KWARATA RETURN 10

Kuma da kikeji tanayin ƙara bawai itace da kanta takeyin motsin ba , kece zaki cire ƙyashi ganda hasda da baƙin cikin rayuwa kiyi tafiya da isarki. Tashi tayi tai tafiya lafiya lau , tace kinji kukan tane ? Nace a , a , tace an kallo ni ne ? A , a , wani yasan na wuce ? A , a , tou tsaya kiji sharrinta. Wata irin girgiza tayi tare da fara bada matakala. Wani irin kuka jigidar ta farayi coss׳. Sake tafiya tayi tace cakas² cas² , ta saman inda muke ta diro ƙasa cosssssssssssssss.. Cissssssss duk malaman dake kusa da inda muke a cikin aji saida suka leƙo. Dariya tayi tare da cewa ai da gayyarmu muke komai idan mutum yayi kuka muna da tsumman goge hawaye….. Aikinta ga maza ne bayan shekaru biyu take tashi daga aiki. Kyauta na baki wannan idan tayi miki kinji kina muradi saiki riƙa bada kuɗinki a siyo miki.
Zata fara bani labarin abinda ya haɗata da malamin dake cikin aji , da Alhajin da suke gidanshi aka aiko ana kiranta. Tashi tayi ta tafi ni kuma nabi jigidar nan da kallo. Tunani na farko daya zomin shine wasiyyar Inna , da tace kar inyi wani abunda mijina banyi shawara dashi ba. Shin da yaddar Dikko zan ɗaura ko kuwa da yaddar zuciyata….?
Har aka tashi makaranta ina tunani. Yau ba Dikko yazo ɗaukata ba Ashiru ne. Kuma dana koma gidan faɗa. Har an faɗa mishi abinda nayi a makaranta. Shi mutuwa zaiyi , ina zai saka kanshi , kinsamin ciwon zuciya sai na tafi na bar miki gidan nan , badai zaki barni in zauna lafiya ba ko ? Idan nayi miki faɗa kiyi zuciya dani kaza². Duk haƙurin dana bashi rufe idonshi yayi bai saurareni ba. Yaci gaba da masifa shi saiya haɗa kayanshi yanzu²n. Bazaki sake gani na ba sai kiyi duk iskancin da kika dama ? Kuma idan ya kama yarinyar nan sai ya kasheta…………. Tou shikenan kaje ka kasheta , kuma wallahi sai nayi kuka , wayyo………… Allahna na kurma wani irin ihu na nufi ɗaki da gudu. Jin ya daɗe bai shigo ba nasan yayi zuciya. Fitowa nayi har yanzu yana nan zaune a inda yake. Daga sama ban sauko ba nace ai sai ka tambayeni me nayi kuma shi malamin me yayi min ? Kawai anzo an karanta maka ƙarya da gaskiya ka hau ka zauna. Gani ina da hawan jinin masu juna biyu. A asibiti ance na rage yawan damuwa da ƙuntatuwa. Kullum saika ɓatamin rai ga ciki kuma , shin dakai da cikin duk sai kunsa na mutu. Idan kin mutum ko baccin rana nayi in huta da halinki. Ƙaramin yaro yafiki daɗin zama. Mtsww. Shigowar Abbakar palon yasa nayi shiru. Shima bawan Allah a bindige yake da ganin idonshi yaji bala’en mace. Dikko bai kalleshi ba nima kuma ban koma ba ina daga sama duk ina kallonsu.
Magana yayi ƙasa² , banji abinda yace ba saidai shi Dikkon yayi murmushi mai ciwo. Ƙara kasa kunnuwa nayi amma duk iyakar masifa ta banji abinda suke faɗa ba , saida suka gama ƙus²ɗinsu Abbakar ya fita. Yana fita Dikko ya fara faɗa. Wai ashe Abbakar shima ɗanyen kai ne mahaukacin banza baima san matarshi tafi wannan wayau ba ? Wai me yace ne ? Tsoki yayi sannan yace wai matarshi zai kawo kiyima nasiha. Nace mishi tou wallahi ya rufa ma kanshi asiri karma ya kuskura matarshi tasan hanyar gidan nan idan kuwa ba haka ba tou fa lallai zamanshi da ita ya ƙare. Fashewa nayi da kuka cewa wannan baƙar shedar kayi min kuma…….? Ƙarya nayi ? Yanzu ba tsayawa kikayi daga nan kinamin rashin kunya ba ? Na tambayeshi shin tana baka abinci ? Yace min ey , tana maka sannu da zuwa yace ey , tana wanka tana wanke ido tana gayu ? Ey. Rashin kunya take maka ne ? A , a , nace tou idan dai ba tauye haƙƙinka takeyi ba ka koma kaita haƙuri nima haƙuri nakeyi , nace mishi gaki nan rashin duka yasa kwana biyu kin warware.
Shiru nayi na juya mishi baya ina magana ƙasa². Tsoki ya sakeyi tare da cewa Allah dai yaso ban faɗa mishi haka ba , cewa nayi dai yayi haƙuri bance kema fama nake dake ba. Kawai dai haƙuri na bashi cewa mata ai lallaɓasu akeyi , ni abinda ya ban takaici wai ke kallon mai hankali yake miki , har yana tutiya zai kawo matarshi tayi koyi da halinki , baisan nima ƙurmusa min takaici kike ba , yadai kamata kisan abinda kike gashi nan har za’a fara baki gabata. Kace ya kawota in mata nasihar. Ki fara ma kanki sannan kiyi ma wani , yana faɗin haka ya fice daga palon…….
Mai gilashi daga inda aka kirata tana gama abinda take gidansu Sharifa ta wuce. Anan palon gyatimar Sharifa aka zazzage kolin rashin wayau. Daga uwar har ɗiyar dan ɗimuwar tunani Mai gilashi duk ta maidasu wasu lusarai…. Mama wallahi matarshi ce duk take ta shige da fice. Yadda yake san Sharifa kika ga gaba ɗaya ya ɗauke wuta tabbas wata irin gagarumar jifa ce , sai kunyi da gaske kun ƙara miƙewa dan wannan tarayyar da babu “yan al’adu ai nasan da tafiyar bata yuwu ba. Tayi maganar dan bugun cikinsu. Ai nan uwar Sharifa ta saki baki taita hawa gefen layi , ina shi Malamin naku ne Mama ? Sharifa dake full charge tace yai tahiya tayi maganar cikin muryar mashaya tana layi. Cikin faɗa na duniyanci Mai gilashi tace gaskiya Mama kuma da laifinku. Laifin meye nawa ni a ciki ? Saboda Allah Mama kuɗan ƙiyasta dihun kai da wayayyar rayuwa , maza fa yanzu idonsu kallon rana yakeyi , akwai wanda baya san mace ? Taya Sharifa zata riƙa zuwa zance da hijabi dan Allah ? Su wa’annan “yan duniyar ai bakya nuna musu hijabi ba domin wayayyar rayuwa zaki fahimtar dasu kin iya , cake take dan haka maganarta bata fita.
Mai gilashi tace da Allah rufewa mutane baki muyi magana da magabata. Shiru Sharifa tayi Mai gilashi taci gaba da cewa Mama ni ina da Malami acan Zandar aiki yake kamar yankan wuƙa , saidai shi aikinshi sai an ɗebo fitina zama ɗaya yake buga aiki fitina ta koma tayi bacci. Malamin shine kika ga ya ɗauremin ƙugu nake baza hajar iskancina kasuwa². Kuɗin mota dana aiki duk ni zan bayar idan buƙata ya biya saiki bani abu na. Mamar Sharifa tace wane irin malami ne sai an jawo fitina yake aiki ? Izzar aiki ake gaya miki Mama , su bala’en suke kwantarwa dan dai kawai su nuna muku jajircewar su a wurin iya aiki , kuyi shawara sannan ku taro bala’e ni zan tsotse muku duk dafin masifar bala’en. Miƙewa tayi ta jawo Sharifa suka fito waje. Wuri suka samu dan ɗan keɓancewa gefe tace ke jaka bakuzo kun daki matar Dikko ba , sautin maganar kaɗai ke fita amma bakajin maganarta. Mai gilashi tace idan kunga dama kuzo ku daketan , tana faɗi haka tayi gaba abunta.
Shegu masu wayan tsiya , na gano kuma kuna haɗawa da ɗan tsibbunku , fashewa Mai gilashi tayi da kuka tana tafe a mota tana cewa Allah ya tsinemiki albarka Sharifa. Kin cuci rayuwata ƙarshe na ɓuge ga zaman b q , wai me nayi miki ? Laifin nena aikata haka da ciwo a rayuwarki ? Me na tsare miki a duniya ? Haɗu barimi rabuwa idan kowa ya tuba shine kika bini kika daƙilemin tafiyar sa’ar rayuwata. Na rantse da girman Allah yadda kika hanani kema sai kin jibge a gidan mai gadi ko ɗan share²n filawowi. Shima malamin naku zan ganoshi duk sai watse a sarari kuma idan na tashi uwar watsi zan muku yadda za’ayi rabuwa ko gaisuwa babu tsakaninku dashi. Wayarta ta ɗauka ta kira Sultana. Saida ta gama karatun da zatayi ta kashe wayarta tana cewa ki auri D ‘ K in zan gani , dani dake dashi da ita matar tashi an watsa kifi abinci a ruwa……..