NOVELSUncategorized

SOORAJ 5

????????????????????????????????????????

                *SOORAJ*

    *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*

*????Kainuwa Writers Association*

_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain and motivate the mind of readers}_


*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*

           *WATTPAD*
     @fatymasardauna

       *CHAPTER 5*

Wanene SOORAJ? 

Alhaji Mansur Mai Nasara shi ne yakasance uba ga SOORAJ, Alhaji Mansur Mai Nasara wani hamshaƙin mai arziki ne dake zaune acikin garin Kaduna, Alhaji Mansur  tsohon commissioner’n  Ilimi ne dake zaune a cikin garin Kaduna, cikakken ɗan boko ne shi, wanda yatara dukiya, sannan mutum ne  dayake jure gwagwar mayar rayuwa, wannan yasa mutane suka masa laƙabi da suna MAI NASARA, saboda duk wani  abu daya sanya agaba saiyayi nasara akai.    Hajiya Sulaimiya  itace matarsa kuma mahaifiya ga SOORAJ, Hajiya Sulaimiya dai irin wayayyun matan nan ne, don asalinta yar ƙasar  Sudan 
ce,  tana da kyau sosai, tsananin kyawunta yana ɗaya daga cikin abun daya sanya Alhaji Mansur, narka maƙudan kuɗaɗe wajen  ganin ya aurota,   zama sukeyi cike da so da kuma ƙaunar juna, koda yaushe cikin farinciki suke, shekaransu uku da aure Allah ya azurtasu da samun ƙaruwan yaro namiji,  tun daga randa aka haifi SOORAJ Alhaji Mansur yaƙara ganin buɗi acikin arzikinsa, soyayyar duniya suka ɗauka suka ɗaura ta akan yaron nasu,  komai Na SOORAJ irin na Mahaifiyarsa ne domin kyawunta ya ɗauko.  sosai SOORAJ ke zuba tashen kyau da burgewa tun yana ƙarami,  saidai yataso da wani irin hali, miskiline na ƙarshe, sannan sam baida yawan magana, komai nasa atsare yakeyinsa, tun yanada shekara 12  mahaifinsa ya turasa England acan yayi gaba ɗaya karatunsa, tundaga kan secondary school har zuwa Masters ɗinsa, P.H.D ɗinsa ne kawai yayi aƙasar America. Sosai SOORAJ yake da ƙwazo akan dukkan komai, babu ruwansa da kowa, rayuwarsa kawai yake,   bashida wani aboki aduniya sama da Mas’oud, sosai abotarsu tayi ƙarfi da Mas’oud, kasancewar sun fara abotanne tun suna ƙanana, gaba ɗaya sirrin Mas’oud SOORAJ yasani, haka shima Mas’oud ɗin yasan wasu sirrukan SOORAJ, saidai akwai wani sirri da SOORAJ ɗin yaɓoyewa kowa, shikaɗai yasan matsalarsa.  Tun daga kan SOORAJ Alhaji Mansur baisake haihuwa ba,  amma hakan baisa sun tashi  hankalinsu ba, kasancewarsu wayayyun ƴan boko, dama ba wani son tara ƴaƴa suke ba,   ayanzu dai SOORAJ yana da shekara 30 aduniya, cikekken matashine mai tsananin ji da kansa, rayuwarsa yakeyi maicike da burgewa baruwansa da kowa,   abune mawuyaci kaga dariyansa,   duk yanda Ƴan Mata keson samun daman kai kansu garesa, hakan baya yiwuwa, domin SOORAJ wani irin mutum ne, da akomai nasa baya sanya mata aciki, duk wata mu’amalarsa baya sanya mace aciki,  mace duk kyau da haɗuwarta sam bata gabansa, batama burgesa, duk wani irin karairaya da mace mai lafiya zata zo tayi agabansa bazata taɓa burgesaba, duk tsananin kyawun mace, SOORAJ bata burgesa, shi yariga daya sanya aransa cewa  mace bata cikin tsarinsa.  Ayanzu yana akine a babban bankin Nigeria dake cikin garin Abuja  wato Central Bank Of Nigeria (CBN)  yanzuma hutu ya ɗauka  shiyasa ya zo Kaduna wajen iyaye da danginsa.  A rayuwarsa yana tsananin son iyayensa, sai gashi kuma daga zuwansa sun laƙaba masa auren dole. Wannan shine taƙaitaccen tarihin SOORAJ MAI NASARA.

Kamar koda yaushe idan yana acikin damuwa  yakan fita yazaga gari, wani lokaci har ƙauyukan dake kusa dasu yake zuwa, sosai yakejin daɗi idan yaziyarci ƙauyuka musamman irin ƙauyukan da fulani ke rayuwa acikinsu,  yauma hakance  takasance dashi,   hakanan yaji yanason fita daga cikin gari, bayaso yakoma Abuja baije yaɗan zaga gari ba…  

Tsab yashirya kansa cikin long pencil jeans black colour,and Black t-shirt, agaban t-shirt ɗinnasa anrubuta ( THE MAN) da farin fenti.   white denim jacket fara irinta maza  yaɗaura akan rigar dake jikinsa, sosai kayan suka amshi jikinsa kasancewarsa mai farin fata,  wasu fararen takalma combat wanda aƙalla kuɗinsu zasu haura sama da 30k yasanya aƙafarsa, hmmm SOORAJ yanason gayu sosai, hakan yasa koda yaushe cikin ɗaukar hankali yake.   Da turarukansa masu tsada ya feshe jikinsa,  take ko ina naɗakinnasa ya gauraye da ƙamshi.  Wayoyinsa haɗe da key ɗin Range Rover ɗinsa ya ɗauka, kana yafice daga cikin ɗakin.

Yanashiga cikin motarsa ya kunnata, maigadi ne ya wangale masa gate,   yana cilla motar tasa kan titi yasoma murza steering motar ahankali cike da salo.. 

*ZIYADA*

Gaba ɗaya ko ina acikin garin yaɗauki shiru, babu wani abu dake kai kawo, kowa yana gida akillace, adai dai irin wannan lokacin mafi yawancin mutane suna kwance ne aɗaki suna bacci,     duhun dare ne sosai, babu wani abu dake motsi, sai ɗan abun da baza’a rasa ba,  kamar yanda ko ina yaɗauki shiru haka gidannasu ma yake shiru, babu motsin kowa, gaba ɗaya jama’ar gidan suna bacci, amma banda ita, idanunta sun ƙeƙashe sun bushe, babu wani alamun bacci acikinsu, tun tana kuka da iyaka ƙarfinta, harta koma sauƙe ajiyar zuciya akai akai, babu wani abu dake ɗaga mata hankali, kamar idan tatuna cewa gobe za’a ɗaura mata aure da Tsoho Ɗan Dashe, tsohon dakowa yasan cewa ba mutumin kirki bane,    shiru tayi tana mai sake nazartan abun da zuciyarta ke raya ma ta.   Tabbas awani ɓangaren tunanin dake kwance cikin  zuciyarta awajenta shine daidai, amma kuma tawani wajen tanaga kamar hakan ba daidai bane, duk duniya bata da kowa sai mahaifinta da kuma danginsa da suka ɗauki karan tsana suka ɗaura mata.     Tana zaune awajen taji ansoma ƙiraye ƙirayen sallan asuba, jitayi gabanta ya tsananta bugawa,  lokaci ɗaya taji zuciyarta na ingizata,  ɗan dangwalin kayanta taɗauka, haɗe da yaye labulen ɗakinnata tasako kanta kaɗan tana leƙa tsakar gidannasu, ganin bakowa yasa tafito saɗaf saɗaf ta nufi hanyar fita daga gidan, saida takai bakin ƙofa kafun ta tsaya tare da juyowa tana mai kallon ƙofar ɗakin Babanta, wata irin karyewa zuciyarta tayi, take sai ga hawaye nasauƙa akan kumatunta, sosai takeson Babanta, tasan duk wani abu dayakeyi mata balaifinsa bane, amma bata da yanda zatayi, dole ko duniya ne ma tashiga, dole tanesanta kanta ga faɗawa halakar auren tsoho ɗan dashe.  Juyawa tayi aɗari tabar cikin gidannasu, gudu takeyi sosai harta yi nisa da gidajen dake cikin ƙauyen tasoma shiga jejin dazai sadata da bakin hanya, komai tanayinshine acikin ƙarfin hali, amma har aƙasan zuciyarta tsorone shimfuɗe..

Bai kwana acikin garin Kaduna ba, kasancewar dare yayi masa, sam shi ba mutum bane mai son tafiyar dare, hakan yasa ya gangara gefen hanya, anan ya kwana cikin motarsa.   Asuban fari yakamo hanyar dawowa cikin gari, saboda yau ɗin yakeso ya koma Abuja.   Gudu sosai yaketa shararawa akan titi kasancewar babu wasu yalwan motoci dake tafiya akan titin. 

Ba ƙaramin tafiya bane daga cikin ƙauyen nasu zuwa bakin titi saboda haka sosai tagalabaita,  ganin takusa  kawo bakin titi ne yasa ta rage sauri tasoma tafiya ahankali, dama ƙarfinta yasoma ƙarewa.   Jitayi kamar anabin bayanta, da sauri tawaiwaya aikuwa wasu maza tagani su biyu abayanta,  waro manya manyan idanunta tayi cike da tsoro tana kallonsu, dariya suka bushe dashi,  ɗayanne ya sanya harshe yalashi laɓɓansa, cikin yanayi irin na ƴan iska yace.   “Baaba yau fa munyi babban samuwa, ɗanyen kaya ce” 

Dariya wanda aka ƙira da suna Baaba yayi, ya karkace tsayuwarsa tare da kai hanunsa kan belt ɗin wandonsa.    “Ay gaye yau zamu more”  yafaɗi haka yana me zare belt ɗin wandonsa.  
Ganin haka yasa Ziyada shiga cikin wani  irin matsanancin firgici, aruɗe tasoma ja  baya,  da ƙarfin gaske ɗayan ya fusgota, ihu tashiga yi tare da yunƙurin ƙwace kanta amma riƙon da yayi mata bana wasa bane,  ɗan kwalin dake kanta ya fusge ya yi cilli dashi gefe, ganin haka yasa taƙara fasa ihu haɗe da turjewa, amma takasa ƙwacewa, hanunsa yasanya da iyaka ƙarfinsa ya ja rigan koɗaɗɗiyar atamfan dake jikinta, ɓesss kakeji rigar ta yage, dama tuni kayan sunyi laushi.  Ganin saman ƙirjinta ya bayyana afili, yasa samarin suka bushe da dariya, kowanne acikinsu jikinsa yaɗauki mazari, burinsu kawai shine suga sun farketa.    Wani irin ihu Ziyada tasa tare da kafa bakinta akan hanun wanda ke riƙe da ita ta sakarmasa cizo, awahalce yasaketa yana fidda wani irin ƙaran azaba, itakuwa aguje ta lula cikin jejin.   Ganin haka yasa suka rufa mata baya, gudu take sosai  suna biye da ita, sam batasan cewa takawo bakin titi ba,  aguje ta zo zata bi takan titin tasake faɗawa wani jejin… Kafun ƙiftawan ido wata mota da tataho aguje tayi sama da ita, tim haka ta faɗo ƙasa.   Amatuƙar razane yafito daga cikin motar yayo kanta,  waro kyawawan idanunsa waje yayi tare dasa hanu ya toshe bakinsa, lokaci guda jikinsa yaɗauki rawa ganin irin ɓarnar da yayi,  kwance take cikin jini ba ako iya gane kamanninta,  wani irin rawa jikinsa keyi kamar anjona masa shocking, hannayensa duka yasanya yaɗagota, buɗe motar yayi yasata agidan baya, yanashiga wajen driver ko gama rufe murfin motar baiyiba, ya figi motar da gudun gaske.   Samarinnan naganin abun daya faru sukayi saɗaf saɗaf suka bar wajen, cike da haushin rashin samun nasara da basuyi ba.

Gudun da yakeyi har ya wuce hankali, tamkar zaitashi sama, gaba ɗaya ya ruɗe, ganin yanda jini ke fita ajikinta.  Alokacin daya shigo cikin garin Kaduna, gani yake kamar motar tasa bata gudu, hakanne yasanya yaƙara gudun motar mintuna kaɗan saigashi a cikin asibiti,   amatuƙar ruɗe yaje yaƙira likitoti suka zo suka ɗauketa aka wuce da ita emergency room.   Ganin yanda kanta ke zubda jini yasa likitoti suka duƙufa akanta wajen bata taimakon gaggawa.

Shikuwa SOORAJ yana nan awaje yakasa zaune yakasa tsaye, hankalinsa amatuƙar tashe yake, tsoronsa ɗaya kar ace masa ta mutu,  wani irin gumi ne ke fesowa ta goshinsa, kowa yagansa yasan cewa yana cikin tashin hankali.

Aƙalla sama da awa ɗaya da rabi likitoti suka ɗauka suna bata taimakon gaggawa,  cikin ikon Allah Kuwa sun shawo kan lamarin, saidai bata farfaɗo ba, amma sun tsaida jinin dake fita daga goshinta dakuma gefen kanta da ya fashe.

Yana tsaye likitotin suka fito daga Emergency room ɗin.  Da sauri yataho wajen  Dr.Salees, baikai ga cewa komaiba Dr.Salees yasakar masa murmushi tare da sanya hanu ya dafa kafaɗan SOORAJ ɗin.    
“Karka damu SOORAJ munshawo kan matsalan, sai dai mujira farkawanta, muje office saina ƙarasama sauran bayanin” 

Babu musu SOORAJ yabi bayan Dr.Salees zuwa office ɗinsa.

Suna shiga cikin office ɗin Dr.Salees ya nunawa SOORAJ wajen zama, kana shima ya zauna.

Sakeyin musabaha sukayi kafun Dr.Salees yacigaba da cewa. 

“Ka kwantar da hankalinka ba wani babban damuwa bane, buguwane  kawai, tabugu sosai gaskiya, amma dayardan Allah munshawo kan komai, saidai kuma bamusan awani irin yanayi zata buɗe idanuba, amma muna kyautata zato, Insha Allahu ma zata tashi lafiya, Allah dai yatsare na gaba” 

Da “Ameen” Kawai SOORAJ ya amsa yana mai sauƙe ajiyar zuciya akai akai. 

Bisa umarnin SOORAJ aka maidata wani special room,,,,   ahankali yaturo ƙofar ɗakin yashigo, sauƙe idanunsa yayi akanta, tana kwance flat kanta na kallon sama, gaba ɗaya rigar dake jikinta ta ɓaci da jini, kanta kuwa a ɗaure yake da farin bandeji (bandage) yayinda tulin gashin kanta ke watse akan pillow, ɗauke kansa yayi daga kallonta tare da ƙarasowa cikin ɗakin, kan wata kujera yaje ya zauna haɗe da kai dubansa kan ledan ruwan da aka saƙalashi ajikin wani dogon ƙarfe, yana shiga cikin jikinta ahankali, kallonsa yakuma dawowa dashi kan agogon kamfanin Gucci dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa.  Ƙarfe goma na safe daidai haka agogon yanuna masa,  hanunsa yaɗaura akan haɓansa haɗe da furzar da iska daga bakinsa,  miƙewa yayi tsaye tare da nufar ƙofar fita, haryaje bakin ƙofar kuma sai ya tsaya juyowa yayi ya kalleta, idanunsa ne suka sauƙa akan ƙirjinta da kusan rabin breast ɗinta suke a bayyane, da sauri yakawar da kansa, wani irin bugawa yaji kansa yayi, kamar andoka masa guduma,   jacket ɗin dake jikinsa ya cire tare da nufar inda take kwance, saidai koda wasa baisake barin idanunsa sun kalli ƙirjinnata ba,   jacket ɗin nasa yarufa mata ajikinta, kana yafice daga cikin ɗakin.     Office ɗin Dr.Salees yaje ya biya kuɗi, aka tura nurses guda biyu wanda zasu tsaya akanta don bata kulawa, shikuwa motarsa yashiga yabar asibitin.     Direct gidansa ya nufa ransa ajagule, sam baiso haka takasance ba, yau yatsara tafiya Abuja, amma ga abun daya faru, zaman cikin Kaduna yakamashi dole harzuwa farfaɗowar yarinyar.

Wanka yayi kana yazo ya kwanta akan gado, lamo yayi yana tunanin yanda accident ɗin ya kasance, sai alokacinne ma mamaki ya kamasa,  ƙaramar yarinya irinta mai zai fito da ita awannan lokacin? da dukkan alamu kuma ba acikin hayyacinta take ba.  “To kodai mahaukaciya ce?” ya raya hakan azuciyarsa, da sauri ya kawar da wannan tunanin acikin ransa,  wayarsa yaɗauka ya kunna karatun Al’Qur’ani mai girma, yana cikin jin karatun bacci ɓarawo ya sace shi….. 

(More Comment nd Vote more typing???? kuyi haƙuri yau banyi editing ba…   Zan fara halina fa readers idan nayi update yau sai jibi kuma???????? Allah yasa bazaku takura ba. )

         
        *18/March/2020*

*✅OTE ME ON WATTPAD*
         @fatymasardauna

#Love
#Romance

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button