NOVELSUncategorized

YAR SADAKA 5&6

???????? *’YAR SADAKA..*????????


*STORY & WRITING BY…*
         *BY*
*MOMN SULTAN*


*DEDICATED TO…..*
*MMN AMATULLAH*


*SPECIAL GIFT TO…*
*MMN FAREESAH*




5⃣&6⃣



Kaka na tafi,,adawo lafiya,,Banda tsokala ki Kuma dawo da wuri,,kaka Kenan kinfasan Bana dadewa Amma kullum sekin gayamin saikace yarinya..
Baki yakumbo ta riqe tana kallan yadda nijlah ta tafi tana Taku daidai,kai kace wata babban budurwace!

Yakumbo Bata qara Magana ba nijlah ta fita tana Mita,,haka haka ta batamin lokaci gashi ‘yar biyar din ma Bata Bani ba,, murmushi ta saki tare da fari da manyan idanunta tace,,nasan iro Yana dandali Yana jirana, tafiya nijlah take tana tinani harta qarasa dandali,,tin Daga nesa tafara Jin qaran sautin gangan danladi me gidan kagane Na tashi..

Tin Daga nesa su indo da Abu suke kallanta Har ta qarasa suka fara gaisawa,, nijlah Zaki Sai tuwan ruwa?turo baki nijlah tayi tace,,kinga niba ciye ciye ya kawoni ba,,kallo kawai zanyi Na Koma gida,kaka tace kada Na zauna,,Bata Ida rufe baki ba Taji an Kira sunanta” dasauri ta dago Ido tana duban Wanda ya Kira sunanta,,bazata taba manta wannan fuskan ba,,Dan shine mutum Na farko daya taba dukanta..

Murguda masa baki tayi tana cewa,,lafiya Zaka Kira sunana?

kiyi hakuri nijlah Bada niyya nayi Hakan ba,,kinji yarinya, Nasir ya fada Suna Hada Ido da mashkur dayayi kama besan abinda suke ba..

Yarinya Kuma,,nice ma yarinya,,to sannu babba,,dariya Nasir yayi Yana Kallan nijlah,,nidai Duk ba wannan ba,kin yafemin?

Karka damu Allah yanasan me yafiya nayafema,,Nima ka yafemin batama Mota danayi”

Nagode sosai Nasir ya fada Yana murmushi,,sedai Bani Zaki nema tafiyan Bata motor ba,kinga Wanda Zaki nema danba motana bane nashine,Nasir yafada Yana nuna Mata mashkur.

Har qasa nijlah ta sunkuya tana kallan fuskanshi tace,,Dan birni kayi hakuri Kaji, murmushi mashkur yayi,ya Bude baki a hankali yace,Tashi kinji kanwata,,maqale kafada nijlah nan yayi murmushi danya gane nufinta yace, shikenan Na hakura Amma Karki qara zana Mota kinji,,to nijlah tace ta Tashi da gudu zatabi kawayenta mashkur yace kinga nijlah zo..

Juyowa tayi da niyyan zuwa idanta ya safka Kan Na iro daya zuba Mata su alamun tambaya” lah iro yanzu nake dubanka anan,Hade Rai iro yayi Yana hararanta,,kai iro Daga tambaya Sai harara, nikaga tafiyana..

Ke nijlah Ina kikasan wadannan ya fada Yana nuna mashkur” cike da tsoro nijlah tace yayanane Daga birni suka zo” kin tabbata eh mana nijlah ta fada tana kallan mashkur” sosai mashkur ya cika da mamakin wayo irin Na yarinya sedai abinda yake tambayan kansa shin wanene wannan yaran da nijlah tayi Karya.

Nijlah Na ganin tafiyan iro ta qaraso kusa da mashkur tace gani” naira hamsin mashkur ya miqa nijlah Yana murmushi,amsa wannan Duk da Naji kince ba ciye ciye ya kawokiba,,

Nagode sedai kaka ta hanani amsar kudin samari indai ba iro ba,,wanene iro mashkur ya tsinci kansa da tambaya”

Iro yarone dabe wuci shekara 21 ba,,shine yake neman auren nijlah,, mashkur yaji Bello Na bashi amsa”

Kai Bello kana nufin kace wannan yarinya saurayi ne da ita??
Kwarai dagaske Bello ya bashi amsa,rufe fuska nijlah tayi tana dariya” mamaki sosai ya cika mashkur Nasir ne ya qara kallan nijlah yace yanzu Ke yarinya kinsan menene soyayya,,kasa Magana nijlah tayi ganin haka yasa Bello cewa..

Kinga nijlah amsa kije ki Sai abinda kikeso nizan Gaya yakumbo,,kasa amsa nijlah tayi Duk da tanasan siyan Abu a dandali,,qara miqa Mata kudin mashkur yayi,,Kanta a qasa tace Ni biyar Zaka Bani wannan yayi yawa ta fada Kanta a qasa..

Ki amsa wannan Bani da chanji,,wannan shine qaramin kudi a jikina,,Nasir Ko kanada Goma,,ta amsa wannan Nasir ya fada alamun Babu..

Kasa amsar kudin nijlah tayi,,kanwata ki amsa mana,kefa Naji yanzu kina Gaya Wani Ni yayankine kodama Karya kike,,Kunya ce ta kama nijlah nan ta miqa hannu ta amsa kudin,, 
Nagode sosai Allah yasaka da alkairi,,Nima gobe Zan Baka fura da nono,,

Bata jira amsar Saba ta Shiga dandali tana murna,,

Bata Dade a gurin ba ta tafi,,tin Daga bakin kofa nijlah Ke Kiran kaka,,kaka!
Kai wannan yarinya Ni harna fara bacci Zaki tadani,,kaka kinga wannan Dan birnin ya Bani kudi harna Sai abin biyar kinga sauran,ta fada tana miqa kaka Chanjin..

Lalala nijlah waya baki wannan kudin kaddai kicemin Wanda ya dakeki dazu,,kaka bashi bane Wanda ya riqe Yana mishi fada,,Kuma Shima yabani hakuri,,to Duk Naji Amma Daga Yau Karki qara amsar kudi ahannun Wani koba na hanaki ba,,kaka Nima ban amsaba,Ina wannan bellon na gidan Liman,eh nagane cewan kaka,to shine yace Na amsa Ze gayamiki,,to Allah ya akaimu goben zansa Malam ya tambaya.



Washe gari karfe 10 na safe Malam yaje gidan liman anan sukayi magana da Bello ya tabbatarwa da Malam yaran bashida matsala,sannan hankali Malam ya kwanta.


Tin asuba mashkur yake Kiran mummy sedai network ya Hana wayan Shiga,,dafe Kai yayi Yana salati,,lafiya mashkur badai wani matsala bane?
Matsalane babba Nasir tin jiya nake Kiran mummy wayan yaqi Shiga gashi kasan halin mummy na tabbata yau bata rintsa ba.
Ni abinda ke damuna Kenan tinda muka zo ban samu kowa a waya ba,,ance semun fita wani Dan kauye anan kusa zamufi samun network,,kaga Nasir Kai kasan da haka Ka Bari nake ta kira,tashi da sauri muje na Kira mummy”
Dariya Nasir yayi yace Kai mashkur tinda muka zo banji Ka Kira Yasmeen ba sai mummy.

Murmushi mashkur yayi kafin yace, Nasir bana hada mummy da kowa na tabbata yanzu Yasmeen tana daki ko bacci taba tashi ba,,mummy ko bazata iya bacci ba Dan bataji lafiya naba.

Nasir be qara magana ba sabida yadda da maganan mashkur ya tashi suka fita,,

Bello suka gani yazo kawo musu kayan kari,,abokaina ina zuwa,,waya mukesanyi cewan mashkur Yana miqa masa hannu,,bayan sun gaisa Bello ya ajiye kayan abincin suka nufi kauyen..

Da Malam suka hadu a hanya nan Malam yake masa godiyan kudin Daya ba nijlah,,bayan Malam ya tafi mashkur ya juya Yana kallan bello..

Bello Naga wannan mutumin sai godiya yake akan naba nijlah naira hamsin,,nawa Raina 50 take daze Namin godiya har haka???


Hmmm Kai agurinka naira 50 bata da yawa Amma Banda gurin Malam da jikarsa nijlah” au dama ba shine mahaifinta ba” 

Mahaifinta da maihaifiyarta sun   rasu suke Kula da komai nata sedai Basu da karfi,, Dan ma suna San yarinyar kullum addu’a suke Allah ya kawo Mata mijin aure su auran da ita su huta” 

Aure kuma nijlah har nawa take daga ganin yarinyar bata Ida shekara 11,, murmushi Bello yace yace ai nata Kai hakabama  saura wata 4 ta cika shekara Goma.

Tashin hankali Amma akesan auran da ita cewan Nasir cike da mamaki,,to Nasir ya zasuyi Basu dashi kuma mu a wannan kauyen muna auradda yara shakara 13 zuwa 14..

Hira sosai suka riqa tafiya Bello Yana Basu akan labarin iyayen nijlah da rayuwarta,,tin daga nan mashkur yafara Jin tausan yarinyar jiyake dayana da yadda zeyi Daya taimaketa, akan auren da akesan yimata,,ahaka har suka Kai inda network ya hau Kan wayansu..

Hamdala mashkur yayi ya Kira layin Mummy,,bugu Daya biyu ta dauka muryanta a sanyaye” Assalamu alaikum mummy na kin tashi lafiya??
Kaima kasani ko lafiya ko akasin haka,,yanzu abinda kayi Ka kyautamin Kenan kodan kaga na damu dakai ko auta.

Kiyi hakuri Mummy wallahi ba laifina bane garin me ba network yanzuma seda mukayi tattaki zuwa wani guri me nisa aka samu network.

What mashkur kana nufin bazan riqa samunka a waya ba,,to wallahi kayi gaggawan baro wannan kauyen kafin naci mutumcinka,,Kako San a zaune na kwana.

Pls mummy kiyi hakuri iya yaune Insha Allahu za’a gyara,,yafada haka danya kwantar Mata da hankali” 

Nidai nagayama kadawo kafin na Gaya daddynka tinda ni Ka rainani,,inyaso Shi yafada kaji” kiyi hakuri bata amashi ba ta katse Kiran ranta a mugun bace” yasan koya Kira ba dauka zatayi ba Dan haka ya tura Mata  text massage.

Layin Yasmeen ya Kira dake zaune kusa abbansu tana Shan ice cream” murmushi tayi tace lah abba kaga mashkur ya kira.

Murmushi abba yayi yace dama na gayamiki ze Kira saiki dauka kafin ya katse,, dasauri ta dauka ta tashi ta koma dakinta,,hello hubby nah!

Na’am baby kin tashi lafiya,,lafiya qlau sai kewanka,,baby daga tafiya harkin Fara kewa da wuri haka,,karki manta shekara guda zanyi,,

Narke masa tayi tana kukan shagwaba tace,,Dan Allah Kada kayimana haka kaface 1 month zakayi Ka dawo” ah ah baby garin da nisa bazan iya wannan sintirin ba,,keya kamata kizo mu gaisa.

Bata fuska Yasmeen tayi tana turo Baki,,kaima kasan bazan iya rayuwa a irin wannan gurin ba,,Kai dai dakaga zaka iya saika zauna”

To ai shikenan kinga Kenan bakisan gani,,Allah hubby inaso Kaine Ka zabamana wannan rayuwa ta nisanta juna,,

Hira Sosai sukayi har Saida Nasir ya kasheshi kafin suyi sallama su koma kauyen,,bayan kwana biyu kowa aka kaishi gurin aikinsa inda mashkur ze riqa koya yara karatu a makarantar primary ta gari.

Sosai yayi mamaki da ganin ko ajujuwan babu gaba daya sun lalace birbiri ya Gama lalata sauran,,a haka yake koya musu duk da ba zuwa sukeba,,watarana sedai yaje Shi Daya yagama abinda zeyi ya dawo…

Nasir yayi sa’a kauyen da aka Kashi a kusa yake sedai Shi ana samun lalbai Dan Har headmaster garesu..

Wasa wasa Shakuwa me karfi Na qara Shiga tsakanin nijlah da mashkur,kullum saita kawo masa warar Fulani shiko yanasan taimaka musu Amma Malam ya Hana yace indai ba auren nijlah yakeso ba Baze amsa kudinsaba,,ba yadda mashkur ya Iya haka ya hakura sedai kullum Yana ba nijlah naira Goma Ko biyar tana zuwa dandali.


Yau tin safe Malam ya tashi bashi da Ko naira biyar balle su Sami abinda zasu sa a bakinsu.

Tinda nijlah ta Tashi take kuka ita yinwa takeji gashi Har karfe 12 Na safe Basu Sami abinda zasu sa a bakinsu ba.

Dan Allah Malam kabar yarinyarnan ta Shiga Ko gidansu Indo ne tasa Wani Abu a cikinta kaga yaro besan Babu ba” Ni kaina abinda nake tinanin kenan sedai Bazan bar yarinya tana zuwa kwadayi gidan mutane ba,,tinda su Basu tausaya sun bamu ba..

Malam me zakayi Kar ka cemin Baka fasa Bada sadakan nijlah ba,,Dan Allah kabari kaqarasa Ko shakara Goma sha biyu ne” kinga yakumbo ki rufemin baki,,Ina yanzu nijlah ta cika shekara Goma.
Dan Allah ba shawaranki nake nemaba..

Amma Malam…!Amma me kinfisu yinwa ya kashe yarinya muna kallo,,Idan Ko Na auradda ita Na tabbata bazata Rasa abinda zata Ciba…

To Malam wazata aura kasan Dai iro bashi da kudin aure Kuma Koda ka bashi sadaka Baze Iya ciyar da nijlah ba sabida Shima dakyar take samu yaci..


Bashi zanba auren taba sedai inaso kisani a kwana kusa Zan auran da ita,,kai malam kafa Duba lamarin nan,

Nijlah Najin batin aure ta tashi tana me Jin Dadi tace,,Malam ka gyale maganan kaka kayimin aure Nima Na riqa tuqa tuwo da kaina mijina Na siyomin tsire inaci…

Yauwa Yar albarka,Allah yasa asamu Wanda Ze Iya riqemana Ke ya Kula da maraicinki,,hawaye kaka ta goge da zanin jikinta tace..

To a gaskiya koka auran da nijlah sedai mijin ya biyota gidannan Dan gaskiya banga Wanda Ze Iya juran rigiman nijlah ba” Idan kinga ana haka Sai kiyi,kinga Nina fita karbomana bashi Ko gari musamu Musa a cikinmu..

Adawo lafiya yakumbo tayiwa Malam kafin ta janyo nijlah ta rungume tana rera kuka” Kaji kaka da baqin ciki,,bakiso Nima mijina ya riqa saimin kayan dadi ..



Yawan comments yawan typing,Dan Allah ku rage godiya ki riqa sharshi Ta hakane zan gane sakon danake San isarwa Yana zuwa muku




Comments & Share????






*Momn sultan ce*✍✍✍

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button