NOVELSUncategorized

RUWAN JAKARA 3

*BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION*                  
( _pens of freedom, home of exceptional and magnificent writers_) 







                *RUWAN JAKARA*………….    
    { _idan baa sha abirni ba asha akauye_)} 




                *~LITTAFIN~*???????? 

*MARYAM HAMISU YUSUF (maman boy*) 





~TRUE LIFE STORY~






“`Page“` *3*





_Kwana biyunannan dakukajini shiru… Bikine yasha kaina.. Amma yanzu typing ba kama hannun yaro insha Allah_


Lumshe mayun idanunsa  anwar yayi  da suka cika da jaraba ya waresu akaina…. “Lafiya pretty ” ya ambaci sunana cikin wata irin sarkakkiyar muryarsa data fara shaking 


Ban iya basa amsa ba dasauri na raba sa na bar falon
Musamman dana fahimci gab hannunsa yake da taba jikina… Duk illahirin jikina rawa yakeyi… 


Lumshe rinannun idanunsa anwar yayi tare da biting lips dinsa…. Lokaci guda ya cakuda sumar kansa da hannayena biyu…  idanunsa suka kada sun soma sauya Kala  Wani irin azabar feelings ke bijiromasa..tare da fizgarsa.. Babu abinda yake bukata illah kadaita da mace wannan lokacin.. Ganin zarah da irin kallon kurillan dayakeyimata ya gano sirrin hallitarta duk da katon hijabin data suturta jiknta dashi……  
Dasauri ya fito compound din gidan.. Alokacin har na dfce da Ga gidan… Nacin anwar bai kyaleni ba saida ya hau motarsa kkrar black toyota Camry ya biyo bayana…. 
Ina fita daga gidan nasaki wata Yar karamar ajiyar zuciya, domin Kuwa nasan anwar da akuyancinsa bunsurune na bugawa ajarida… Duk da dai nasan yafi karfin yace ya nemeni… Domin duk tantaramcinsa da masu class yakeyi…. 
Nidai atsorace nake tafiyakawai nake Ina neman Allah yayimin tsari daga dukkan abinki… Nikam yau umma tajamin… Tun kafin nagirma rabona da gidan…. Sai yau.. Danko sallama banyi da, mutanen gidanba
Ji nayi Ana min horn tabayana… Ai Tun kafin na juya naga waye cikinsa ya juya..
Fito da manyan idanuna  nayi arazane Dana fahimci anwar yafara bina…. Nashiga uku na furta afili arazane Wanda hakan yayi dai² da fitowar wani mai adai² ta afirgice natsayar dashi na shige bat are da na fadamasa inda zai kaini ba.    Waige² kawai nakeyi.. Bansamu kwanciyar hankaIi ba.. Saida na tabbatar na daina gamin KO da kaIar motar anwar ce. .. Lumshe idanuna kawai nayi
Sai alokacin nasamu Damar sanarwa dan adai²tar bayanin inda zai kaini…. 

Ina isa gidan umma na dirowa. Itama.. 
Ina dakina ina nazarin litattafaina umamh ta hankado labulen dakin KO sallama babu…. Dayake akwance nake shigowarta yasa na yunkura inayimata sannu da zuwa…. 
“Baibaki Komai bane shi alhaji mansoor din? “…. 
Ta jefomin tambayar amaimakon amsa sannun da nayimata…. 
Sunkuyar  dakaina nayi nasoma yimatabayani “ummah basusan tafowa taba… Wlh umma halin ya, anwar ya baro dani gidan… Jikina fa yafara kokarin ta6awa….. “
Ai bankarasa maganarba.. Ta bugemin bakina da ya tilastamin yin shiru na date bakina ina hawaye…. 
Tana huci take magana “ke kau kinji haushin rayuwarki batula.. Wannan gadon bakin ciki na bakin halin  mahaifinki da kikayi bakiji dadinshiba…domin mahaifinki  tun yanada rai idan akwai abinda ya tsana yaga ina cigaba har yabar duniya bakin cikiyakemin….. 
Fashewa nayi da kuma ina shafa lips dina danakejin sun soma kumbura sakamakon bugun da ummah takaima bakina “umma kiyi hkr dan Allah.. Amma ummah wlh badai dai bane ya anwar ba muharramina baneba… “… Na idar da maganr kuka na sarkeni
Huci kawai umma keyi kafin tanunani da yatsa “ai wlh bakincikinki ke zai ci.. Kuma kema zakiji ajikinki bazakici abincin da re ba dan kuwa ban memo dakeba… “
Ta fada tare da ficewa kamar kububuwa.. Kifar dakaina nayi ina kuka ba, abincin data hanani bane yasakani kuka ba… Illah halayenta data gagara sauyawa…. Tashi nayi na wanko fuskata na zira hijab dina dazummar tafiya gidan ma man abbah kamar yadda nayimata alkawari….

Kicibus nayi da gwaggo kwazo Tana shara.. Da dukkan alamu taji duk kwakwazon da ummah keyi…. 
Kiran sunana tayi tare da nufo inda nake “uwar dakina kici gaba da hakuri da halin mahaifiyarki.. Nasan kinayimata tsananin biyayya karki daina har lokacin da Allah zai kawomiki miji ku rabo lafiya kinji kije Ki dawo abinda kike so  zan girka wato dambu”… 
Murmishi nayi tare da fadan “gwaggo Ngd Ki jirani na, dawo yanzu sai muyi aikin atare “… 
Dariya kawai tayi tare da min adawo lafiya…. 
Ahankali nakejin zuciyata na sanyi har na isa gidan ma man abbah…. Anan fa naga karramah Komai saida takawomin… Saidai bazan iyacin Komai ba saboda inason cin dambun gwaggo kwazo mai dadi… Lemu kawai na kurba na ajiye danni ba mai yawan cin abinci bace… 
Atake tafara zayyanomin damuwarta game da mijjnta, da uwar mijjnta, “Sam jamilu yadaina kulani zarah.. Baya kusantar duk wani abu dayake da kusanci dani.. Idan nayi girki byaci… Ga sharrin mahaifiyarsa da kanwarsa kullum Kara yawa yakeyi. malama fadima kibani shawara.. Da ingantattun Addo in dazan dingayin Allah yajuyomin da hankalin mijina… 
Taidar da maganar Tana sharar kwallah…. 
Zuba mata idanu nayi na tausayawa ma man abbah domin matar batada matsala dakowa…. 
Cikin sanyin murya nasoma magana “kiyi hakuri maman abbah bakomai ne ke dawwama ba jindadi KO akasinta… AbubUwa dayawa zasu zama tarihi…. Amma Ki yawaita istigfari domin yana Kara kusantar bawa da ubangijinsa sannan kuma kowace sallah idan kingama Ki dinga karanta wallahu galibun ala amrihi kafa 41.. Da sannu Allah zai kawomiki daukinsa.. Ita addua bata faduwa kasa…. 
Tunda na fara magana takafeni da idanu Tana share kwallanl… 
Kamo hannayena tayi “nagode malama zanyi amfani da shawarwarinki… Wlh zarah duk sallar dazanyi sainayi addua Allah ya bani ya datakeda koda rabin iliminkine da nutsuwar da kaifin harsher wajen iya tsara zance.. Wlh mahaifiyarki tayi farar haihuwa… Saura gwarzon namiji mai saa dazai  daukeki…. 
Murmishi kawai nayi…. Ina, sunkuyar da kaina… Sai bayan sallar asar na baro gidan ta cikani da kayak arziki da humrori masu kamshi da, kayak kwalliya…. 
Ina isa gida umma harta kuma ficewa… Saida Muka gama dambun shinkafar hausa da yaji kayan lambu nida gwaggo kwazo… Muna ci muna fira Tana bani labarai Na su na mutanen da nikuma ina aikin dariya harsaida nayi dam.. 
Wanka nayo domin tunbayan sallar issha nakejiran zuwan malam kamal.. Na shirya cikin wani leshi wanda jikar gwaggo kwazo ta bani shi.. Banyi make up ba na zira hijab dina nakwanta tare da lumshe idanuna ina tilawar hardata ta alkur’ani mai girma.. Hayaniya nasoma juyowa sama² hakan ya tilastamin ware idanuna tare da fitowa daga dakin… Ya faruq nagani tare da umma dtashigo ynxu sai yaran unguwa da matar makwabcinmu malam mustapha wait ya faruq shine ya sacemata akuyoyinta…. Masifa akeyi agidannan ummah ta kafe Tana tarewa ya faruq duk da tasan shidin banda gaskiya… Jingina nayi akofar dakina kasancewar jiri danaji na diba na innalillahi nake karantowa sauba adadi…. Hakan yasanya kwallar data faru a idona kin zubowa….. 
Zuwan mijin gwaggo kwazo ne ya lallaba matar ta tafi dan Ana ganin kimarsa a unguwar… Yakuma kora yaran dasuka taru agidan sunayiwa ummah da ya faruq ihu….. 
Fashewa nayi da kuka na durkushe anan… Wata uwar harara umma taballomin “wahalalliya ahaka idanunki zasu kafe indai akan wadanna tambadaddun yayyunnaki ne…. “

“Aah  hajara ba ayiwa yaya haka. Aisai su ida lalacewa.. Addua zakiyi Allah yashirya “… 

“Wlh gwagoo kwazo bazan bata loakciba wurin yeah was faruq addua ba shi dai ba yaro bane….. “

“Ance malama zarah tazo”…. 
Sallamr yaron takatse musu maganr su… 
Waye yake kiranta kuma akan mashin yake ko akafa KO kuwa amota yake?…… 



Maman boy

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button