TAKUN SAAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

TAKUN SAAKA 13

        Ido Yaya Umar ya rimtse da ƙarfi yana dunƙule hannunsa. 

     “Kai fitsararre, idan shi ka rainashi ai mu ka ɗaga mana ƙafa kodan rashin saninmu da kai ko.”

     Ƙafa Yaya Umar ya ɗaga zai cigaba da tafiya wasu hawaye masu zafin gaske na gangaroma kumatunsa.

      “Dawo ka zauna”. Umarni da ga Ummi ya hanashi ajiye kafar da ya ɗaga ɗin.

       “Iyeee! A lallai Haƙilu kuna ganin jalalar rayuwa. Wato itace kawai mai sawa da hanawa akan ƴaƴan, bayan wahalar da kaci na kula da su tsahon shekaru. Tabbas Hasiya kinyi asara kekam. 

        Da sauri Ammar ya ɗago ya kallesa. Ya miƙe tare da nuna Kawu Bello da ɗan yatsa cikin kaushi da ɗaci yace, “Kai kaine kai asara tsohon banza ɗan tasha”.

        A tare Hajiya mama da Abba da kawu Bello da kawu Hannafi suka zazzaro ido suna zabura. Ummi tai saurin fisgo hannun Ammar tare da daka masa tsawa. “Aliyu!!”.

          Cikin ficewar hayyaci ya fisge hannunta a cikin nasa da faɗin, “Haba Ummi, wai sai yau she ne zaki daina zama anacin kashi akanki a gidannan ne? Babu ruwana da alaƙarsu gareki. Na rantse da ALLAH idan tsoho bai gyara kalaman harshensa ba to kafin ya fita a falon nan zan datse harshen kuwa na jefar ƙasa”.

      Ɗimmm

Ummi ta sauke ma Ammar dundu. “Ammar kanada hankali kuwa? Miyasa kai bana faɗa maka kaji ne wai?. Kasan waɗan nan ɗin su wanene a wajena? To iyayena ne, ƙannen mahaifiyata ne, tamakar yanda Hajiya mama ta ke uwa a gareni itama. Ka shiga hankalinka kona saɓa maka kaji ko”.

      “Amma Umm…..”

Wani kallo da ta masa ya sakashi yin shiru ya haɗiye sauran maganar.

     Wata ƴar dariya Abba yayi da faɗin, “Kun gani ko? Hakafa gidan yake kullum kamar na ƴan tasha. Sun rainani basa ganin mutunci na bale na mama, bayan ma yaƙi nai da zuciyata wajen rufa mata asiri. To uwar tasu ma ba wai raga mata sukeyi ba. Dan haka na ɗakko ku nan dan ayita ta ƙare. Bazan iya cigaba da ciyar da ƙattan banza ba. Dan haka na yanke shawarar aura musu su Amlah, inba hakaba wataran yankan rago za’a samu sunmin a gidan nan. Ita kuma waccan fitsararriyar uwar ƴan janye-janyen jidalin da suke ɗaurama ƙugu a gidan tana zuba taɓara saboda ita ƴar ido ce Junaid zan aurawa. kunga shikenan anyi tuwona maina ko ba komai sun huta da gori ma asalin uwarsu.”

       “Wannan gaskiya ne Haƙilu. Ai kama taimaki rayuwarsu. Dan a zamanin nan kowa yaji tushen zancen ta ina zai basu ƴarsa. Balle ma ita da take ƴa mace. Bayan ma ka riga ka bata Junaidu ɗin ai wlhy da nayima Musa kamu ma”.

          Da sauri Abba ya ce, “Shi Musan sai yay haƙuri tunda na riga naima Junaid ɗin alƙawari dai. ALLAH ya bashi ta shi”.

       Yaya Muhammad da ya ƙule matuƙa da takaicinsu ya buɗe baki zai yi magana. Amma sai Ummi tai saurin girgiza masa kanta cikin gargaɗi. Kawai sai gani tai hawaye suna sakko masa tsabar zuciyarsa ta kai ƙololuwa a ɓaci.

         Ummi itace ke katange dukkan yunƙurinsu, sun rasa miyasa take hakan a gare su game da dangin mahaifin nasu. Abinda ma basu gane ba shine a yau. Shin ta amshi ballagazayen ƴaƴan gidan da ake iƙirarin an basu kenan matsayin matansu ko mi? Koda ace zasuyi haƙuri suyi mata biyayya bazasu taɓa amincewa a aurama Junaid Hibbah ba. Sai dai komi zai faru ya faru wlhy………..✍

*_Tofa masu karatu, yaya kenan? Wanene zai ci nasara tsakanin su Abba da su Yaya Muhammad? Ni kaina inason jin wace ƙaddarace baibaye da Ummi da ta fi bukatar haƙuri da cin kashin waɗan nan mutane haka?. Kumuje zuwa. muna gab da tsunduma cikin wasan gadan-gadan????????????_*

*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????

#team ZAFAFA BIYAR????????????????????

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_* 

         

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button