NOVELSUncategorized

WA ZAI FURTA 16

???? *WA ZAI FURTA?*????
              1⃣6⃣

*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( Hajia Rabi badawi Kano maman Ibrahim ), Allah ya Kara arziki ya shirya Miki zuri’a ya Kara Miki tsawon kwana. Amin.* ( Allah ya Kara tsareki daga sharrin munafukai Kuma azzalumai ).



*KINA RAINA MAMAN WEEDAD*

*Domin ki…… beloved sister Khadija Dahiru wowo miji na gari I pray*


          ************
*Federal University dutsinma*

……Ta rike kugu ta tsare shi da ido sannan ta ce *Who are you?*
  Ya kyalkyace da dariya *Nine Anwar*….. Wallahi ka Fara bani tsoro ni ban yarda da Kai ba,kawai ta firgice mishi tana baya baya…… Tana neman Tara mishi jama’a ya Fara magana a hankali “`look calm down please I’ll explain let’s go“`…….ba inda Zan bika sai kwallah sharrrr, duk jikinta ya tsinke da rawa.
Ya zaro ido yace “`this is serious“`……. Yallabai an saka a mota…. Please zanyi magana bani minti biyu just go away…
Bilkisu please kizo muje Zan Miki bayani…. Wallahi bazan bika ba. Kai Bari na fada maka ni ban ma yarda da dakai ba……sai kuka.
Ya runtse ido yace ohh my God this girl nawaoooo.
Ya fiddo waya, ya Kira sadeeq…. Sadeeq please come to Abis super market now am there with Bilkisu… Ya latse wayar….. Kiyi shiru Dan Allah ke ba ki wuyar kuka what’s wrong with you???
Ta mishi banza…
Ya sa hannu zai kamota tayi baya saura kadan ta fada cikin kwalayen lemuka…. Zaki Fadi fa ya daka Mata tsawa.
Ta makure wallahi kana tabani Zan maka ihu.
Ya kura mata ido kawai ya maida hannuwa ya rungume.
Yana hango sadeeq mashin ya ajiyeshi ya fita da sauri….. Please save me she’s suspecting me…mtsew ya doka tsoki ya wuce Shi.
  Tana tsaye ko motsi ta kasayi, sadeeq ya kalleta zo muje Bilkisu kinji.
  Duk jikinta ya mutu ta biyo shi, ya bude Mata mota tana Zama shima ya shigo ya rufe kofa, Sadeeq ya shiga gaba suka tafi.
   Bayan an sauke kayan kaf, sadeeq ya kalleta ya akayi ne Bilkisu me ya faru?
 Kwallah suka zubo mata, Dan Allah kiyi hakuri kiyi shiru menene ya faru? Idan Kuma kina da tamabaya akan Anwar kiyi mun Zan baki amsa wallahi…… Wanene Anwar?, Wallahi ni ban yarda dashi ba, duba ka gani ta nuna mishi tulin kayan da hannu wannan siyayyar hankali ce? Kuma naga dollars sun fado aljihun sa yace ajiyar ka ce he’s always hiding something from me why?.…..
Kiyi hakuri…… Wallahi bazanyi hakuri ba yace mun Shi a kauyen Kano yake Yana business da wani ubangidan sa Kuma…… Karya yakeyi. Sadeeq ya katseta.
Ya kalleshi da sauri, me kake nufi?
Ina nufin gidan ku akwai kudi Kuma cikin garin Kano kake ba kauye ba. Ya kalleta what else do you want to know?…….. Ya ingijeshi shikenan ka tafi tunda taji daga bakin ka Zan Mata bayanin saura.
Ya yi dariya, wannan rawar kafar da kakeyi Shi ke tona maka ASIRI….. I said go ya Kara tura shi.
Allah ba inda zanje.
Bilkisu karya yakeyi babba gida ya fito.
  Ni meye nawa a ciki da yake boye mun? Ta fada tana hararar sa, ya yi murmushi hankalin ki ya kwanta Yanzu?
Ban sani ba ta juya…… Ya kamota, me yasa baki ganewa ne ke? Nace idan Ina Miki magana ki daina tafiya bazaki daina ba ko? Sai ranar dana kamaki gaban wadanda kike ji ma kunya Zaki…..Amma Kai iyakar Dan iska ka Kai.
Saketa wallahi.
Ya saketa Yana Yar dariya.
Kinga Bilkisu je kirawo kawayenki su shigar Miki da kayan Nan…..bazata dawo ba Kuma wallahi binta zanyi ciki Kama fada Mata.
Don’t mind him jeki abinki.
Ya bita da ido…….
Zaka rikita Yar mutane Anwar wallahi ta tsora fa da gaske…… Ya kwashe da dariya kawai.
Asirin ka ya Fara tonuwa sai ka yi kokari Kuma Yanzu ka  *FURTA* Mata…. Uwarka…. Yakai mishi duka.
Yarinyar can sadeeq rigimammiya ce Kuma shagwababbiya…… Komai sai ta bude Baki tana kuka.
  A gaskiya ka takura mata….. Fitowar su yasa ya tsayar da maganar.
  Ko kallonsu baiyi ba ya ce Bilkisu minti biyu….. Ya danyi gefe can nesa.
  Tayi tsaye, sadeeq ya kalleta kije kada ya Kara Mata Mana lokaci I’ll talk to him please.
 Ta wuce kanta kasa, ta rasa inda zata sa ranta.
Ta tsaya nesa dashi,
Ya kalleta ki matso koni nazo Nan…. Ina jinka daga na…… Taku daya ta ganshi gabanta wallahi kina motsawa Ina kamaki, ya fada.
Tayi kasa da Kai…. *tawa ta sameni ni Bilkisu* tace a zuciya.
  Ya kamata kiyi mun godiya ko?
Ko nayi laifi ne?
Hmmm, na gode Allah ya biya.
Good, yace Yana murmushi.
 Ya kalli hannun sa *I really like this watch honestly* 
Ta ce hmm, kawai.
Yanzu hankalin ki ya kwanta kin Kuma yarda dani tunda kinji na fito daga babban gida?
Um, ta ce a takaice.
   Gobe ba lecture ko?
Ta ce um.
Sai dare kenan zamu hadu?….. Anwar Dan Allah ka rage zuwa wurina bana son abinda zaiyi affecting karatu na gaskiya.
Ya kura Mata ido yayi shiru…..har sai da ta dago ido ta kalleshi.
Ta mayar da Kai kasa.
  Kamar zaice wani Abu sai Kuma ya fasa yace okay I’ll try.
Ta ce na gode, sai da safe…..
Ya matsa baya kawai ya bata wuri ta wuce.
Ta Dan kalleshi kadan fuskar sa ta canza alamar damuwa…. Kirjinta ya buga da karfi.
  Kamar tayi magana Kuma ta fasa ta wuce.
Sadeeq na tsaye su Aisha Kuma sun shiga da kayan, ta mishi sai da safe ta wuce….
  Har ta shige idon sa na kanta ya kalli sadeeq shi Kuma ya banka mishi harara, wannan rawar kafar ita zata……I don’t know how to control my self. Abun ya Fara damuna.
 Wata muguwar dariya sadeeq ya saki tare da fadin *Anzo wurin.*
  Murmushi kawai yayi.
Kana hauka ne kayi Mata irin wannan shopping din?
Mtsew wallahi Bilkisu da kake gani ta banbanta da ko wace irin mace class din yarinyar yayi yawa could you imagine she refused to take abinda takeso sai da taga da gaske Zan kwashe kayan shagon?.
  Da sai ka bita a haka for once gaba gaba idan kun Kara sabawa sai ta dauka…… I don’t think so.
  Kuma wadannan banzayen dollars din ne suka rikitata cos har muka Kare she was shocked but couldn’t….. Gaskiya ta firgita.
  Ya kamata fa ka Kama kanka gaskiya wallahi kada ta birkice maka kuma ko ta tsorata tsoron yasa ta gujeka.
    Mtseew…. I said I’ll try. Ya fada Yana yarfa hannu.
And ka rage kakkamata fa….. Ba laifina bane wannan fa, sadeeq yarinyar nan fa baza ka gane ba. Wallahi sai muna tsaka da magana sai ta nemi guduwa I told her this is what will happen idan tayi she refused to listen….and I have no choice than…. This is not an excuse idiot. Ya katse Shi.
Ya kamata fa ka duba kada kazo ka kasa shawo kanta bayan ta rikice maka….. Mtsew naji Zan jaraba.
Yanzu ai hankalin ka ya kwanta ka fada Mata Ina da kudi….. Kuna da kudi dai ba kana dashi ba.
Bari kaji na fada maka a yanda kayi Mata Yanzu wannan kadai ce hanya da zata fisshe ka. 
  Kana tunanin Koda kudi nane da gaske kana iya wannan gabatar? Kayi abinda hankali zai dauka Mana. Amma Yanzu na fada maka Kuna da kudi komeye ta dauka zata ajiye.
 A yanda ta firgita some muka fada Mata bayan wannan wallahi Koda ta yarda a fili a zuciyarta zata ci gaba da wasi wasi Kuma hakan zai haifar Mata da bincike akanka… Kayi tunani Mana.
 Kuma fa hakane.
Yawwa.
Amma Yanzu kaga tasan Kai Dan masu kudi ne zaka iya komai shikenan.
Yayi ajiyar zuciya *I too much like you sadeeq*
Suka kyalkyace da dariya tare da tafawa……

Aisha kadai ta tarar dakin a zaune ta tasa Kaya gaba tana kallo.
  Ko takalmi bata cire ba ta fada bisa katifa……. Aisha na shiga uku.
  Wai ya akayi ne? Fada kukayi da Anwar din bayan fitar ku? Naga alamun kinyi kuka Shi Kuma sai babbata Rai yakeyi…… Aisha Anwar yafi ciwon ciki…. Ta kwance Mata zance kaf!
Ko kadan Aisha bata razana ba. Sai tayi murmushi tace, ni wallahi nasan Anwar Dan manyan mutane ne. Haba kiyi tsam da Rai ki kalleshi da kyau ya Miki kama da mazauni kauye?
Ko fatar jikin Anwar Kika kalla kinsan ana rayuwa cikin A/C da Jin dadi.
  Bari in Baki karamin takadiri ki kalli yanayin shigar da yakeyi duk kayan Anwar tsadaddu ne daga manyan kamfuna manya manya irin su *Gucci, M&S, C&K* ke gasu nan. Ji takalmomin da yake sawa….. Haba mutane, Ni wallahi nasan karya ne ace duk sadeeq ke musu sai dai na yarda shikeyi ma sadeeq saboda ko dressing yanayin dauka a jiki ma ba daya ba Koda kuwa iri daya suka saka .
  Ji lokacin zuwan su daddy ke baki lura bane Amma wallahi wani taku da Anwar keyi nasan yaron yaji bariki wallahi…..
Ke ni al’amarin sa ya Fara bani tsoro Aisha…… Hakuri zakiyi sonki yakeyi Kuma ya kasa *FURTAWA* kawai idan ya Miki kina sonsa Ina Baki shawarar kada ki Bari wata tayi Miki shigar kutse sannan kada ki yarda ki nuna kin San inda ya dosa ki barshi har ya gaji ya *FURTA* idan da gaske yakeyi.
Koda yake wannan hauka haukan da ya Fara tabbas saura kiris ya *FURTA*……. Aisha bana iya wa Anwar har ga Allah….. Ba Kya son sa?
Ta tsare ta da ido…… Tayi shiru ta kasa magana.
Kinji?
Idan bai Miki ba ki fada mishi ya rabu da ke, naga dai yanda Yan Mata ke neman kashe kansu saboda Shi Amma ke ya zabe ki kamar tumun dare Zaki….. Understand me please.
I’ll never understand you. Namiji kowa da kalar soyayyar sa, Anwar miskili, gadararre, Wanda ya Raina kowa kije kina bada labarin da kike bani Yanzu wani sai ya mare ki saboda cewa zasuyi karya kike yi amma Ni ganau ce ba jiyau ba.
 Amma ji yanda yake Miki rawar kafa.
Wallahi Yanzu dan ana farkon dawowa ba mutane Amma tabbas ni nasan wannan semester din akwai daru za ‘ayi kallo. Sai ki dage….. Abinda ke tayar mun da hankali kenan wallahi.
Tayi dariya zai tare Miki nasan dole ya….. Wani abun ba agaban sa zai faru ba Aisha…. Yanzu ni ya zanyi da wadannan Kaya ni Bilkisu…. Ci zamuyi. Yanzu fa aka dawo.
Ai wallahi mun gode……… Wayarta ta Fara Kara.
Ta kalli Aisha Anya Anwar zai barni nayi abin kirki wannan semester din?..
 Tayi dariya ta kwashi biscuits da wasu tarkace tace keni sai da safe…… Taja Mata kofa.
  Ta kanga wayar a kunne ba tare da tace komai ba…
 Ko har wayar ma an Sanya Mata doka?.
Ya fada Yana Yar dariya.
Hmmm, kawai tace.
Ke na gaji da hmm, dinnan da kike neman ki ringa kawoshi bana son sa ki bude Baki kiyi mun magana kinji ko?.
  Toh, tace a hankali tana murmushi.
 Da gaske ba Kya so Ina zuwa wurinki?
Eh, tace da sauri.
Saboda me?
Ta runtse ido anya mutane sun San Anwar kuwa da ake mishi shaidar baya magana?… Kinyi shiru. Ya katseta.
  Haka Nan,
Baiyiwuwa ki fada mun dalili ko Kuma gobe ki ganni…… Dokar daddy ce, sannan zuwan naka zai rinka haddasa mun fitina tsakanina da Yan matanka, idan Kuma aiki yayi nisa Zan Sami raunin  karatu…… Zuwa gidan naku?
Eh,
Fine. Zan daina zuwa shikenan ko?
Eh, ta ce tana murmushi.
Idan Zan ganki muyi magana Kuma fa?

Sai na sameka class….fine, gobe mu hadu new lecture rooms by four. Yana fadin haka ya kashe wayar.
   Ta bi wayar da kallo tace ikon Allah….. Allah ya kawoni ni Bilkisu…..
  Tayi shiri daga sallar la’sar, a hankali take tafiya ga nisa daga masallaci zuwa classes din, kanta a kasa kadan kadan take gaisawa da mutane.
  Kugin mashin taji a bayanta tayi saurin Kara matsawa gefen titi, gabanta suka tsaya, ya sauko sanye da kananan Kaya kamar kullum ya rufe ido da facing cap… Ajiye ni a nan.
Ta dago ido da saurin Jin maganar sa. Shida sadeeq ne bisa sabon mashin fari duk leda jikinsa.
Sadeeq Ina wuni ta fada tana murmushi.
Lafiya Lau Bilkisu.
Ta Dan kalli gefen sa Ina wuni.
Yayi kamar baiji ba, ta ce ai kaji tsiyar Shi dizgi wurinsa bai daukeshi bakin komai ba.
  Ka kawo man upstairs Yanzu please ya fada Yana kallon sa ya juya da mashin din Shi Kuma ya jera da ita suka ci gaba da tafiya bai ce komai ba,
Ina gaishe ka amma kayi shiru.
Ya dago ido cikin facing cap kince sadeeq Ina wuni Ni Kuma kin wani ce Ina wuni sunan nawa Yana Miki wahalar fada ne?
 Murmushi tayi kaii ikon Allah Wai haushi kaji?
Anwar Ina wuni?
Sunana Hamza…. A’a Nan Kuma daya fa. Sunan da kowa ke kiranka Zan ambata sai dai idan kana neman magana ne sai inji.
   Shiru kawai yayi Mata.
Tayi Yar dariya yau gadara ake ji, ta fada cikin zuci tana satar kallon sa Yana ta faman Shan kamshi Yana Bata rai.
   Maganar meye zamuyi kace mu hadu yau?
 Kina sauri ne?
Tayi dariya ohh ni Bilkisu halan bani da ikon tambaya.
 Murmushi kawai yayi ta gefen kunci.
 Suka shiga class din ba kowa sai mutum daya shima da alama chargy yakeyi, kasancewa farkon semester ne.
Ta toge bakin sit….ya kalleta wuce ciki ko ni Zaki saka cikin kujera?
 Ka zauna ni Bari……. Ya ingizata da karfi tayi ciki ya bita dole ta matsa da sauri kada ya Kara kamata…… Kina da gardama, na fada Miki idan Baki son Ina kamaki ko taba ki kada kiyi mun gardama amma da alama kina da kunnen Kashi…… Ya karasa maganar Yana Zama kujerar kusa da ita.
Da sai ka bada tazarar kujera daya tunda magana ce zamuyi ba karatu ba…… Bazanyi hakan ba.
Tayi shiru tare da sunkuyar da Kai tana wasa da yatsun hannunta.
   Yasu daddy?
Lafiya lau, dazun munyi waya yace mun zasu tafi Paris da mommy.
Haba?
Allah.
Yayi murmushi *Yan gayu*.
Ta Dan harareshi.
Dafatan baki sanar da kawayenki abinda ya faru jiya ba, kin San bana son yawan surutu ne yasa bana nuna ni din wanine…..
Aisha ce Kuma ta rigani sani…  Tasan meye?
Kuna da kudi?
Kice wallahi…. Tayi murmushi Allah kuwa, ta bashi labarin yanda sukayi.
Ya danyi tsoki, kawai don Ina sa Kaya masu kyau Shi zai nuna muna da kudi? She’s not well.
  Eh din. An dai gano ka.
Ya danyi dariya kawai.
Wace magana zamuyi kace nazo?
Ba gashi munayi ba?
Ko wata ta daban kike so muyi?…… Tsayuwar mashin din sadeeq yasa maganar da zatayi ta koma.
   Ya dora Kai bisa table ta bi bayanshi da kallo.
Ko baka lafiya ne yau? Naga duk kayi sukuku Anwar….. Sadeeq ya shigo ya ajiye ledoji bisa table din gashi nan Zan je na karbo sako isah kaita idan ka  gama ka kirani.
Bai dago Kai ba Yana duke ya rufe ido kawai.
Tayi shiruuuuu tana kallonsa…
Anwar….. Ta kirashi a hankali.
Ya dago Kai ya akayi?
Baka lafiya ne?
Ya yamutsa fuska yunwa nake ji ….. To ba gashi nan sadeeq ya kawo maka ba Kuma kana Jin sa Anwar kamar karamin yaro kayi shiru.
Fiddo ki ban ya fada tare da kokawa ya kife….. Bata San lokacin da tayi dariya ba ta Mike tare da saka hannu ta janyo ledar sai gogar jikinsa takeyi yaki Kuma gyarawa.
  Ta fiddo hollandia biyu milk and strawberry, tashi gashi ta fada tare da fiddo wata leda, katuwar gasassar kaza ce taji cabbage da kayan miya nade a foil paper.
Ta bude ikon Allah dadi za’aci Alhaji Anwar….. Ya dago Yana Yar dariya keni wallahi tuwo nake son ci miyar kuka….. Ta kalleshi ka iya tukawa ko?.
   Yayi murmushi Allah da gaske nake Ina son cin tuwo Bilkisu ya langabe Kai.
  To ka je ka siyo Mana.
Ke zakiyi mun. Zan siyo semo kiyi mun anjima…… Kam wallahi kada kasa ma ranka abinda bazaka samu ba. Zan samu yau sai naci tuwo Kuma ke zakiyi mun.
Ya bude kazar ya cire wurin cinya ya Fara ci.
  Tayi shiru kawai.
Wane kike so milk din ko strawberry?
Kai wane zaka sha?
Bani da choice as long as nidai cikina zai cika….. Ta yi dariya kawai ta dauko milk din ta Fara Sha a hankali.
Zakici kazar ko kunya kike ji?
Ta Kara Yar dariya, na ci abinci na koshi.
Me Kika ci?
Taliya muka dafa.
Zaki mun tuwon?
Zan maka Amma ka Bari sai gobe yau dai marece yayi sosai.
In siyo semo din?
Ina dashi Kar ka damu.
Good.
  Ba za kici ba da gaske?
Allah na koshi……. Zan baking baki matukar Baki sa hannu kinci ba….. Rage mun idan naje daki zanci da dare.
Mtsew, Allah ya raba ki da gardama.
  Yaci gaba da cin abinsa.
Mamaki kawai takeyi Wai me yasa maza Basu da kunya ?
Kamar ya karanci zuciyar ta ya kalleta…… Ni banjin kunyar ki.
Ta danyi dariya ….yabi kuncinta da kallo…. 
Kin San cewa kina da kyau kuwa?……. Ta kalleshi da kyau me kace?
 Yayi murmushi kina son in maimaita abinda Kika Riga kinji?
Hmm, tace.
    Samarin ki nawa?
Zaka Fara ko?
Ana zaman lafiya ka Fara tamabayoyi marassa amfani kuma azo ayi fada ko?
  Ba Kya so na sani ne?
Ina ruwanka da samari na an fada maka irin ka ce da kowace jik and jak …… Ya sa hannu ya buge Mata Baki…… Kai Kai Kai ta rike Baki…. Sai tayi kwal kwal zatayi kuka.
Ya harareta wallahi yau kikayi mun kuka Zan baki mamaki ke baki da aiki sai shagwaba.?
Gaskiya bana son abinda kakeyi mun Anwar….. Gaskiya bana son abinda kake yi mun Anwar ya maimaita Yana kwaikwayonta.
   Karfe nawa Zan zo na karbi tuwo gobe…. Zan Aiko maka Dan Allah ba sai kazo ba ko ka turo sadeeq ya karba…. Wani kallo ya jefe ta dashi kafin yace *why are you pushing me away?*
 Ba haka bane…… Haka ne.
Bazan zo ba, ki Aiko mun ya Miki ko?
Tayi murmushi eh,
   Duk ya kware tsokokin kazar ya tura Mata kasusuwa ga naki….. Ta danyi dariya wallahi kana da ci Anwar…… Ya yunkura zai Kara buge bakin ta tayi baya tana dariya.
   Tashi muje kada six tayi na gaji tunda ka gama.
Ki shanye tukun.
Tabbb bazan ya ba.
Shi yasa ba Kya kiba.
Hmm, kawai tace.
Wayarsa tayi Kara Yana dubawa ya Mike please Ina zuwa…… Ta mishi wani kallo ya nuna Mata fuskar wayar Alhaji Abbas ne kin gani?… Ya fice Yana dariya kunya ta Dan Kama ta ganin zai fassara ta.
   Ya Dan dade kafin ya dawo tana ta latsa waya taji yayi fit da ita……. 
 Bani naga suwaye samarinki…….Aka Kara kiransa a waya.
Ya kalla sai kawai yayi tsoki, sai ka bar nan ka kirata ne?…… Sai bani  kawai yayi picking yasa handsfree….. 
Ya akayi?
Haka ma zaka ce?
Baki bani amsa ba nace ya akayi ne?
Jiya an Kai maka abinci ka dawo dashi, tun jiyan nake kiranka kaki dauka Wai me yasa….. Nace kiyi mun abinci?
Sai kace sannan zaka ci?
Ke idan Baki da abin fada Ina da abinyi ya kashe wayar.
Ya kalleta kin yarda Yanzu ita ce ke damuna bani nake binta ba?.
Kai ji Ni me nace toh?
Sai kince? Rigimar ki ai nasan ta.
Wannan semester din na ganki da wani Kato wallahi sai naci …… Maganar ta makale ta zaro ido ya Mike da sauri tashi muje na rakaki.
  Ka karasa abinda kake son fada?
Yayi murmushi kawai,
Ya daure fuska ta mike ka Isa ka hanani gaisawa da mutanen arziki na?
A matsayin a na wa to da zaka Sanya mun irin wannan dokar?
Ke ya Isa tunda nayi shiru kuma Dan Allah ki kyaleni.
Suka jera suna tafiya.
   Suna karyo wata kwana su mufeeda na tahowa ta tsaya gaban sa kutumar uba Wai kana cikin school din Nan…………???????✍????

*Zainab wowo* ????????

Zan kawo muku wani true life story anjima Dan Allah Ina bukatar comments din ku please. Na gode masoyana Ina kaunarku.????

KU TABA HOTON KASA DON BADA GUDUN MUWAR KU

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button