NOOR ALHAYAT 81-90

“Sorry I didn’t tell you shi yayi accompanying din mu jiya, coz Shureim was sick” Ya langwabar da kai yace “Da gaske?” Bata ce komai ba, ya d’an yi murmushi
shi ma bai ce komai ba, tayi breaking silence din tace “We where very close da baby, farkon xuwa na gidan su ne kadai muka samu problem, after that she was
kind to me, she took me just as her sister, tana so na sosai, nima kuma ina sonta, and I really want us to be frnds now tunda bani da kawaye” a sanyaye ta
kare maganar, Yana gyada kai yace “That’s nyc then…” Tace “Me yasa baka xo da little Amira ba?” Yace “Ba daga gida nake ba” Khadijah tace “Ohk, Toh ko
ruwa ban kawo maka ba, shud I bring some?” yace “Daga eatry fa nake yanxu haka” ta d’an buda ido tace “Kai da xaka koma gida kuma meye na xuwa eatry da
daddare Barrister” murmushi yayi yana shafa beard dinsa bai ce komai ba, can yace “Shureim fa?” Shiru ta d’an yi, ta dago tana kallonsa tace “Yayi bacci” ya
wara ido yace “So early? duk da nasan ba gaskiya kika fada ba” xaro ido tayi tana kallonsa, yayi murmushin sa mai kyau yace “Yea, sai ki ce min Aliyu ya
tafi da shi” da mamaki tace “How did you knw” yana murmushi har sannan yace “From ur facial expression, and don’t forget my field….” Yar dariya tayi tace
“Kai My Barrister” yace “Sure My Meerah” ta boye fuskarta a tafin hannunta tace “Gobe ai xai dawo in sha Allah” yace “Alryt then, bari in tafi Amira, gobe
xan dawo mu yi hira sosai am exhausted gaba daya yau” tace “Ayya, kana komawa gida kayi wanka ka kwanta you will feel relieve” Yana murmushi yace “Toh
Amaryata” juya masa baya tayi tace “Uhn ni dai bana so” a hankali yace “Xa ki so ne ma ai” Bude motarsa yayi ya dauko leda ya dawo gabanta yana kallonta ya
mika mata yace “Though Shureim na kawo ma amma tunda kin min rowar ganinsa gashi sai ke da meye ma kika ce sunanta…” Khadijah tayi murmushi tace “Sunan mu
daya, Amma baby ake ce mata ita” ya wara ido yace “Ashe Mami na ce ita ma” a hankali khadijah ta gyada masa kai, yace “Toh ina gaisheta specially, she’s
having a great name, and naga suna kama da yayan nata ma” Khadijah ta amshi ledan tace “Toh xata ji mun gode sosai” murya can kasa yace “Noo thanks
sweetheart” sunkuyar da kanta tayi, yace “Gobe xan kawo maki IV in case you have people to give” tace “Toh Allah ya kai mu” yace “Ameen dear, let me get
going” daga haka ya bude maxaunin driver ya shiga, ta koma baya tana kallonsa, sai da yayi reverse ta daga masa hannu ya sakar mata murmushi sannan ya ja
motar ya wuce, juyawa tayi a hankali ta koma cikin gida. Washegari karfe goma baby tace xata koma gida, duk khadijah ta ji ba dadi, babu yanda bata yi da
ita ta bari sai da yamma ba tace inaa ita lokacin xata wuce, Khadijah tace “Toh ki kira yayanki ya dawo min da yarona nima” dariya sosai baby tayi tace “Sai
kace baki da number sa, ke ki kirasa mana” Khadijah ta dau wayarta ta shiga kiran Aliyu, yana dagawa tace “Ka dawo min da yarona tunda wucewa baby ma xata
yi yanxu” yace “Koh?” Tace “Eh mana, nace ta bari sai da yamma ta ki” kamar xata yi kuka ta kare maganar, Aliyu yayi murmushi a hankali yace “Toh bata
wayar” Mika ma Baby wayar tayi, baby ta amsa tana dariya ta kai kunne yace “Baby ki bari da yamma” tace “Toh yayanmu an gama” daga haka ta ba khadijah
wayarta, kashewa khadijah tayi tana murmushi tace “Me yace?” Baby ta harareta tace “Ba don halin ki ba xan kai yamma” sosai khadijah taji dadi tace “Yauwa
ko ke fa, kinga kafin nan Barrister ya kawo katin da yace sai in baki ki kai ma su Mumy” shiru baby tayi tana kallonta, khadijah ta wara ido tace “Ko bai yi
ba hakan?” A hankali Baby tace “Ke dai ki kai da kan ki xai fi” Khadijah tace “Toh shkkn ko ran Friday sai Sudais din ya kai ni in kai” Baby tace “Khadijah
Ina son maki wani magana amma Allah yasa baxai bata maki rai ba” Khadijah na kallonta tace “Ina ji baby” Baby ta kamo hannunta tayi kasa da murya cikin
sanyi tace “Khadijah me yasa kika ki amincewa Ya Aliyu ya aure ki bayan ya nuna yana son yin haka, kin ga akwai advantage din hakan biyu xuwa uku, na farko
shureim… Idan yau ace Ya Aliyu xaki aura har duniya ta tashi ba lallai yaron yasan irin kaddarar da ta afka maku ba da yanda aka yi aka samesa sai in ku
kuka fada masa, he will neva ever know wllh, idan wani gidan kika yi aure fa? Wllh komin daren dadewa watarana sai ya sani, sai ya san matsayinsa khadijah,
na biyu Aliyu baxai taba maki gori a rayuwa ba idan ma yayi wlh yasan kansa yayi ma, kunya a kansa, balle ma wllh baxai yi ma don yasan shi ya cuce ki,
sannan kin ga babu wani matsala da xaki samu gun Mumy, da mu yan uwansa, Anty khadijah ce problem dama, toh tana can har yanxu asibiti sai karaya ya dauko
warkewa abu ya dawo baya, ga cikin shege jikinta har ya fito, don haka ta kanta take yanxu, kowa yaje sai tace ya yafe mata har masu gadi da driver… toh
wanda xa ki aura fa khadijah? Though nasan Barrister yasan everything about you amma khadijah ki kyale namiji wllh ko ba directly ba watarana sai ya maki
gorin nan barin ma wannan da kika ce yana da mata, ko cikin bacin rai wataran sai ya jefe ki da bakar magana irin ta gori ba tare da kilan yasan yayi hakan
ba, kawai ta dalilin bacin rai, balle a je ga yan uwansa da relatives, sannan uwa uba matarsa, yanxu duniyar da wuya wllh a rike maka sirrin ka, khadijah ki
duba wannan xancen nawa plss ba wai don ina son ki da yayana bane amma it’s better ku rufa ma kan ku asiri ku hadu ku rike sirrin ku, kin ga sai ki kara
haifo mana wasu kyawawan yan biyun……” Da xolaya ta kare xancen, Khadijah dake ta kallon kofa ta xame hannunta daga nata a hankali tace “I really like
you baby, Ina ji da ke har raina saboda kin min halaccin da baxan taba mancewa da ke ba, plss baby kada ki sa in fara jin haushin ki in ga kamar ke ba
masoyiyata bace, baby mu bar wannan xancen plss bana so, Kuma kar ki sake min irinsa” A hankali baby tace “Toh Allah ya baki hakuri” Khadijah tace “Ameen,
So baki gaya min level da kike ba yanxu, Kuma yaushe xa mu sha naki bikin?” Da murmushi ta kare maganar tana kallonta. Bayan la’asar Sudais ya kira Khadijah
yace yana waje, da kyar ta lallaba baby da har ta kira Aliyu ya xo ya dauketa ta gama shiryawa suka fita waje gun sa, yau ma yana tsaye jikin motar suka
fito, Baby ce ta fara gaishesa ya amsa da fara’a yace “Lafiya lau Mamina ashe baki koma ba” Baby tace “Ehh wllh ina jiran yayana ne” Sudais yace “Alryt, ya
gidan” tace “Lafiya lau” Kallon Khadijah yayi yace “Ya aka yi Madam?” Tayi murmushi tace “Lafiya lau, ya aiki?” Yace “Alhmdllh… Ya Ummar mu” khadijah tace
“Tana ciki” juyawa Baby tayi tace “Toh sai anjima xan shiga ciki” yace “Alryt nagode da gaisuwa” daga haka ta wuce ciki, Sudais ya bude motar ya fiddo
invitation card ya mika mata yace “Here dear” amsa tayi tace “Nagode, Ina Amira fa” yace “Tana gida” mota ce tayi parking kusa da na Sudais khadijah ta
dinga kallon motar har Aliyu ya fito, Shureim ma ya fito ta daya side din, da gudu ya taho ya rungume Sudais yace “Unclee…” Sudais ya daga sa sama yana
pecking goshin sa yace “Evening son, where are you coming from?” Ya wara ido yace “From my kind Mama’s home” Sudais yace “That’s good” karasowa Aliyu yayi