NOVELSUncategorized

SOORAJ 4

“Wayyo Mamana kinga rashinki abundaya jawomin, Ya Allah kataimakeni kakawomin ɗauki!” Ziyada tafaɗi haka cikin matsanancin kuka.  Tsabar kukan da Ziyada tayi harsaida muryarta ta dashe.     Tana zaune aɗaki taji muryan Babanta, a tsakar gidan nasu, da sauri ta ɗaga labulen ɗakin tana leƙensa, sosai takejin tsananin tausayin mahaifinnata, duk da cewa tana da ƙananun shekaru amma hakan baisa takasa fahimtan cewa wasu abubuwan dayake aikatawa ba acikin hayyacinsa yakeyinsu ba,    ganin yafice daga cikin gidanne, yasa tafaki idon mutane tarufa masa baya, zaune ta iskeshi akan ɗan dakalin dake ƙofar gidannasu.  Tsugunnawa tayi agabansa  Cikin da shashshiyar muryarta da ta ƙoshi da kuka tace

“Baba!”  

ɗagowa yayi ya kalleta, batare da ya amsa mata ba.

“Dan Allah Baba kataimakeni, wallahi banason ɗan dashe!”  tafaɗi haka hawaye suna mai kwaranya daga cikin idanunta.

Shiru Malam Garba yayi cike da tausayin ƴartasa, lokaci guda kuwa ya zabura kamar anjona masa shocking.  

“Uban maikikeyi anan?” yatambayeta atsawace.  

Jikintane yasoma rawa, yayinda kuka yasakecin ƙarfinta,  cikin kukan tace.  “Dan Allah Baba kaceci rayuwata, katunafa ni amana ce Allah yabaka, dan Allah Karka bari acutar da rayuwata!!”

Wata uwar tsawa yakuma doka mata, haɗe da rufe idanunsa yakorata gida.

Haka takoma gida tana kuka maicin rai, lallai tasake tabbatarwa da kanta cewa ita cikakkiyar marar gata ce, zama tayi akan  tabarmarta haɗe da sanya hanu ta share hawayenta, lokaci guda taji zuciyarta tayi wani irin bushewa, yayinda wani tunani yaɗarsu acikin ranta…

(Menene ra’ayinku akan auren ZIYADA da Tsoho Ɗan Dashe? Bazan cigaba ba harsai naga ruwan comment da vote ɗinku, dama nace yawan comment yawan typing.)

*✅OTE ME ON WATTPAD*
           @fatymasardauna

#Love
#Romance

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button