Uncategorized

MATAR UBA 23

Murmushin takaici tayi Tace ” Magana nake so muyi”

” Dawa? ”

” Dakai Mana”

A hankali yace “idan ina bukatar hakan ko? ”

“At least Hashim ka tashi Mana muyi Magana dan Allah, tun fa da na shigo kake kallon bango, ko kallo na bakayi ba”

“Bana bukatar ganin ki Diyya”

” Hashim me yasa kake da taurin Kaine Dan Allah? Yanzu kana nufin ka rabu dani Kenan?”

” Eh” kawai yace a takaice,

Zagayowa tayi ta zauna a bakin gadon tana kallon sa, hawayen da ta gani a idon sa ne yasa ta Fara kuka, Tace “Hashim Dan Allah Kar ka Mana haka, ya kamata kayi bincike Kan ka yanke hukunci a kaina”

Tashi yayi tsaye sa hannun said yayi a aljihun three quarter wandon sa ya juya Mata baya, Kana yace “wani bincike ya rage nayi? Bayan Ni Nan ganaune ba jiyau ba” Yana maganar Yana d’an bubbuga faffad’ar kirjinsa

Cikin shesshekar kuka Tace “Wallahi tallahi ba abinda kake tunani bane kawai…..” Juyo wa yayi a tsawace “kawai me? Nace kawaii me Diyya? Baki da abinda Zaki fad’a min, dama na dad’e ina zargin ki dashi Kuma kin tabbatar min da zargina”

Fashe wa tayi da kuka Mai sauti Tace ” am sorry please Hashim kana tsorata ni ban tab’a gannin ka acikin irin wannan halin ba,kayi hakuri ka yarda dani Dan Allah”

” In yadda dake Kika ce? Hmm” ya share hawayen dake fuskar sa kana ta d’aura da fad’in “Ta ina kike so Na yarda dake,idan da dagaske kike ai da tun a ranar zaki nemi muyi sulhu Amma Baki Zo ba,sai d’azu Zaki kirani,sai da muka d’auki two weeks”

” Nasan Kana fushi ne shiyasa na bari ka huce”

A tsawace yace ” To hell with you Diyya,I hate you”

Tashi tayi Tace “Karya kake Hashim you love me  Hashim and you’ll forever do” 

Murmushin gefen baki yayi ya d’aura hannayen sa a kunkunmin sa yace “Okay haka kikace?”

“Eh Haka nace,Kuma haka yake”

“Alright,get out of my room”

Yana Maganar Yana nuna Mata kofa

Cike da mamaki ta nuna kirjin ta Tace “Ni? I should get out?”

“Yes get out”

“Hashim Ni kake cewa na fita a d’akin ka?”

“Eh ke waye ce ke da ba zan ce ki fita ba? Kawai malama ki fice min daga d’aki”

Huci tayi Tace “Okay naji zan fita,Amma Hashim tell me one thing ya kake so muyi da su Daddy da mummy? Kasan cewa dawowar mu kawai ake tunda an Mana baiko”

“Wannan Kuma ke ta shafa ki fad’a wa iyayen ki cewar Ni Hashim Ahmad Shettima na janye Maganar auren dake tsakani na da ke”

Badiyya ganin Hashim dagaske yake tace “Kar kamin haka hashim,zaka sai  Mana dariya”

” Tunda ke baza ki fita ba Ni bara na fita bar Miki d’akin”

Wayar say ya d’auka ya nufi hanyar fita sai da yazo daf kofar yace “Idan kin gama ki rufe min kofar” yayi ficewar da, Badiyya bin bayan sa tayi da kallo ita gani take abin kamar Wasa Amma dagaske yake,zama tayi a bakin gado ta shiga kuka sai da tayi Mai isarta kana ta shiga toilet ta wanko fuskar ta, tana fitowa da fice daga d’akin ta rufe Masa kofar kamar yadda yace ta ajiye Masa makulli a inda yake ajiyewa.

Yana ganin fitowar ta yayi saurin d’aura waya a kunnen sa kamar Yana waya, kallon sa ta tsayi tafi minti biyar tana kallonsa,Hashim ganin zata iya Karya Mata zuciya hakan yasa yayi saurin barin gun, kad’a Kai tayi ta fice da ga compound d’in.

Yana ganin ta tafi ya koma d’akin,kwanciya yayi Yana jallony saman d’akin yana tunanin happy moments da sukayi spending da ita,tabbas Yana kaunar ta Amma bazai iya auranta ba.

Badiyya bata gaji da bibiyarsa ba,amma ganin wulakancin a yake Mata hakan yasa ta hakura,har suka kammala projects d’insu Bai bari sun hadu ba haka Kuma baya picking calls d’inta d’ga bisa ni yayi blocking d’in ta,ya goge duk wani abun da ya shade ta, number ne kad’ai ya bari Shima Kuma bai San dalilin da yasa ya kasa gogewa ba.

NIGERIA

A tsawace yace “Baka da hankali dama ban sani ba? Ni kake so ka kunyata a idon duniya Hashim?”

Kai a kasa yace “No  daddy ba haka  bane, babu yanda za’a yi na jawo maka abin kunya,Amma idan ka bari aka d’aura aure na da Badiyya shine abun kunya ba auren ta ba”

Zama Daddy yayi yace ” Me yasa kace haka,akwai wani abinda ya kamata na sani wanda ban sani ba?”

“Eh Daddy”

” Uhmn ina sauraron ka” Maida hankalin sa yayi don ya fahimci inda Maganar tasa ta dosa, bai rage komai ba haka Bai Kara komai ba, Mummy dake zaune tun d’azu akan sofa Tace “Kai Hashim kaji tsoron Allah ka fad’a mana gaskiya dukkanin mu mu mun San Badiyya yarinya ce mai tarbiya”

” Hakane Mummy amma Badiyya da kuka sani a baya dabance da ta yanzu”

Ta amsa da ” Allah ya kyauta”

Suka amsa da “Ameen”

Daddy yace “Tashi ka je zan duba na ga yanda za’a yi”

Yace “Toh Daddy na gode”

Ya tashi ya fice.

Daddy Maida kallon sa yayi ga Mummy yace “Amina,ya kike ganin zamu b’ullowa al’amarin yaran nan,wallahi kaina ya kulle”

” Nima haka Alhaji,to Amma ya zamuyi yaron Nan dai shi ga yarinyar Nan yace Yana so,Kuma yanzu yace ya fasa bai kamata mu sa shi yin abinda baya so ba”

“Okay idan ma fahimce ki,so kike na janye Maganar auren sa da Badiyya Kar ki manta fa, Mahaifin yarinyar Nan amini na ne fa,idan na Masa haka ai ban kyauta Masa ba”

” Hakane Alhaji,Amma ya kamata ka Sani yaran yanzu ka haife sune Amma baka haifi halinsu ba,tunda yace baya so a janye Maganar Kar Kuma a Zo Ana da na sani”

“Kai Amma banji Dadi ba ko kad’an yanzu ban San yanda zan tin Kari Alhaji Usman ba”

” Ka kwantar da hankali Alhaji,yanzu tunda dama jiran su Hashim ake a had’a auren su day Fadeelah ina ga kawai gara a Sanar dasu ayi bikin Nan Nan da wata d’aya”

“Toh Shikenan zan duba na gani”

Tashi yayi yace “bari na watsa ruwa idan yaso zan nemi shi Mahaifin Suraj d’in in yaso zanje har gida na Sami Usman muyi Magana ta fahimta don wannan ba Maganar waya bace”

“To alhaji a fito lafiya,kamun Nan bara na kawo maka abinci”

“A a hajiya bar abincin Nan duk ina ji ba Ni da appetite”

“Toh Shikenan yanda kake so hakan za’ayi.”

Bayan ya fito Kai tsaye ya zarce gidan su Badiyya, ya Sanar da mahifin ta Akan cewar Hashim ya janye Maganar auren yarsa, sannnan ya bashi hakuri, Alhaji Usman mutum ne Mai hakuri sannan ya d’auki hakan a matsayin kaddarar Badiyya, ya Kuma Masa alkawarin hakan bazai shafi abotar su ba,yayi Masa godiya ya tashi ya koma gida,ya sanar da mummy yanda sukayi jikinta yayi sanyi matuka.

Tace “banji dadin abin Nan ba Sam,Nima insha Allah gobe da safe zanji Ni gidan nasu na bawa mahaifiyar ta hakuri, yanzun ma don dare yayi ne da naje”

” Sai Kuma kiyi,duk laifin kine duk kin bi kin sangarta yaro”

Yana kai Nan ya haura sama sai surutai yake ya na d’aga hannu.

Mummy Tace “Oh ‘ya ‘yan kuka mai jawo wa uwar sa jifa,Allah shi kyauta” sai ji tayi yace “Ameen” ba tayi tunanin yaji ba hakan yasa tayi ficewa daga part d’in say ta koma part d’inta, hashim ta tarar a parlor a kishingide kana ganin sa kasan Yana cikin damuwa,cewa tayi “Damuwa ko? Baka ga komai ba tukanna”

“Haba mummy ya kuma Zaki ce haka?”

“Me kake so Na ce maka Hashim? Tunda burinka shine kaci mutuncin Mahaifin ka,to yaje gidan su Badiyya an janye auren hankalin ka ya kwanta?”

Ji yayi kirjin sa na duka uku uku, wani hawaye ne masu zafi suka Fara zubowa daga idanunsa yace “an janye?”

Ta amsa da “Eh hankalin ka ya kwanta ko? Mu Kuma ka tada Mana namu”

Jin shesshekar kukan sa yasa tayi saurin kallon sa Tace “Hashim!!! Kuka?”

Baice Mata komai ba, tayi saurin karasowa inda yake ta dafa shi a kafad’a Tace “Hashim ya kuma Naga kana kuka ba Kai kace baka son auren ba?”

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button