Our website is made possible by displaying online advertisements to our visitors. Please consider supporting us by whitelisting our website.
Labarai

Yadda ‘yan sanda suka kama malama Zarah da ta rika saka wa dalibarta ‘yar shekara 4 yatsa a gaba

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta kama malamar makaranta mai shekara 32 da ke saka wa dalibarta ‘yar shekara 4 yatsa a gabanta.

 

Mahaifin yarinyar Hasan Dala ya ce a ranar 11 ga Maris ‘yarsa ta dawo daga makaranta tana kukan cewa gabanta na mata ciwokuma duk lokacin da za ta yi fitsari ta kan ji zafi.

 

“ A lokacin na yi zaton cewa kukan da ‘yata ke yi matsala ce na rashin shan ruwa sai naumarci mahaifiyarta ta rika bata ruwa tana sha.

 

“ Sai dai mahaifiyar ta fada min cewa yarinyar ta ci gaba da kuka a duk lokacin da za ta yi fitsari sannan ta kula da jini a gaban yarinyar.

 

Dala ya ce cikin gaggawa sai muka garzaya asibiti.

 

“ Da muka je babban asibiti sai likita ya bayyana mana cewa yarinyar ta ji rauni a gaban ta ta hanyar neman shigan sa da karfin tsiya.

 

“ Da muka dawo gida sai na ce wa mata ta tambayi yarinyar abinda ya faru da ita.

 

“ Mahaifiyar ta ce yarinyar ta ce malamar ta Aunty Zarah ce a makaranta take saka mata hannu a gabanta sannan ta sakata cikin hijabi tana tilastata sai ta rika tsotson nonuwan ta dole.

 

“ Da na garzaya makarantar domin ganawa da mahukuntar makarantar sai shugaban makarantar ya karya tani ya kuma kin ya bi diddigin abin.

 

“ A dalilin haka ya sa na kai kara ofishin ‘yan sanda.

 

Yan sanda sun kai kara kotu sannan kuma a wasu lokuttan da ake sauaren karar, an tsare wannan malama. Kungiyoyin kare hakkin yara da aka ci zarafinsu a jihar sun baiwa mahaifin wannan yarainyar tabbacin sai sun ga abinda ya ture wa bizu nadi game da wannan magana.

 

 

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button