MATAR UBA 23

Ya d’aga Mata Kai alamun eh, Tace “To Kai da ya kamata kayi farin ciki Mai yasa kake kuka?”
“mummy ina fa sonta”
” And so? Kuma kace baka sonta, Wai me yake faruwane?”
Kwantar da kansa yayi a kafad’ar ta, yayin da ita Kuma take d’an bubbuga Masa baya, a dai dai Nan Daddy ya shigo yace “Ga irinta Nan ai kina Nan kina lalata yaro”
“Amma Alhaji baka ga halin da yake ciki bane?”
” To sai me ya mutu Mana, mtsww Dan Allah ki d’auko min chaja na ki kawo min d’aki yanzun Nan”
Ya yi ficewar sa.
Daddy yayi fushi sosai, don dakyar yake amsa Masa gaisuwa Amma hakan Bai Hana Hashim basa hakuri ba, daga bisani ya huce.
An d’aura auren Fadeelah da Suraj cikin farin ciki da kaunar juna.
BAYAN SHEKARA ‘DAYA
mummy na zaune a parlor tana kallon News kwasam taga Ana sanarwa jirgi yayi hatsari from Dubai to Nigeria, aciki harda wannan shahararren Dan kasuwa Mai suna Alhj Ahmad Shettima, mummy hannu ta sa a Kai ta saki Kara a gun ta yanke jiki ta fad’i.
Hashim da already yaji Labarin mutuwar Mahaifin Nasa yayi saurin dawowa gida daga gidan su faisal, shigowar sa Kenan yaji news din da take ji, Kan ya nufi ta harta yanke jiki ta fad’i.
????????????????????????????????
Please Vote and comment
[ad_2]