RAUDHA Page 41 to 50

Be dena kallon ta ba, har sanda ta ɓace wa ganin sa, sai kawai ya saki numfashi da sauri da sauri, kasancewar tun tozali da ita da yayi ya ɗauke numfashin nasa, be taɓa ganin yarinyan da ta tafi da imanin sa kamar wannan ba, duk kuwa da cewa ya ga ƴan mata bila adadin waɗanda suka fi ta kyau da komi, amma shi dai wannan ɗin ta daban ce a wajen sa. Yana tsaye ya kasa motsawa a wajen har sai da good 5 minutes ta shuɗe, sannan a hankali ya taka ya bar wajen yana sake rufe fuskar sa da hulan kansa, inda ya ga tabi nan yabi amma kuma ko me kama da ita be gani ba, hakan yasa ya nufi wajen ƴan Taxi ya hau ɗaya suka bar wajen.
????????????
*RAUDHA* na fita wajen airport ɗin, ta hangi Yayan ta mafi soyuwa a birnin zuciyar ta, da sauri ta ƙarisa wajen sa sai ji yayi an rungume sa
Wani irin farin ciki ya sake kama sa ganin ƙanwar ta sa rungume da shi, ai nan da nan shima ya rungume ta yana me sake nuna farin cikin ganin ta
Ita kuwa sai faɗin “I Miss You so Much Yaya”. Take yi, bakin ta ya ƙi rufuwa sabida tsaban murna
Ɗago kanta tayi tana kallon sa, cike da washe haƙora tace, “Yaya ina Daddy be zo ba?”
“Baby Daddy yana gida, Ni kaɗai na zo ɗaukan ki”. Suhaib yayi maganar yana shafa kanta shima bakin sa har kunne
Har zata yi magana sai wasu maza biyu masu uniform a jikin su, suka ƙariso mata da Trollys ɗin ta da tasaka su ɗauko mata
Ganin su da akwatin sai Suhaib ya je ya buɗe musu Boot suka saka mishi, sannan ya biya su suka bar wajen, shi kuma ya buɗe mata gaban motan ta shiga, ya zaga ya shiga suka bar wajen.
A cikin mota surutu RAUDHA ta dinga yin masa yana biye mata, tamkar ba ita ba domin ta sauya sosai fiye da da, duk da a yanzu ɗin ba ta yawan surutu ga kowa idan ba da su ɗin ba, har yanzu halin ta na nan na rashin sabo da mutane
Shekaru huɗu kenan ta shafe a ƙasar Madina, abubuwa da dama sun sauya a tattare da ita, duk wani halin ta mara sa kyau ta dena gaba ɗaya, tunda ta je karatu kawai ta saka a gaba, bata da aiki sai karatu sai research akan addinin ta, kafin ta shiga makarantar islamiyya sai da ta shafe kusan shekara da zuwan ta, a time ɗin ta gama sanin wasu abubuwa sosai a addinin ta, sannan daga baya ta shiga islamiyya, makarantun da ta shiga guda biyu ne duk islamiyya, idan ta je boko ta dawo sai ta wuce can wani Islamic school, sai dare take koma wa gida, da weekend ma school ɗin da take zuwa daban ne, babu nisa da inda take zaune
Lokaci ƙanƙani RAUDHA ta gama sanin komi sabida ta saka abun a ranta, dama ga ta da ƙwaƙwalwa, a lokaci ƙanƙani tayi suna sosai a ko wani school da take yi, musamman ma boko.
Su Daddy suna kawo mata ziyara akai-akai, kuma sun ji daɗin yanda take mayar da hankali fiye da tunanin su
Kankace me harshen ta ya gama juye wa irin na larabawa, larabci a bakin ta kamar ruwa, sosai take son harshen shiyasa duk abinda zata yi, tafi son tayi magana da harshen larabci akan ko wani yare, sabida school ɗin da take yi ana karatu ne da English and Arabic
Sometime tana tambayan su Daddy idan suka zo mata ziyara, akan su taho mata da Ramcy, sosai take kewar ta, yawan tambayan ta da take yi ne, Daddy har ya yanke shawarar tambayan mahaifin ta, idan har zai bar ta taci gaba da school, shi kuma zai biya mata makaranta ta koma can wajen RAUDHA ɗin, amma kuma sai Baban Ramcy yace be yarda ba, shi ba ya son ɗiyar sa tayi nesa da shi, hakan ya sa Daddy ya yanke shawaran biyan mata taci gaba anan A.B.U Zaria, kuma akayi Sa’a Baban ta ya amince. Sau uku tana zuwa kai wa RAUDHA ziyara, wani lokacin idan Suhaib zai je sai ta bi shi, wani lokacin kuma Daddy ke tafiya da ita. Itama dai taci gaba da school ɗin ta anan kamar yanda Daddy ya alƙawurta zata yi, yanzu haka kusan watanni bakwai da gamawar ta, har an saka mata rana yanzu saura wata ɗaya bikin ta.
????????????
Suhaib na yin parcking motan, RAUDHA ta buɗe ta fito, cike da zumuɗi ta nufi hanyar cikin gidan
Suhaib na mata dariya yana faɗin “baza ta jira sa ba ta tafi?” Amma ina ba ma taji sa ba, burin ta kawai ta isa ciki ta haɗu da Daddyn ta
A hanya duk ta gama gaisa wa da wasu daga cikin ma”aikatan gidan. Suna mata murnan kammala karatu, ta amsa su cike da farin ciki. Su kansu sun yi mamakin sanja war RAUDHA. Bata bi ta kansu ba ta shige da gudun ta da ya zame mata jiki
Ai kuwa Daddy na zaune a parlour’n ƙasa, yana ganin ta ya miƙe yana mata waƙa yana dariya
Da gudu ta ƙarisa gare sa ta rungume sa tana faɗin, “Daddy na Ni kaɗai! Daddy na da yafi na kowa”.
Still dariya yake yi yana cewa, “na’am my dear daughter, Ina miki murnan kammala school ɗin ki lafiya, Allah ya miki albarka”.
“Ameen Daddy”. Ta amsa shi tana sakar mishi peck a kumatu kamar yanda larabawa suke yi, bakin ta a washe
Time ɗin ne Suhaib ya shigo, bayan sa ma’aikata suna jaye da akwatunan ta, ajiye wa suka yi suka bar wajen, yayinda su kuma suka zauna akan sofa suna ƙara gaisa wa tare da tambayan ta school da inda ta baro
Nan ta washe baki tana ta zuba musu surutu tamkar an kunna rediyo, gaba ɗaya ta haɗa su ta matse idan ta rungume wannan sai ta rungume wancan, tana faɗa musu missing ɗin da tayi nasu, tana tsakiyan su ne tana zaune
Su kuma bakin su ya ƙi rufuwa saboda murna, sai biye mata suke yi, sai da aka kira sallan magriba sannan ta tashi ta nufi ɗakin ta, su kuma suka wuce masallaci.
Tana shiga wanka ta soma yi, komi tana yin sa ne cike da kewa, sai rera waƙan “i miss You home” take yi. Sallah ta soma gabatar wa wanda ake bin ta, sannan ta ɗaura da magriba, ta saka riga da wando ma su santsi da kwalliya ta fito
A Parlour ta tarar da su zaune suna jiran ta, tana fito wa Daddy ya ce, “su hau kan dainning su ci abinci”
Zama suka yi suka ci abincin, sannan suka koma Parlour tana ta ba su labaran da ya ƙi ya ƙare, sai kuma daga baya ta soma raba musu tsaraban da tayi musu, har da nasu Farida da yaran ta biyu, Haneep da Abdullahi da ta haifa kusan shekara biyu da rabi, suna kiran sa da Abdul kasancewar sunan mahaifin Farida ne, yanzu yaran sun ta so kansu ɗaya ne tamkar ƴan biyu, har Abdul ya fi Haneep wayau yanzu sabida halin laluran da yake fama da shi, Suhaib be taho da su bane sabida akwai school na yaran, zuwa gobe weekend za su zo, ranan Lahadi kuma su koma gaba ɗaya har Suhaib ɗin.
Anan suka shantake har kusan ƙarfe 11:30pm. Kafin suka je suka kwanta.
Washe gari da wuri sai ga Ramcy ta bugo musu sammako, kasancewar har yanzu RAUDHA akwai ta da son huta wa, shiyasa idan ta kwanta tana kai wa 11:00am bata tashi a barci ba, idan har ba Lectures take da shi ba to tana wuni ne a kwance da safe, sai da rana zuwa da dare wannan kuma time ɗin karatu ne, ya rigada ya zame mata jiki har yanzu bata fasa ba.
Ramcy bayan ta gaisa da su Daddy sai ta wuce ɗakin RAUDHAN, anan ta ganta shame-shame tana barci, zama tayi ta soma tashin ta
Koda RAUDHA ta tashi, ganin Ramcy a gaban ta, ai da sauri ta rungume ta suna murnan ganin juna, ko wacce cikin su cike da kewar ƴar uwan ta, har da ƙwalla suka share
RAUDHA tace, “ana haƙƙan ishtaƙtu laki ya jamilaty”.
Dariya Ramcy tayi tace, “Besty kin manta ne, nan fa ba Madina bane”.
“Ya Salam naseetu wlh, ana asif”.