NOVELSUncategorized

KWAI CIKIN KAYA 10

  ????ƘWAI cikin ƘAYA!!????


                 BOOK ONE
                    Shafi na goma
______________
………..Wani siririn fito ya saki yana mai kallon kowacce kusurwa ta gidan.
      Hakanne ya saka yaransa fahimtar jama’ar gidan ya kema kiranye.
     Mai-tawaga, babban yaronsa ne yay magana cikin muryarsa mai kama da ƙattan farkon ƙarni, ga amo gata a matuƙar buɗe.

      Kafin kace mi jama’ar gidanmu sun fara yo waje da gudu-gudu.
        Muma dai ayari mukabi, duk da Firdausi taso yin tirjiyar ƙin zuwa, sai da inna tai mata magana sannan ta biyo bayanmu dan dole.
          Kowa tsaye yay a ƙofar ɗakinsa yana jiran ƙarin bayani, abunda zaisa kaji tausayinmu kuwa hatta da mazan gidan sun koma mata maza, dan kuwa suma sunzo sun jeru a cikinmu, bayan kuma mafi yawansu sun girmi Jazugan, harma da waɗanda zasu iya haihuwarsa.

          Har yanzu yana a bakin ƙofar tsaye, yana jingine a jikin bango dukkan hannayensa na cikin aljihun wando three queater ɗinsa a zube, rigace armless mai zanen tutar ƙasar Amurika a jikinsa, hakanne yasaka bayyanar ƙaton bandejin da aka naɗe damtsen hannunsa dashi, tabbacin yaji ciwo a wajen kenan.
       Jajayen idanunsa ya ɗago yana kallonmu, sai kuma ya fara takowa yana wani rausayar layi irinta marasajin maganar gayu, fito ya fara rairawa yana cigaba da tinkaromu.
           A gabana yazo ya tsaya cak.
     Wata irin bugawa zuciyata tayi, tare da yin zallo tamkar zata fito, nai wuƙi-wuƙi da idanu kamar an tsamo zomo daga ruwa, addu’ar da nake ƙoƙarin haɗowa a harshena sam ta kasa haɗuwa……
         hijjab ɗin dake jikina ya cikuykuye ya maidashi iya wuyana, yakamashi a hannu tamkar zai shaƙeni ya jani zuwa tsakkiyar gidan yana cigaba da fitonsa, Saikace wanda ya sayo akuya a kasuwa.
     Duk da bansan warin giyaba inada tabbacin warinta ke tashi a jikinsa.
      Yanda jikina ke rawa ina hawaye da ƙoƙarin bashi hakurine ya sashi kallona cikin razanarwa, ya ɗora yatsansa saman bakinsa yana faɗin “Shiiiiii”.
       Duk da hawayen basu bar kwaranya ba dole haka na gumtse bakina kuwa.
     Ƴan gidanmu duk sun tsorata, innar Firdausi kam ta kasa kallonmu, saima naga kamar kuka takeyi.
           Ya gyara tsayuwarsa mai kama da zai ɓalle biyu yana dakama jama’ar gidan tsawa.
       “Kowa ya ɗago ya kalleni, dolene yau na nuna muku real jazuuli, ina son ku ɗauki darasi akan wannan mara kunyar yarinyar, yanzu ni har nakai matsayin da zan saka wani aiki a duniyarnan yaƙi min? Wato ɗaga ƙafar da nake mukune har take bama wasu lasisin bijiremin ma……..”
       “Kai wanenen da baza’a bijire makaba, wawa kawai sauran giya da wiwi, mikake takama dashine shin? Da har kake tunanin sai an bika dole? Ko ka ɗauka tsoronka akeji….”
     Firdausi ce a matuƙar hasale take wannan maganar tana nuna Jazuuga, takowa tai inda muke ta fisge hannun Jazuga daga hijjab ɗina a rikice..
     Gaba ɗaya jama’ar dake wajen babu wanda bai zaro idanun mamaki ba, sai dai saukar ƙarar marin da ɗaya daga cikin yaran Jazuga suka saukema Firdausi ya kuma sakamu sake firgicewa.
        Gaba ɗayansu sukai ribdugu akanta suka hau duka.
    Hakan ya sakani fashewa da kuka ni da inna mukayo kansu, amma ni sai Jazuga ya fisgi hannuna ya nufi ɗakinsa dani.
    Kuka nake ina tirjewa, shima yana jana a matuƙar fusace.
       Ai sai gidan ya kuma ruɗewa da koke-koke.

          Inaji ina gani ya kaini ɗakinsa, babu ko tausayi ya hankaɗani kan gadonsa, ihu na shiga kwarawa iya ƙarfina, amma babu mai ceto.
    Inaji ina gani jazuga ya fara ƙoƙarin shiga mutuncina, UBANGIJI sam bai kasance azzalumin sarkiba, hakanne yasaka kawo wani haske a rayuwata, dan kuwa ina lalubawa sai ga ƙarfen da bansan kona mineneba, jawosa kawai nayi na maka masa akansa.
      Wata razanannniyar ƙara mai firgitarwa ya saki, kafin yay luuu zuwa gefe, jini kuwa tuni ya ɓalle har a jikina.

      Ihun Jazuga ya saka yaransa barin dukan Firdausi data gama fita hayyacinta sukayo cikin ɗakin.
         Su duka kansa sukai suna kiran sunansa, da wannan damar nai amfani wajen fitowa da ga ɗakin da gudu, dukkan illahirin jikina rawa yakeyi, dan kuwa nasan tabbas na kasheshi.
         Ban saurari dukkan masu min magana ba cikin ƴan gidanmu, dan kuwa hannuna da gaban ƙirjina duk jinine, nasan mafita ɗaya ta ragemin shine nabar gidan. Hakan yasa na zaɓi ficewa ba tare da nasan ina na dosaba.

         Fahimtar Jazuga baya numfashi ya saka wasu a cikin yaransa biyo bayana suma a guje, ganin hakanne ya saka ƴan gidanmu suma fara guduwa zuwa wajen.
         Atake anguwa ta ruɗe, wasu gudu kawai suke amma basusan akanmi bane, wasu kuma azatonsu bomb ne ma.
    Ruɗewar da anguwarmu tayi baki ɗayane ta bani damar samun wajen ɓuya, dan kuwa wuuff nayi a cikin massalaci, nashige cikin mankarar dake jingine a bango taimin katanga.
     Dukkan ihu da anguwar ta ɗauka inajinsa, harma da ƙarar guje-guje, taimakon da ALLAH yaymin babu wanda ya shigo massalacin, dama kuma ban iske kowa a cikiba.
          Kusan mintuna talatin anguwar bata lafa ba, saima ƙarar jiniyar motar ƴan sanda danaji, ƙara tsurewa nayi da tsoro, nasan dai ni akazo kamawa ba waniba, kuka nake sosai, hannuna dafe da bakina, na jiƙe sharkaf da zufa har diga nake, duk mai imani ya ganni a wannan halin dolene hankalinsa ya tashi.
    Nai wujiga-wujiga na fita hankalina gaba ɗaya.

         
      Ɓangaren su Jazuga kuwa dai a tare dashi babu rai babu alamarsa, yaransa da sukabi Bilkisu tare da saka ƴan anguwa gudun dolene ya ankarar da ƴan sanda, hakanne ya sakasu zuwa dan suga mike faruwa.
       Har cikin gidan ƴan sandan suka shiga, kowa ya fice a gidan, innar Firdausi ce kawai tsigunne gaban Firdausi dake kwance itama babu rai a tsakar gidan, sai yaran Jazuga guda uku da keta kai kawo a kansa shima, harma sun fito dashi waje da nufin kaisa asibiti saboda jinin dake malala a kansa.
         Zuwan ƴan sanda yay dai-dai da zuwan Alhaji Lado naira, hankalinsa tashe ya hankaɗe ɗan sandan gabansa ya nufi wajen ɗansa yana ƙwala kiran sunansa.
      Atake nanma gidan ya kuma ruɗewa, dan mutane sunɗan fara shiga hankalinsu suna shigowa gidan suga mike faruwa.
          Bayan bayani da ɗaya acikin yaran jazuga ya shirya na ƙarya, da kuɗin da alhaji lado ya ɗebo a aljihu ya bama ƴan-sandan yasasu jiki na rawa suka kira Office ɗinsu, tare da shirya nasu tsarin akan Bilkisu ce tai kisan duk ita kaɗai, saboda Jazuga saurayintane, tazo ta gansa da ƙawarta Firdausi shine tayi yunƙurin kashesu ta hanyar kawo ƴan daba suka doki Firdausi, itakuma ta ƙwalama Jazuga abu a kai.
           Innar Firdausi dake kuka tana faɗin ƙaryane ƴan sandan suka kaimata duka, ɗaya a cikinsu yace a fiddata daga gidan kafin manyamsu suzo.
     Hakan kuwa akayi, dan an kulle innar Firdausi a ɗaki bayan an ɗaure bakinta.
    Koda ƴan sandan sukazo akan bayanin ƙaryar suka zauna, dan basusan minene gaskiyarba, an ɗauki Jazuga da Firdausi zuwa asibiti, bayan ƴan sanda sun rufe gidan saboda bincike, sannan wasu aka bazasu neman Bilkisu a anguwar tako ina.


????innalillahi wa’inna ilaihirraji’un????????‍♀️.


_______
JAWAAD
_______


            Wani barcine mai daɗi ya sacesa take a wajen, gashi har lokacin ruwa ake zabgawa.
      Kamar kullum dai yauma dai mafarkinsa akan mahaifiyarsa yake, hakanne ya sakashi farkawa a firgice, sai da ya karanto addu’a kafin ya miƙe zaune sosai hannunsa dafe da kansa. 
     Barcin nasama bawani nisa yayba, dan bai wuce mintuna ashirinba.
     Dukda abinda ke nuƙurƙusar ransa bai barsa yay tasiriba tamkar yanda ya saba, miƙewa yay yanata sauke ajiyar zuciya a jere-jare, falonsa ya fito, inda ya hango kulolin abinci saman D/table, takawa yay ahankali zuwa garesu, dan ɗan barcin saiya saukar masa da kasala, ga kuma sanyin ruwa da garin ya ɗauka.
       Kulolin yabi ɗai-ɗai yana buɗewa, yay ɗan guntun murmushi a kasalance, dan kuwa abincin da yafi sone a rayuwarsa, wato Masa, tayi ƙyau suɓu-suɓu, ga miyar taushe mai tsafta da tasamu ingantacciyar dahuwa.
         Sauka yay ƙasa inda ya ɗakko filet dama duk abinda zai buƙata ya dawo.
       Yana zama a kujerar dani ɗin Shahudah na fitowa daga ɗakinta saboda motsinsa da taji.
      Duk da yasan itace sai yay biris ya cigaba da hidimar zuba masar sa, 
       Fuskarta da alamar damuwa taja kujera ta zauna kusa dashi gab, ta ɗora kanta jikin damtsen hannunsa ta kwantar tana lumshe idanu, tare da maƙalesa da hannayenta duka.
     Nanma bai motsaba, bai kuma kalleta ba, saima laumar masa da ya fara kaiwa bakinsa cikin zaƙuwa.
       Taunawa yakeyi a hankali yana wani luuu-luuu da idanu, ɗari bisa ɗari daɗinta yakai a yabama mai hidimar girkata.
      Shahudah ta ɗago kanta tana kallonsa da mamaki, sai faman ƙyaɓe baki take tana wani yamutse fuska saikace taga kashi, itafa sosai kyankyamin abincin gargajiyar nan takeyi lokuta da dama, ji wata irin miya dan ALLAH……
          “Wai dan ALLAH bb baka tsoron irin waɗanan abincin su sakaka yin nauyi da yawa?”.
      Banza yay mata kamar baijiba.
    Ta daki damtsen hannunsa kaɗan tana buga ƙafafu da turo baki cikin shagwaɓa.
      “Kai kaji tsiyarka riƙon masifa, ba nazo na baka haƙuri ba amma dan wula ƙanci ka kulle ƙofarka dan karna shigo”.
     Nanma ɗin banza yay mata.
     Tagumi tayi hannu biyu ta zuba masa idanu tana hawaye.
        Yi yay tamkar baisan tanaiba, yaci abincinsa yay nak, hannunsa ya wanke cikin ruwan daya ajiye, ya ciri tissue yana goge bakinsa da hannunsa. Duk dai Shahudah na kallonsa tana cigaba da kukanta.
      Miƙewa yay zai bar wajen ta miƙe itama a zafafe, sai ta faɗa bayansa ta zagayo hannayenta a cikinsa ta sakar masa kuka mai sauti.
            Cak ya tsaya bai motsaba, kusan mintuna biyu suna a haka, idonsa a lumshe yana sauraren sautin kukanta da saukar hawayenta a gadon bayansa.
      Hannu yasa ya cire nata dake akan cikinsa, ya tureta daga jikinsa yay gaba zai bar waje.
        Kuma kamo hannunsa tai da sauri tana fadin, “Haba bb, miyasa kakeson wulaƙantani ne? Kodan kaga inasonka da yawa haka? Nasan bakason a tara maka mutane a gida, amma nima ka dubi uzirina mana, kaji tausayin kaɗaicin da nake zama a ciki, ka hanani fita, dukda nasan ƴancinane na fita inda nakeso a lokacin da nakeso, amma nai haƙuri saboda kayi farin ciki, ya ka ke so na rayu dan ALLAH? ban saba da wannan rayuwar takuba, rayuwar ƴanci na taso a cik…….”
      Yanda ya juyo a zafafe ne ya saka bakin Shahudah rufewa akan dole.
      A tsawace tare da matsota kamar zai hadiyeta yace, “Ƴanci ko jahilci? Hudah ke wace irin daƙiƙiyace ne wai? Miyasa fitilar ƙwaƙwalwarki bata haska miki hanyar da zaki sanya ƙafa? Wlhy nayi nadamar aurenki, nadama irin wacce bama zan yafema kainaba, wawuya kawai mai koyi da toshewar basirar jahilai”.
           Shahudah dake tsaye tamkar wata gunki ta bisa da kallo harya shige ɗakinsa, duk da bagama fahimtar kalaman nasa tayiba sun girgizata, dan ita hausarma bakomai take ganewa a cikiba saboda ba yimusi akeba, ɗan dawowar tasun nanmane take ƙara fahimtar wasu abubuwan????????‍♀️(kaga turawa???????? ).
         Hawayen da suka sakko mata a farar fatarta ta goge, duk da kayan dake jikinta basu dace wani ya ganta da suba, haka ta fice daga sashen nasu, ga yayyafi har yanzu anayi ƙaɗan-kaɗan.
        Da gudu ta isa sashen tsohuwa Mama atika, (wato kakarta data haifi mamanta).


                 Zuciyar Jawaad a wuya take sosai, gaba ɗaya Shahudah ta sake ruguza masa dukkan farincikin da Ummansa ta bashi tare da ƴar uwarsa Batool.
       Haka yay shirin barci yanata sauke ajiyar zuciya, yanayin shafa’i da wutiri ya haye gado yay kwanciyarsa.
      Amma sai barcin yaƙi zuwa sam, haka yayta tunane-tunane har kusan ƙarfe uku, kafin barci ɓarawo ya sacesa.


        ★★★★★★

          Da safe haka ya tashi babu walwala, yana dawowa sallar asuba yay shiri ya fita wajen aiki batare da ya yarda kowa daga jama’ar gidan ya fito ya sameshi ba.

              Koda suka iso gimba ya buɗe masa motar ya fito.
       Da Qaseem ya fara cin karo, ya tara zaratan matasan ƴan sanda yana musu magana, da alama dai ya haɗa rundunane.
        Wani mugun murmushi yayma Jawaad yana kanne masa ido ɗaya. 
    Waishi a haukarsa ai ya karɓi damar da Jawaad ɗin ke takama da ita.
         Shima Jawaad ɗin murmushi yay masa, tare da sumbatar yatsun hannunsa biyu ya nunama Qaseem alamar saƙo.
      Saikuma abin ya soki zuciyar Qaseem, tuni fara’ar fuskarsa ta bace ya koma bin bayan Jawaad da wani mugun kallo.
      Baima san yanayiba, dan tuni Jawaad yama shige sashen da zai kaisa Office ɗinsa.
       Yana zama da saƙo yafara cin karo.
    Zumbur ya miƙe ya fice tamkar zai tashi sama dan rawar jiki.
            A ƙofar Office ɗinsa yaci karo da Qaseem Ali, kallon mamaki Jawaad ke binsa dashi, amma baice komaiba.
     Qaseem yay wata dariya yana watsa hannaye gefe, 
     “Yaya dai gwarzon ma’aikaci, yaya kaga wasan nawa? Ka shiga ruɗani ko? Aikin da kake takamar dashi an amshe cikin lokaci ƙankani an bani, nine zan jagorancesa yanzu, dama iyakar izzar taka kenan?”.
             Murmushi Jawaad yayi cikin ƙokarin katse Qaseem, buso iska yay daga bakinsa yana takowa cikin tsantsar takama da izzar jarumta irinta zaratan matasan da jini ke yawo ta kowace kafar jikinsu zuwa gaban Qaseem ɗin, ya dafa kafaɗarsa da hannu,
          “Na yarda kayi nasara my dear, ni kuma na faɗi, sai dai ina baka shawara akan ka kula kafin wani ya kula da kai, sannan ba’a cika baki da nasara kafin a nemota, nasara anan take Qaseem, (ya faɗa yana nuna saitin zuciyar Qaseem da ɗanyatsa), ina baka girma dalilin kaiɗin yayan matatane kuma ɗan uwana, sannan ogana a wajen aiki, karka bari zuciyata ta fara ƙoƙarin yin fito na fito da kai ko maida murtani. Nabarka lafiya, tare da fatan nasara jarumin ma’aikaci”.
      Ya ƙare maganar da salute ɗinsa, tare da zagayesa ya wuce.

            Harya shiga mota suka fice daga station ɗin Qaseem na tsaye kamar bishiyar giginya, zuciyarsa na tafarfasa da ƙuna, tare dajin tsanar Jawaad mai tananin gaske………………✍????

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button