AALIMAH HAUSA NOVELNOVELS

AALIMAH HAUSA NOVEL BOOK 1, 2,3, & 4

AALIMAH HAUSA NOVEL BY SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI

                  ******

Jirgin Ethiopian Air ya sauke su a Boston Logan International Airport da misalin karfe goma na dare agogon Massachusetts. Mummy ba ta san da dawowarsu ba a ranar don tsayin lokacin nan babu wanda ya yi magana da ita, daga su har Daddy. Su kansu ba su san dalili ba, don rashin sayen layi na kasar bai isa ya zama dalili ba, abubuwa da yawa sun janye hankalinsu a Nijar, kama daga tafiye-tafiyen da suka yi ta yi, da yadda suke zama busy cikin ‘yan uwa. Ga shi Mummy ba ta yin social media, hada layin ne ya zame musu wahala. Don haka cab suka dauka tun daga airport har kofar gidansu da ke cikin rukunin gidajen Martha’s Vineyard Estate, Mummy ta jima da kwanciya sai jin kararrawar gidan ta yi tana ta faman ruri ba kakkautawa.
Barci fal idanunta ta zo ta bude kofar, sai kawai ta gansu kamar daga sama, sai murmushi suke dukanta da shi. Sai dai wannan hargagin nasu duk babu, Yesmin ce kawai ke mata karadi, ta kuma hahhanga bayansu ba ta hango sanyin idaniyarta ba, ba ta hango tauraron zuciyarta ba, ba ta hango Ishaq dinta ba.
‘Where’s your Dad (ina Babanku)?†Shi ne abin da ta fara tambayarsu, kafin ta bi su da runguma da sumba daya bayan daya. Amma da ta zo kan Aalimah hannunta kawai ta kama, sannan ta ce mata, “Welcome back (sannu da zuwa)â€.
Zubewa ta yi a kan gwiwoyinta ta ce, “Mummy ina wuni, ya ya gida, mun same ku lafiya?â€
Sosai ta ji zuciyarta ta motsa, ta kai hannu ta daga yarinyar tsaye sannan ta rungume ta. (kyautatawa da ladabi suna canza kiyayya daga zuciyar ma’abocinta, zuwa akasinta- Takori).
Aalimah ta lumshe idonta na lokaci mai tsawo da ta ji ta yau a jikin Mummy Zulaiha. Ji ta yi kamar ABULKHAIR ne ya rungume ta. Kafin ta farfado daga duniyar shaukin Abulkhair da ta tafi a jikin Mamansa, Mummy ta sake ta, sannan ta kama hannunta tare da taya ta da daukan jakarta daya suka shige cikin gidan.
Mummy ta tambaye ta, ya ya ta samu mutanen gida? Nan ta ke gaya mata, “All our stay was in Niamey (Niamey kawai muka je)â€.
Ta jinjina kai. Suka ci gaba da hira da sauran ‘ya’yanta. Labarin zuwansu Zinder, Arlit da Tessoua suke ba ta da irin wahalar da suka sha a sahara. Dukkansu kamar an sa zare da allura an dinke musu baki, babu wadda ta yi gangancin faxa mata maganar auren Daddy, ko da da subutar baki ne. Ta tambaye su ina yake? Suka ce akwai abin da ya zaunar da shi, zai taho in ya gama.
Yau Aunty Zulaiha cike ta ke da farin ciki wanda dawowar ‘ya’yanta gare ta shi ne sila. Ba su taba daukar irin tsayin wannan lokacin ba sa tare ba. Kowa ya kasa barci, raba dare akai ana hira. Ta yi musu alkawarin kai su MIAMI RESORT shakatawa sati mai zuwa idan yayansu Abulkhair ya zo hutu.
“Wouldn’t you take us to Las Vegas?†Yesmin ta tambaya tana mai kwanciya a jikinta. Duk da baya sake musu, ba ya shiga sha’aninsu kamar Abulkhair, zuciyar Yesmin tana son Mu’azzam. Duk da suna daukar lokaci mai tsawo ba su ganshi ba ba ta manta shi. Duka Khaleesat ta kai mata, Mummy ta janye ta da sauri,
“Mu je mu yi kaniyarki a Las Vegas?â€
Rungume Yesmin Mummy ta yi tana murmushi, “He is not at Las Vegas Yesmin, he went to Bahamas. I promised taking you to him as soon as he is back (ba ya Las Vegas yanzu, ya je Bahamas. Na yi miki alkawarin kai ki wurinsa da zarar ya dawo) in ba ku koma makaranta baâ€.
Aalimah upstairs ta haye ta barsu, ta shige dakinsu. Nemo layin wayarta ta yi na gidan wayar Verizon jikinta har rawa yake ta sanya cikin wayarta, she cannot even express how much she missed him, (bazata iya fadin yadda tayi kewarsa ba) kawai ka sanya wa zuciyarka mai karatu cewa, Aalimah ta yi kewar Abulkhair yadda hasashenka ba zai iya bayyanawa ba. Duk da ta yi farin cikin ji daga bakin Mummy cewa, yana nan zuwa sati mai zuwa. Unfortunately, alkawarin da suka daukar wa Daddy ya fado mata, na haramta musu kiran juna a ranakun mako. In ta yi hakan ta ci amanar Daddy…
Da sauri ta yi jifa da wayar a kan gadonsu ta fada bisa lallausan gadon ta nitse cikin (water mattress) dinsa tana maida numfashi dai-dai. Su Basma na shigowa ta rufe idonta kamar mai barci. Barcin ta ke so ya dauke ta don ta huta daga azabtuwa da zuciyarta ke yi da tunanin Abulkhair. Basma ta hango wayarta tsakiyar gado ta dauka ta sanya mata a charging.
Washegari tun asubah da ta yi sallah ta kira Mamanta, Daddynta da Yaya Aboubacarsuka sha hira. Ta ba su labarin zuwansu Niger. A karshen wayarsu kowannensu sai ya ce da ita ta gaida Abulkhair. Kunya ta ji tana kamata, ko dai Abulkhair ya ce musu wani abu ne? Sai kuma ta ce, “Kai ba zai fadi komai ba, tunda Daddy ya ce ya bar masa komai na maganarsu a hannunsa, ba zai yi wannan azarbabin baâ€.
Ita kadai ta yi breakfast a gidan don rashin kwanciya da wuri ya sa duk ba su tashi da wuri ba. Kafin ta bar kitchen Easther ta zo suka gaisa ta bar kicin din bayan ta shirya musu karin kumallon a dining. Basma ta tayar don ta shirya, ta ce mata ba za ta iya shiga makaranta ba yau, akwai gajiya mai yawa tattare da ita. Wanka ta shiga ta fito ta shirya tsaf! Ta kira Joseph a waya ya kai ta makaranta. Sun yi karin sati daya a kan hutunsu, don haka ta tadda note mai yawa a wurin Alex da abubuwa masu yawa da suka soma tsere mata. Sai dai tana tunawa da Abulkhair da alkawarin da ta yi masa ba ta kara kebewa da Alex ba. A cikin aji suke magana gaban kowa, Khaleesat da Yesmin su da ma nasu hutun na sati hudu ne. Islamiyya kawai suke zuwa.
6/28/21, 7:33 AM – Buhainat: HAULATU 66

%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%

A haka satin ya kare musu, tana lissafe da kwanakin. Ranar juma’a wadda ta kama ranar zuwan Abulkhair kasa zaune ta yi ta kasa tsaye. Kwalliya ta yi ta har sau uku tana canzawa. Ba ta da lecture ranar, don haka ta makale a kicin da sunan taya Easther aiki. Nan kuwa masoyinta ta ke son yi wa girkin da zai yi farin ciki da shi. Waina (massa) ta soya masa wadda ta jika shinkafar tun daren jiya, ta markada da safe. Sai miyar ganye wadda ta ji tsokar naman talo-talo (Turkey). Ta dade da sanin Abulkhair na son chips wato soyayyan dankalin Turawa, ta zauna ta fere ta yi masa kyakkyawar suya. Mummy na office, Basma na school, Khaleesat da Yesmin suna Tahfiz dinsu. Gidan daga ita sai Easther, ta yi light make up kamar yadda ta saba, sannan ta zabo wani lallausan swiss lacelemon green mai stones da aka yi wa dinkin gown ta sanya.
Ita da Easther suna shirya abincin a diningaka danna kararrawar kofar gidan. Cewa Easther ta yi ta je ta bude, ita kuma da gaggawa ta gudu upstairs dakinsu. Ba ta san me ya sa ba, kunyarsa ta ke ji yau, kunya sosai, it has been long…har wata uku da rabi without them seeing each other (ba tareda sun ga juna ba)Ba ta san da fuskar da za ta kalle shi ba, ko wace tarba za ta yi masa. Fuskarta ta sanya cikin tafukanta ta zauna a bakin luntsumemen gadonsu.
“Yaa Allah! Grant me the courageâ€. Shi ne abin da ta furta a hankali.
Ya tambayi Easther da ta shigo masa da jakarsa, “Duk ina mutanen gidan?â€
Ta ce da shi babu kowa sai Aalimah. Cikin mamaki ya ce, “Sun dawo? Yaushe? Tana ina?â€
Bai kuma tsaya ta ba shi amsar ko guda daya ba, ya shiga hada steps biyu-uku, yana hawa sama.
Sai da ya murdo kofar dakin nasu ya shigo ya yi daidai da dago kanta da ta yi ta dubi saitin kofar. Kirjinta na harbawa.
Yana nan yadda yake, handsome Abulkhair. Well dressed in a Nordstromshirt and jeans trouser, masu kalar baki da fari, mai yawan gargasa a jiki, da sumar kai irin na buzayen usul. Ko bakar jakar da yake goye da ita a bayansa bai sauke ba. Sai dai kuma ya yi rama sosai. Kallo daya za ka yi masa ka san cewa ya rame din, duk da physique chest din yana nan ba abin da ya girgiza shi.
Idanunsa suka sauka cikin nata, sun dade suna kallon juna kowannensu yana sakin murmushi kafin ya saki jakar da ke bayansa kasa, ya bude mata hannayensa. Girgiza masa kai ta shiga yi alamar a’ah, ba ta san sanda ya iso gabanta ba har inda ta ke zaune ya zube gwiwoyinsa ya zauna a gabanta, ya zuba mata ido ba ya ko kiftawa. Daga bisani lumshe idanu kowannensu ya yi cikin jin wata irin nutsuwa na sauka a zuciya da gangar jikinsa.
“Kallon ya yi yawa. Babu aure a tsakaninkuâ€. Tunanin da ya shiga kan Aalimah kenan, ta mike tsaye da sauri. Shi ma mikewar ya yi ya harde hannayensa a kirjinsa yana kallonta a tsanake, ta kara kyau ta cicciko sosai, wanda ke nuna ita kam cikin kwanciyar hankalinta ta ke. Duk wahalar nan da ya yi tsayin sati hudu bai ji ko da muryarta ba, ita ba haka ba ne a tare da ita ba.
Murmushi Aalimah ta yi, “Monsieur…â€
“… Don’t dare call me Monsieur againâ€.Yakatseta. “Na ga abubuwa sabanin yadda na zace su, ni kadai na yi kewarki. Ni kadai na damu da ke…!â€
Ya karasa maganar in subdued wato cikin muryar da ke nuna how dissappointed he was. Tare da juya mata baya.
Takowa ta yi a hankali har ta zo dab da shi, sannan ta tsaya. Cikin sanyin murya ta ce,
“Ba haka ba ne. tunda muka je ban…â€
“…Ba ki sake tunawa da ni ba, balle halin da rashin ji daga gare ki zai sanya ni. Quite four weeksâ€. Ya fada yana daga yatsun hannunsa guda hudu, akwai fushi sosai cikin muryarsa.
“Daddy bai ba mu layi ba…â€. Ta fada cikin son kare zarginsa na cewa ba ta damu da shi ba.
“In ba ku da layi ba za ki iya siya ba? Ko ba za ki iya roaming naki layin ki yi amfani da shi ba a ko’ina? In duk hakan ba mai yiwuwa ba ce, ba za ki iya aron wayar wani ki kira ni ba?†Wannan karon da fada sosai yake magana.
Abin da Aalimah ta ki jini kenan, tuni idonta ya cicciko da kwallah.
Hakan ya sa Abulkhair sassauta fushinsa, ya juyo yana kallonta. Fahimtar hakan ya ba ta damar iya yin magana cikin kwantaccen sauti.
“Na ji Basma na fada wa Malam Razee cewa jarrabawa ka ke yi, kuma ka yarda da ni ko su Mamanmu ban kira ba har muka je muka dawo. The house is always full and very busy… Mun kuma yi tafiye-tafiye na garuruwa masu nisa cikin sahara inda babu network har mutum sai ya manta ma yana da waya, amma ba don na manta da kai ba, ko ba ka zuciyata. Ina dawowa na yi niyyar kiranka na tuna ba weekend ba ne kada in ha’inci Daddy. Ina tabbatar maka tunaninka na tafiya ne tare da bugun zuciyata. Babu inda zan shiga, ko wani yanayi da zan shiga da zai sa in manta ka ko na kasa tunaka…â€
Ba karamin sanyi kalamanta suka yi masa a zuciya ba. Ya manta duk wani bacin rai da ya samu kansa a ciki.
“Then give me a hug… don in tabbatar ba dadin baki kika yimin don in yarda da ke baâ€. Ya fada yana cin magani.
Dariya ta yi, ta ce, “Not nowâ€.
Kwafa ya yi ya fice daga dakin jin shigowar motar Mummy, yana ce da ita,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button