JIDDATUL KHAIR

JIDDATUL KHAIR 3

Abuturrab na xaune parlon Umma tare da Ahmad suna cin abinci a tare, Umma dake xaune tana kallo tace “Toh ba dole ku yi shiru ba dama” murmushi kawai Abuturrab yyi, Ahmad yace “Ni xan kawo maki ita ai ta gaisheki Umma….” Umma ta katse sa tace “Ka kawo min wa?” Bai kuma cewa komai, Abuturrab yace “Warce xai aura wai Umma” Umma tace “Akwai wata da xai aura bayan Ramlah ban sani ba?” A tare suka kalleta, Ahmad dai ya ci gaba da cin abincin gabansa bai ce komai ba, Umma tace “Ban da dai ku yaran yanxu abinda ku ke hange daban gida bai koshi ba ai ba a kai waje ba, is there anything wrong with Ramlah da baxaka iya aure ba?” Still Ahmad bai ce komai ba, Umma tace “Ni baxan yi abinda xai cutar da kai ba, meye da Ramlan da baka sonta ka gaya min” Jin bashi da abun ce mata ta mike ta fita daga parlon, Abuturrab dai sai kallon Ahmad yake, bayan few seconds Ahmad ya dago ya kallesa, d’an murmushi kawai yyi ya ci gaba da cin abincinsa, calmly Abuturrab yace “I dont want to believe kayi ma Umma shiru ne saboda Ramlah kanwata ce” Ahmad ya d’an kallesa sai dai he was mute, Abuturrab ya girgixa kai yace “Don’t be quiet because of me, coz if i were in ur shoes i wont keep quiet, baka son Ramlah ga warce kake so to meye na yin shiru? Abinda ake tunanin shi xai karfafa xumunci shi ke 6ata shi, meet Umma…. Pour out ur mind to her, tell her who u intend marrying” Murmushi kawai Ahmad yyi ya maida dubansa kan TV, mikewa Abuturrab yyi yace “Xan amsan ma Ummi drugs a pharmacy so i will be on my way now” Ahmad yace “Alright, anjima da daddare xan shigo in sha Allah” Abuturrab yace “Ok then” daga haka ya fita parlon, amma sai da ya fara shiga main parlor yyi ma kanwar Mahaifiyarsa sallama sannan ya fita gidan. Abuturrab na bedroom dinsa bayan magrib Ahmad ya shigo, Ramlah ce biye a bayansa hannunta rike da cup din shayi da xata kai ma yayanta kamar yanda ya sa ta, Ahmad ya xauna gefen gado, Abuturrab na kallon Ramlah bayan ta ajiye shayin yace “Aunty ta dawo?” Ta girgixa kai tace “Aa bata dawo ba” Yace “Ohk” Ta kalli Ahmad dake danna wayarsa tace “Ya Ahmad su Umma fa?” Ya kalleta yace “She is fine, ya school?” tace “Lafiya lau, ya su Siyama” Yace “Alhmdlh” tace “Kai ma in hado maka shayin?” Yace “Aa sai kace nine Abuturrab” Dariya tayi, Abuturrab dai bai ce masu komai ba, ta nufi kofa, bayan ta fita Abuturrab yace “Mun yi waya da El-Basheer daxu yana gaisheka” Ahmad yace “Oh Yarima, kwana biyu bamu yi magana da shi ba ma” Abuturrab yace “Xai shigo Kadunan amma may be kana Abuja lkcn” Ahmad yace “Allah sarki, Allah ya kawosa lfya” Abuturrab yace “Did u talk to Umma?” Ahmad yace “About what?” Abuturrab yace “Ohh har ka manta” Ahmad yyi murmushi yace “No i dont need to, tunda ga abinda Umma take so, in sha Allah hakan xa ayi” Abuturrab ya mike a fusace yace “What nonsense, why will u say so bayan kai ba son hakan kake ba” Ahmad yace “Tunda Umma tana so nima dole in so” Abuturrab yyi masa kallo yace “Why just speak like an illiterate now?” Ahmad yace “Wait Captain, is there anything wrong with Umma’s choice?” Abuturrab yace “Yes tunda ba son choice din kake ba” Dariya Ahmad yyi yace “Mun ta6a magana da kai nace bana son Ramlah? Asali ma duk cikin cousins dina babu wanda muke shiri da irin Ramlah, Ramlah was kinda brought up in our home since she was 2, tunda takwaran Umma ce kuma rainonta ce ita shi yasa take son ta hadamu, fine if Ramlah is okay with that ni bani da damuwa” Tsaki Abuturrab yyi ya koma ya xauna, Can yace “Ita kuma Maryam din dama yaudaranta kake kenan?” Ahmad yace “Idan wani xai min wnn kallon banda kai Abuturrab, it’s just that my Umma’s choice is my choice” Abuturrab ya jawo wayarsa dake ring ganin Aneesah ke kiransa ya katse ya shiga kiranta, Ahmad ya mike yace “Bari in gaida Ummi” daga haka ya fita dakin….

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button