.
      Nikam kasama d’aga ido nayi balle na kalleshi dagashi har Samhar, saima wani yaam nakejin jikina tamkar zan fad’i.
      Lura da hakan da yayine yasakashi azamar rik’o hannuna, na shige jikinsa ina sauke tagwayen ajiyar zuciya, dagani harshi idanu kowa ya lumshe, tsawon lokaci muna a haka munkasa sakin juna, ahankali na shiga k’ok’arin janye jikina, bai hananiba yabani damar barin jikinsa, ra6awa nayi ta gefensa na wuce, na koma saman sofa na zauna ina dafe kai, juyowa yayi yana kallona, kafin yatako shima zuwa bakin gado ya kwanta, k’afafunsa na k’asa duka, yayinda yay filo da hannayensa yana lumshe idanu.
      Duk munyi shiru d’akin tamkar babu wata halitta mai numfashi a cikinsa, kowannenmu shiyasan mi yake sak’ama zuciyarsa.
      K’arar wayarsace ta sakamu d’an firgita mu duka, duk sai muka zubama wayar ido tamkar wani ojuju. harta tsinke bai d’aukaba, saida aka sake kira sannan ya cirota daga aljihun wandonsa yay picking.
           Muryarsa vary low yace, “Nuren Yaya dai?”.
       Mamaki da al’ajabi ya cika Nuren, yakuma Ciro wayar daga kunnensa ya duba Dan tabbatar da Galadima ne kuwa?, lallai shine, maida wayar yayi a kunne yana fad’in “brother lafiyarka kuwa?”.
      Taune lips nashi yayi, ya yanke wayar, dan indai ahaka zasuyi wayarnan bazai fahimci komaiba, ajiye wayar yayi yatashi ya shige bathroom.
    Da kallo k’asa-k’asa kawai na iya binsa, amma nakasa ko kwakwkwaran numfashi.
      Daga can kuwa Nuren kwashewa yayi da dariya saboda tuno wani Abu, (to su Nuren dai dama bariki sune manyanta????), dariya yakeyi iya iyawa yana dukan kansa, daya fara tsagaitawa saiya kuma saka wata, saida yayi ta ishesa sannan ya daina, ya rik’e ha6a yana fad’in “oh ni su brother ansan takan tsiya, ina ganinsa lab-lab Ashe d’anba sauk’ine, toma uwar miye na d’agamin wayar tunda yasan yafara sauka a network????, yakuma saka dariya saikace wani sabon kamu.????
       Galadima kam ruwa ya sakarma kansa kawai, ya dafe bango da hannu biyu ruwan na kwarara saman kansa, sai faman taune lips yakeyi shi kad’ai, yayi da zuciyarsa ke sak’awa da kwancewa, saida ya ji k’arfi-k’arfi sannan ya kashe shower d’in yaja bathrobe d’in ya saka yana faman sauke 6oyayyar ajiyar zuciya.
      Inda yabarta anan ya fito ya isketa, kallo d’aya yamata ya d’aukekai, bakin gadon ya zauna yana goge kansa da k’aramin towel, yajawo wayar da d’ayan hannun ya danna kiran Nuren.
     Bugu d’aya Nuren d’in ya d’aga, da k’yar yasamu ya danne dariyarsa, “brother wai miya farune naji muryarka haka? nifa ka tadamin hankali”.
        “Ba komai, shin kajene?”.
        Nuren ya toshe bakinsa gudun kar dariya ta kufce masa, Sameer d’an rainin wayone ALLAH, wai babu komai, to naji babu komai aje a haka.
       “wai kana jina kuwa?”. Galadima yafad’a.
       “Oh sorry brother network nayin wasa, gani a gidan, amma bankai ga shiga inda takebane”.
      “ok tom kaje, amma kabar wayar a kunne, inason naji komai”.
      Nuren yace “to”.
Da sallama ya shiga d’akin, sai wani ciccin magani yake.
       Farhat dake zaune bakin gadon  d’akin ta zabga tagumi ta d’ago kai tana kallonsa, yayin da wasu hawaye ke shirin zubo mata.
       Kujera guda d’aya dake d’akin ya jawo ya zauna.
     Farhat ta share hawayen kumatunta, murya a sanyaye tace, “yayana dan ALLAH kayi hak’uri, wlhy ina missing d’in families d’ina da karatuna, dan ALLAH idan kasheni zakayi ka kasheni kawai na hutama rayuwa ma ni gaba d’aya”.
      Murmushi Nuren yayi, idonsa a kanta yace, “bazan kashekiba Farhat, dan bakimin komaiba, kamar yanda na sanarmiki mahaifinkine yaja miki, ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zaki koma gidanku kwana kusa, yanzuma dukba wannanba, wata tambaya nazo yimiki, ALLAH yasa zaki bani had’in kai?”.
       Kanta ta jinjina masa tana kuma share sauran hawayen, “insha ALLAH inhar nasani zan fad’a maka”.
       “good girl ”. ‘cewar Nuren yana gyara zama’.
        “Farhat nasan kinsan duk yaran Abbanki ko?, ina nufin masu masa hidima a office ko a gida?”.
      “Eh nasan mafi yawansu, dan ina zuwa wajensa a Office, kuma wasu acikinsu sukanzo gidanma”.
     “Masha ALLAH, kokin san SD?”.
       “SD!?”.
   “eh shi”.
“gaskiya a yaran Abbana dana sani babu wani mai suna SD”.
         “okay, amma ko wani mai Something sunan dazai iya kasancewa full name bazaki iya hasasowa ba?”.
     Shiru tayi ta lula duniyar nazari, shidai Nuren ya zauna mata idanu yana kuma jinjina ma ubangiji akan yin k’yak’yk’yawar hallita, dan Farhat black beauty ce masha ALLAH.
      A jiyar zuciya ta sauke, “yaya inaga kamar dai akwai wani Sagir dauda dana Sani, amma bansan aikin da yake a k’ark’ashin Abbanmu ba, sai kuma ya Shareffudden k’anin Aunty Umma, sai Steven Daniel”.
       “shi Steven d’in wanene shi a gidanku, itama Aunty Umman haka?”.
      “Driver d’insu Mom ne, shike kaisu anguwa, ita kuma Aunty Umma matar Abbanmu ce ai, itace amaryarsa”.
      “Uhyim”. Nuren yafad’a yana jinjina kai.
        “Dan ALLAH yayana in tambayeka mana?”.
     “ina saurarenki”.
“laifin mi Abbana yamuku hakane?”.
       murmushi Nuren yayi, “karki damu nangaba kad’an komai zai wuce, kuma bashi yay laifinba, wanine yayi na kusa dashi”.
      “to ALLAH yasa Ku kamashi, amma dan ALLAH karkuma Abbana komai”.
      “insha ALLAH babie”.
     Murmushi Farhat  tayi, Nuren kuma ya mik’e tsaye idonsa a kanta. “babu dai wata Matsala ko?”.
      Cikin shagwa6ar data saba tace, “please ko TV ka samin, banajin dad’in zaman hakanan”.
      “Am sorry to say dear, har kibar gidannan dokace, babu television, babu phones, amma way not nakawo miki irin Hausa novels d’innan danaga mata na karantawa?”.
      Idonta ya cika da kwalla, “ayya yayana wlhy ban iya karatun hausaba sosai, yana bani wahala”.
       Ido yad’an zaro waje, yace, “saboda mi? Keba bahaushiya bacene?”.
      “bahausa mana”. ‘tafad’a cikin turo bani irinnan ta6ararru’.
      Baki ya ta6e yana kama hanyar fita, “zaki cigaba da kad’aicinki ashe kuwa”.
      Ganin zai fice da sauri tace, “please ka siyo zan fara koya to”.
      “it’s better”. ‘yafad’a yana ficewarsa’.
       Saman gadon ta fad’a ta fashe da kuma mai ban tausayi.
    Duk abinda ke faruwa Galadima najin komai ta waya, Munaya ma na zauna a sofa har yanzu tana satar kallonsa, amma batajin miyake saurare da ya nutsu haka.
    Cire wayar yafara k’ok’arin yi ya jiyo muryar Nuren na fad’in “hello brother kana jina?”.
     Galadima yace, “eh”.
       “okay duk kaji aimi ta fad’a ko?”.
      “duk najiku, saika samin ido akan duk d’unsu, a bincikomin komai daya shafesu”.
     “indai wannanne insha ALLAH angama, amma ni a ganina banda wannan Shareffuden d’in datace, domin babu wani kamanni a cikin nashi sunan, ballema tace k’anin step mom natane”.
       “Humm Nuredeen kenan, shifa mak’iyi ba’a rainashi, mutane da yawa sukan d’auki cinnaka ba komaiba, amma idan yacijesu sukan ji cizon har a ransu, dan haka karka ta6a d’aukar mage mafi sauk’i akan kare, itama idan taga nama citakeyi”.
     “wannan gaskiyane brother, ALLAH yabamu sa’a”.
       “amin ya rabbi, naji kuna maganar buks da ita, kaje ka samo mata dukkan Wanda take buk’ata, har English novels d’in, sannan ak’ara tanadar mata dukkan abinci mai k’yau datake so”.
      “insha ALLAH angon Munaya”.
      Girgiza kai kawai Galadima yayi ya yanke wayar.
       Kallon Munaya yayi suka had’a ido, saita janye cikeda basarwa. Shima tashi yayi ya koma gaban mirror, duk uzirinsa yayi ya gama sannan yamatsa ga wardrobe ya ciro kayan dayake buk’ata.
      Ganin haka Munaya tazame ta kwanta cikin kujerar yandama bazata gansaba.
     Baki kawai ya ta6e yacigaba da saka kayansa.
         Bayan yagama yamatsa kusada ita, “tashi ki canja kaya ki rakani wani waje”.
      Fuska Munaya tad’an yatsina, kamar zatace wani Abu saikuma ta yunk’ura zata tashi kawai, hannunta ya kama ya taimaka mata ta tashi zaune. fita yayi abinsa. Hakan yasata fahimtar zai jirata a falo kenan.
        Bata 6ata lokaciba ta canja kayanta da atanfa skt da riga, takawo after dress ta saka sannan ta nad’a Vail d’in rigar, d’as ta fito itada cikinta, kamar ka saceta ka gudu abinka.
     Tunda ta fito ya zuba mata idanu, ko k’yaftawa bayayi, saida yaga tana gabda k’arasowa garesa ya basar yana mik’ewa. Gaba yayi tabisa abaya, yandama yake taka steps d’in benen dolene ya birgeka, duk takunsa nakan idonta, yayinda itama take binsa daki-daki a hankali.
      Babu kowa a falon, dan haka suka fice basu nemi kowanba.
 
       A mota yana tuk’i da sauraren karatu itakuma tana latsa waya suna charts a families group d’insu. Sai murmushi take zubawa, duk abinda take yana kallonta ta gefen ido. Sun isa wani k’aton shagon saida kayan babies, duk abinda kake buk’ata zaka sameshi indai na yarane daga 1year zuwa 15. Itadai mamaki ya ishi Munaya, miye nawani kawota nan? yabari a haihun mana ma.
         Tarba ta musamman aka musu, hakan ya tabbatar ma Munaya yasan mai shagon kenan, dan yanda aketa girmamasu sai abin ke bata mamaki. gashi indiyanci sukeyi bata fahimtar maganganunsu. Itadai tana zaune hankalinta ya rabu gida biyu, wajensu Galadima da kuma wasu mata biyu da yaransu uku dabazasu wuce 7-7years ba, yaran k’yawawa masha ALLAH, ga wayo.
        Galadima ya juyo zai mata magana saiya lura da inda ta zubama idanu, shima shagala yay a kallon yaran, iyayensu na za6ar kaya amma su suna tibirewa sai Wanda sukeso za’a d’auka. Munaya sai zuba murmushi takeyi, dan suntafi da imaninta, shima murmusawa yayi yana lasar lips, kafin ya d’auke kansa ya maida ga Wanda suke maganar.
     Zuwa can gardama ta hark’ume tsakanin yaran akan wani game da iyayen ke dubawa maybe zasu saya musu ne. Kuma games d’in suna kusada Munaya ne, d’aya a cikin yaran ya d’akko yazo wajen Munaya yana tambayarta wai “Aunty wannan yafi dad’i aidai ko?”.
     Munaya bata fahimceshiba, dan yayi maganane da yaren dabata ji, dan haka saitayi murmushi ta tambayesa yanajin English?.
     Yaron ya d’aga mata kai alamar eh.
    Ta kuma murmusawa, duk abinda ke faruwa a idon Galadima ne.
       Da turanci munaya tace, “yarona kai kata6a irin wannan game d’inne?”.
      Murmushi yamata shima, yace “aunty akwai dad’i ma sosai, ranar saida na cinye kharan a gidansu ma”.
      “da gaske?”. munaya tafad’a tana dafa kafad’arsa.
    Kansa ya d’aga mata, cike da d’oki yace, “Aunty na koya miki?”.
    Munaya ta d’aga masa kai.
      Game d’in ya d’ora a cinyarta, ya danna wasu Number, sai kuma ya zubasu cikin d’aya, duk suka shige. Cikin mamaki munaya tace “mikenan to?”.
      Shima dariyarsu ta yara yayi, yace “Aunty ai wayo na miki, Abu guda d’ayane, amma sainayi ammafani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d’aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had’a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d’aya ne na had’aka kuma akan Abu guda d’aya kacal”.
       Sosai abun ya birge munaya, tayi dariya har hak’oranta na bayyana, jawo yaron tayi a jikinta ta rungume.
     Iyayensa dake tsaye suna kallonsu tun d’azun duk sukayi dariya suma, sannan suka matsa kusada munaya suna bata hannu alamar gaisuwa. itama ta mik’a musu suka gaisa, d’aya tace sunanta Radha, d’ayar kuma tace Anjali, munaya ta fad’a musu nata suna itama, sannan takamo hannun saran yaran tana tambayarsu suma, d’aya yace vanish, d’ayan kuma Anjun, duk kumatunsu ta sumbata tana sakama rayuwarsu albarka.
     Wadda tace sunanta Radha tace  “kiyi hak’uri da surutun Vishnu shi baya gajiyane ko kad’an”.
     Munaya tace babu komai.
        Daganan sukai gaba, munaya tana binsu da kallo tana murmushi, yaran sai waigenta suke suna d’aga mata hannu.
    Sunje wajen biyan kud’i akace subar kud’insu inji mai shagon, da mamaki suka tambayi wanene? Mikuma yasa ya barmusu.
        Mai kar6ar kud’i ya murmusawa yana fad’in mijin matarcan da kuka gaisane mai shagon ai.
       Munaya batasan mike faruwaba taga sun dawo, godiya suka shiga yimata, ta tambayesu akan me?.
     Suka bata amsa da cewar mijinta bai kar6i kud’in kayansu ba. Murmushi tayi, k’asan ranta tana mamakin dama shagon na Galadima ne?.
       Sun katse mata tunani da tambayar kozasu samu number ta, babu musu tabasu sukayi sallama suka tafi.
      Maida kallonta tayi ga Galadima dake zaune yanata latse-latsen laptop tamkar baisan mike faruwaba, da alama yana duba kayane ko wani Abu, dan time to time Wanda yake gefensa yakan nuna masa wani yanki na kayan dake shagon, shikuma ya waiga ya kalla, idan bai hango sosaiba saiya kalla ta cikin Computer d’in dake tareda cctv cameras d’in shagon.
        Munaya tace kai mutuminnan akwai son kud’in tsiya, kai komai kana saidawa, wata zuciya tace idan bai nemi kud’iba dame zai kula da mahaifinsa?. “hakane kuma”. ta fad’a a fili tana sauke ajiyar zuciya.
       Kusan mintuna 15 saitaga ya taso ya nufota. Zama yay kujerar kusa da ita yana fad’in “sorry friend na barki ke kad’ai. kin gaji mu tafi ko?”.
       Munaya tad’an yamutsa fuska tace “ba sosaiba”.
       Ya d’an murmusa, “ok tunda baki gajiba kozaki d’an mana taimako ni da abin cikin kwan?”.
          Hararsa tad’anyi, itafa haushin wannan abin cikin kwan dayake fad’a takeji.
       Hannu yasa ya dafe bakinsa yana fad’in “maida wuk’ar”.
           A tare suka dinga zagayawa cikin shagon, dayake babbane sosai, kayan yarane kuma zalla a wajen, komai bibbiyu take d’auka, baice komaiba, dan yasan dai bai wuce tana had’awa da cikin ‘Yar uwarta Munubiya bane. Sund’an d’iba kaya babu laifi, yabada ATM d’insa aka d’auka harda na wad’ancan matan, yaran shagonne suka kai musu har cikin mota.
        Yanzuma haka suka taho tamkar kurame.
    Kowa da abinda yake sak’awa….
       Danja data tsayar damune yasakashi juyowa yad’an kalleni, ganin hankalina nakan wasu yara ‘yan makaranta dake mota yace, “dama haka kike da son yara?”.
        Juyowa nayi Na kalleshi, amma saiya d’auke kai tamkar bashine yay maganarba ma.
     Nima maida kaina nayi ga yaran, a kuma time d’inne muka sami damar barin wajen.
     Saida muka fara tafiya nabashi amsa da “yalla6ai kenan, waye zaice baison yaro, a duniya babu abinda yafi k’uruciya dad’i”.
       Kad’an ya juyo yad’an kalleni yana fad’in “really?”.
        Nima kallon nasa nayi ina fad’in “na tabbata amsarnan kowama zai baka idan ka tambayesa”.
      Bai kalleniba yanzun kam, hankalinsa naga tuk’insa, yace, “ALLAH ya kawoka duniya lafiya abin cikin kwan”.
      “shiru namasa bance uffanba”.
      Har muka isa gida kuma babu Wanda ya sake magana a cikinmu. Saida yay parking motar a harabar gidan sannan ya juyo gareni, ina niyyar bud’ewa Na fita ya ruk’o hannuna. kallonsa nayi da mamaki, yawani ci magani irin babu raininnan, kamar zanyi magana saikuma nayi shiru muka zubama juna ido, kowannenmu zuciyarsa Na bugawa da sauri-sauri. Cikin k’asaitarnan tasa yace, “Addu’a nayi amma jan aji yahanaki amsamin da amin”.
       Ni dariyama ya bani wai jan aji, hakanne yasakani murmusawa kad’an ina k’ok’arin janye idona daga cikin nasa, amma saiya hanani hakan, nace, “na amsa ai, bakaji bane kawai”.
       “aiba kurma kika auraba”.
      Uhm wannan aure ana tak’ama dashi, Na fad’a a raina, a fili kuma nace, “a zuciya Na amsa”.
       “k’arya haramun, banji wannan sak’onba a tawa zuciyar”.
      Da mamaki Na waro idanu waje ina fad’in “ban fahimceka ba”.
     Lips d’insa yad’an ciza da hak’ora yana matsoda fuskarsa dab da tawa, gashi ya sark’eni da idanu nakasa matsawa, d’an yatsansa ya d’ora saitin zuciyata, muryarsa k’asa-k’asa tamkar mai rad’a yace, “zuciyoyi aminan juna sukan kar6i sak’on juna alokacinda d’aya ya aikashi ga d’aya, karki jahilci kanki har yanzu akwai sauran dama”…..
     Yana gama fad’a ya saki hannuna, tareda bud’e motar ya fice.
     Galala nabisa da kallo tamkar wata sokuwa, nakasa motsi nakasa fassara zantukansa da ma’anarsu.
    Tsawon mintunan dahar bayin gidan sungama kwashe kayan da mukazo dasu ban fitoba, bud’ewa naji anyi, hannunsa kawai ya mik’omin alamar nakama Na fito. tamkar sokuwa haka Na d’ora hannun cikin nasa, ya kamoni ahankali Na fito, maimakon ya sakeni saiya jawoni Na shige jikinsa, ya d’ora kansa a dokin wuyana, cikin kunnena yace “wasu bayanan basa buk’atar fassara, ayanda sukazo ahaka ake barinsu, karki zurfafa tunani, dan yana kawo ciwon kai da hana Hutu”.
     Ya d’ago kaina tareda janye jikinsa yana d’agamin gira da salute d’ina, ya juya zuwa cikin gida.
     Binsa kawai nakeyi a baya tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki.
        A falo muka iske duka ahalin gidan, har Momma dazata kwana yau a gida, Abba ne kawai babu, muduka sun birgemu, Dan hira suke ta nishad’i da girmama juna.
    Dagani harshi gaishesu mukayi, Sauban da Samha dasuka k’arasa da kayanda da bayi suka shigo dasu suka sakko daga samanmu suna mana sannu da zuwa.
     Ni kad’ai Na amsa, Galadima hannu kawai ya d’aga musu.
       Momma tace, “kuje ku huta mana”.
      mik’ewa mukayi duk a kunyace, ina gaba a yanzu yana baya, suduka da kallon sha’awa suka bimu, dad’i da farinciki Na ratsa zukatansu, innarmu harda kwalla suka cika idonta, Wanda ita kad’ai tasan fasaarar kayanta.
★★★★★★★
     Da daddare Galadima Na zaune akan sofa ya d’aura k’afafunsa saman teble yana latsa laptop, yayinda Munaya ke zaune a tsakkiyar gado tana karatun wani English novel na Galadima, buk d’in love story ne dan haka taketa faman zabga murmushi, lokaci-lokaci yakan d’ago ido ya kalleta, saboda idan tayi murmushi yakan jiyo sautinsa.
     Maida kansa yayi, yacigaba da aikinsa dayakeyi akan numbers d’in layin Abba na sirri, kwatsam sai maganar yaron d’azu na shago mai suna Vishnu ta fad’o masa a rai.
         *_Aunty ai wayo na miki, Abu guda d’aya ne, amma sainayi amfani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d’aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had’a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d’aya ne na had’aka kuma akan Abu guda d’aya kacal._*
     Saida yakuma maimaita maganar kusan sau uku a ransa, kafin ya kalli Munaya da dukkan hankalinta ke kan Novel,
       “Friend!”.
  Ya kirata a nutse.
        Da “na’am” Na amsa ina kallonsa, saikuma Na janye saboda wandon jikinsa baiko rufe masa cinyaba, sai k’aramar riga mara hannu.
      Yace, “mikika fahimta ga zancen abokinki na shago?”.
      “abokina? waye abokina?”.
      Tasowa yayi dagashi har laptop d’in da coffee d’insa ya hawo gadon, nima saina tashi zaune sosai.
     Ya zauna ta gefe tareda ajiye mug d’in hannunsa a drowa d’in gefen gadon, laptop d’in kuma a saman gadon d’ayan gefensa. hannu ya mik’amin alamar nazo.
     Ban musa masaba Na matso, ya kamoni ya sakani a jikinsa, dan tsakkiyar k’afafunsa ya sakani, saina zame Na kwanta na d’ora kaina a cinyarsa, (dama wajen lak’ewa nake nema????).
     Ya kar6i buk d’in hannuna ya ajiye gefe, ya d’ora hannunsa a saman cikina.
     Kuma maimaita masa tambayar nayi.
     Ya shafa sajensa yana cije lips, “miyasa wataran kike da basarwa”.. 
      “ni d’in?”. ‘nafad’a ina nuna kaina da kallonsa’.
      Bai bani amsaba yace “ina nufin yaron d’azun”.
      “Oh sorry”. nafad’a ina gyara kwanciyat.
     Nace, “wai Vishnu? ”.
    Kansa ya d’aga min
      “to amma wace maganace tasa? tazama abin nazari yalla6ai?”.
       “game”.
“game! game!” nashiga fad’a ina k’ok’arin tunanowa.
      “okay, wai yanda yafad’i yaci game d’in?”.
      “Uhhm”. ya fad’a a tak’aice..  
       Nikuma saina murmusa, “to dukda dai bansan ma’anar d’aukar maganar da muhimmanciba amma anawa tunanin yana nufin _abinnan mabanbantane, amma saiyayi amfani dasu cikin Abu d’aya, kuma sukai masa aiki iri d’aya, sannan duk shi kad’ai ya sarrafasu akan Abu d’aya bawai yayi tarayyar da wasu mutane da yawa bane ko aikinsa had’aka,_ wannan itace fahimta ta ga zancen nasa”.
     Lumshe ido Galadima yayi, ya duk’o a hankali ya mannamin Sumba mai k’au a goshi. Sannan ya d’akko novel d’in ya damk’amin a hannu, yajawo laptop d’insa yacigaba da aikinsa.
       Kallon mamaki kawai na zuba masa, kokad’an ban fahimci muhallin maganar tasaba da son fashin bak’i.
     Batareda ya kalleni ba, idonsa akan system d’insa yace, “kallonfa?”.
     Janye idona nayi ina ta6e baki.
    Shima saiya ta6e nasa alamar yaganni kenan. karatuna nacigaba shima yacigaba da aikinsa yana shan coffee time to time.
        Yayi aiki mai tsawo kafin yasaki wani murmushi da ajiyar zuciya, ya kalli munaya da barci ya kwashe, fuskarta ya shafa yana kuma sakin wani murmushin, “tabbas gaskiya Vishnu ya fad’a, mutum d’ayane ke amfani da Numbers daban-daban wajen kiran Abba munaya, duk wadda yagama da ita bazai sakeba, tagama aikinta, a wannan karon lallai kunyi aiki da basira, wadda harta birkita tunanin Sameer, kuna kiran Abba da mabanbanta Numbers wad’anda kunrigada kun gama shirya matakan da kowacce number bazata sake aikiba, shima kansa ya d’auka mutane daban-dabanne ke kiransa. O ALLAH wannan shine bada k’afa, to ai inkunsan wata bakusan wataba kuma, Muhammad Sameer ruwane, idan bakasha yanzuba zakasha anjima, idan kak’i kuma k’ishirwa ta kasheka. Inhar tarkon dazan d’ana zai d’annu dai-dai, tabbas zan cafke kurayen daji mai duhuwa a wannan karon”. ‘Ya k’are maganar da jan hancin munaya yana kuma sumbatar goshinta’.
     Kwanciya ya gyara mata sosai, ya ja bargo ya lullu6a mata sannan yaje bayi ya d’auro alwala, kamar yanda ya saba ya raya wannan dare da nafilfili da godiyar ALLAH, kafin yazo ya kwanta gefen munaya zuciyarsa na cike da annashuwa da farinciki, kaikace komai yayi done ne.
      Addu’a ya musu sannan yasakata jikinsa barci ya Lula dashi shima.
        Nima mai d’aukar rahoto bara nad’an rintsa my sweet sisters????????………………….????
Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, nayi up date WhatsApp d’inane????????????????????

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu????

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button