YAR BAIWAH HAUSA NOVEL

YAR BAIWAH HAUSA NOVEL

Haka rayuwa tasance gwanin sha’awa salame da sirikarta bamai jin Kansu har aka wayi gari ta haifo santaleliyar yarta mai ban sha’awa kowa sai santin ‘yar yake kamar kasace ka gudu daranar suna ta zagayo aka saka mata Rukayya sunan mahaifiyar Maman Sa’idu suna kirantada ‘yar baiwa kasancewar Allah yamata hkr tun tana karama batada hayaniya ko wanason Rukayya haka ta taso cikin kulawa ga takwararta na sonta bataso taji kukanta ko wasa ake aka doketa yanxu nan zakaga Baaba ta daura ta yafa wai sai taji mafarin dukan yar lelenta abinka da yara kowa shakkar taba Yar Baiwa yake Dan kar yajaxama kanshi mita a wurin Baaba Dan har gidansu mutun takanje idai game da yar Baiwane

Luv u all my fans
Maman ussee

???? ‘YAR BAIWAH????5⃣
Maman Usman

Haka suka ci gaba da ratsa sabara har suka cinma titi sukaita tafiya tun Rukayya na kallon gari gari har ta gaji tai Bacci tasake farkawa kuma basu kaiba.

Ai kuwa basu suka isa garin sokoto ba sai misalin karfe 6 na yamma suna isa suka dauki hanyar arkila federal lowcost adai dai saitin wani gida ma dai daici yayi faking kamin nan ya umurci Rukayya data fito bayan ta fitone ya bude both ya Ciro mata yar Jakarta ya CE shiga mana ai nan gdnku ne ta dauki jakar ta shiga cikin gdn shi kuma ya bude get yasaka mortar a cikin gida San yabi bayan Rukayya.

Da sallamar sa ya shiga cikin gidan yana kwalawa Atine kira maman sajeeda maman sajeeda kin gammu sai yanxu ko oyoyo Abba cewar Abdallah yaxo da gudunsa mahaifin nasa yadaga sa sama yana dariya sweet boy ya ina mamanku da Auntynku suna kitchen cewar fadil daya fito da niyar zuwa masallaci ya gaida Abban nasa yaja hannu Abdallah suka wuce Atine tazo ta rumgumeshi sannu da zuwa my Dear kunsha Hanya ya INA yar tawa banganta ba au ai na zata tashigo tin dazufa nace da ita tashigo Dan zanshigo da mota kila ko bata gane kofar bane oho bari in dubota daga nan na wuce masallaci da an fara kiraye kiraye ko ta amsa da to.

Yar Baiwa kuwa tunda tashiga gidan takasa gane hanya kawai sai kalle kalle take ta Shafa nan ta taba can tanata mamakin ikon Allah can dai ta tsaya a wurin flawers tanata mamakin wai yau itace a birni muryar mutane datajine ya fargar da ita sai ta kewayo ta Inda ta biyo daga farko Rukayya INA kika shigane ko baki gane hanyar bane ta sadda kanta kasa shima murmushi yayi ya ja hannun ta ya kaita har cikin gidan kamin ya koma zuwa sallar magrib,

Yarta barka da zuwa ya su yaya da Baaba ta amsa suna nan kalau sunce na gaidaku harma da abu akace na kawo muku tau Rukayya bari yanxu kiyi sallah sai kiyi wanka kici abinci kinji ko bara na kira sajeeda taje dake dakinta saita nuna maki komai kinji ki saki jikinki kinji nan ma gidankune munan iyayenkine ki daukini a matsayin ummanki ki dauki Abban Abdallah a matsayin mahaifinki bakida matsalar komai kinji ta ammasa da to,

Kallon falon ta farayi Wanda aka kawatashi da kujeru masu kyau sai kayan kallon da dining area sai kuma dayan gefen store da kitchen sai dakin yara dake kusa da store gefe daya kuma room& falor ne sai dakin me gidan dake kusa da na sajeeda cikin kankani lokaci takarewa gidan kallo a ranta fadi take aljannar duniya dankari Ashe akwai ire iren wadan nan Abubuwan more rayuwa haka tab gaskiya maganar hausawane da sukace nazaune baiga gari ba.

Murya Sajeeda CE ta dawo da ita a duniyar tunanin da ta Lula yar uwata zomuje kiyi sallah kinji ta amsa da to yayinda tabi bayan sajeeda dauke da Jakarta a ka suna shiga dakin wani sanyine ya doki fuskar Rukayya tare da daddadan kamshin air fresh sajeeda taja hannunata sukashiga bayi ta muna mata komai kamin nan ta fito ta barta me Rukayya zatayi inba sake baki ba ta fara tabe tabe ba abinda yafi Jan hankalinta irin gani. Kanta datakeyi a mirror sai murmushi take can dai sajeeda taji shuru ba labarin fitowar ta gashi ita har ta gama sallah amma Rukayya. Bata fito. Ba ta kwankwasa kofa yadai Ruky naji ki shuru koda matsalane a San nan ne yadawo haiyacinta ta tuna nan wai bayan gidane ta kunna tap tayi alwala San nan tafito tana fitowa sajeeda ta bata sallaya da hijab ita kuma ta fada toilet Dan tahadawa Rukayya ruwan wanka.

Bayan ta kamala sallah ne sai ta karewa dakin kallo ba komai bed ne kawai sai drower sai dressing mirror ba laifi kam gidan ya tsaro sosai bayan tayi wanka ta fitone sai ta Shafa mai kawai sajeeda CE tabata. Body spray tashafa Dan sajeeda akwai son kamshi zata girmi Rukayya kadan Ruky cewar sajeeda kidaukeni a matsayin yar uwarki kuma kawarki nasan bamu wani saba ba Dan ko munje can Raba ba wani dadewa mukeba su mummy sun muna bayanin komai bakida wata matsala kiyi sallar isha sai muje muci abinci kinji ???? murmushi tayi hadi da yin sallah tana idawar itama sajeeda sallar tafara yi bayan takammala ne suka fita tare suka fito zuwa wajen cin abinci anan suka tarar da iyayesu har sun fara cin nasu sai Abdallah ne yace daddy wan nan CE new Sister dinmu ko ai na Santa a Raba take itace Baaba take cewa yar Baiwa ko aikuwa kowa ya fara dariya kai son ka cika surutu dayawa eah sunanta Rukayya daga yau sister Ruky kunjiko fadil yes momi suka amsa Abin yabaiwa yar baiwa sha’awa a ranta tace lallai inbaka mutu ba zakasha kallo haka akaci abinci cike da raha ana kamalawa sai kuma aka fara labarai anan ne kuma Daddy yafara yiwa Rukayya tambayoyi. Ba laifi tasan wasu wasu kuma bata amsawa sai kuma fadil da Abdallah suka CE su bacci sukeji Sajeeda ma taja Ruky sukabar mummy da daddy a falo.

Daddy yanisa gaskiya da ace Baaba bata amince ba da an cuci yariya kinga yanda takeda brain kuwa Dear Mummy tayi murmushi Allah dai yabamu ikon rike amana ameen ta amsa nimafa azo asan yanda za’ai dani Dan ah gajiye nake ya kashe mata ido daya ta murmusa da tasan halin Mijin nata,

A bagaren su Sajeeda kuwa banda tadi ba abinda akeyi sun Dade suna fira kamin nan su kayi addu’a suka kashe wuta suka kwanta Rukayya kam godiya takeyi ma Allah wai yau itace a. birni dasunan boko.

Muje zuwa kuna tare da Zeenat Yusuf maman ussee

???? ‘YAR BAIWA ????6⃣

Maman ussee

Tun da asuba mommy tashesu daga bacci Dan su yi sallah bayan sun idar ne kuma suka sake koma wa bacci kasancewar week end ne ba makaranta,
Basu suka tashiba ba sai kusan 10:am wanka suka farayi kamin nan sajeeda ta ja hannun yar uwartata domin suje cin abinci Dan tasan yanxu kowa ya tashi dayake al,adar gidan ne atare ake cin abin suna fito gaida iyayensu sunka farayi kamin. Nan Abdallah da Fadil suka gaidasu suma mommy CE tace ‘yata bawata matsala saiki Rukayya tace ba komai insha Allah daga nan kuma akayi saving din kowa yafara cin abinci amma banda Rukayya dantakasa cin abinci itasam bata saba dashi ba tafi son dumamen tuwo ko koko da kosai ko waina amma INA ita in cin wan nan kwamacalar,
Daddy ne ya kula da ita sai yakira sunanta Ruky ya.bakya cin abinci ne ta sadda kanta kasa cikin in INA tace a gida koko nakesha ko dumamen tuwo ai ko mexasuyi inba dariya ba Mummy CE tace ki Dan Dana mana kiji ai da dadi inbaxaki iya shaba to kici doyar mana tadai daure tayi spoont daya na damar miyar typeyocer din ai kuwa saita hau sha Sajeeda dariya kawai take kasa kasa ,

Bayan sun kammalane daddy yace dasu su shirya aje islamiya yaushi da kansa zai kaisu Dan ya mika Rukayya nan danan kowa yahau shiri kowa tafito cikin uniform din Islamiya Daddy yafito suka fice gabaki daya mommy kawai suka bari agidan,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Leave a Reply

Back to top button