AALIMAH HAUSA NOVEL BOOK 1, 2,3, & 4
AALIMAH HAUSA NOVEL BY SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI

“Jira ba ya kisa. Da yana kisa da ban kawo yau ba!â€.
Kamar yadda Mummy ta yi alkawari washegari ta shirya musu tafiya picnic zuwa ‘Miami’.
Ko a kwanaki uku da suka karar tare a Miami Resort, Mummy ba ta fahimci komai tsakanin Abulkhair da Aalimah ba. Suna zaune a gabanta suna chatting da juna da wayoyinsu bata san me suke yi ba. Sannan daki daya ta kama musu dukkansu ita da yaran, Abulkhair na dakinsa shi kadai, sai sun fito bakin beach suke haduwa. Watakila kuma don ba ta da kurillah ne da ta gano yadda suke magana da juna cikin halittar idanunsu. Da ta hango matsananciyar soyayyar da ke kwance cikin idanun kowannensu.Sun shakata yadda suke so. A jirgin Alaska Airlines suka je Miami daga Boston a cikinsa suka dawo.
Da suka sauka a filin jirgin saman Boston Logan, Mummy ta fiddo waya ta kira Joseph. Shi ya zo ya kwashe su zuwa gida.
Tun daga harabar gidan suka ga alamun an canza wa motar Daddy matsugunni. Motar da shi kadai yake hawanta, wato Chevrolet volt. Har suna hada baki yaran da Mamansu wajen tambayar Joseph, “
Daddy ya dawo ne?â€
A nan yake gaya musu ai tun washegarin tafiyarsu suka dawo shi da second madam dinsa.
Mummy ba ta wani fahimce shi ba. Cike ta ke da dokin ganin mijin nata abin kaunarta. Amma su sun gane me Joseph ke nufi da second madam, ban da Abulkhair. Jikinsu gabadaya ya yi sanyi, don haka ba su wani fita da sauri ba, Mummy ta riga su isa kofar shiga gidan da kanta ta danna kararrawa kafin su karaso.
Wata kyakkyawar ba’abziniya kamar balarabiya, ita ta bude kofar. Idanunta cikin na Zulaiha. Ba ta fice age mate (sa’ar) Abulkhair, wato ba za ta wuce shekarunsa ba. Mai yawan fara’a da hasken idanu da na hakora. Kallon-kallo suka shiga yi, sai dai kowacce nau’in kallon da ta ke yi wa ‘yar uwarta daban yake da na ‘yar uwarta. Zulaiha kallon ya tashi daga na mamaki ya koma na tsoro, da tunanin aljana ce ta shigo mata gida, don wannan ba ta yi kama da turawa ba. Yayin da Gumsu Moiram, ke kare wa uwargidan Ishaq kallo da son tantance rukunin matan da ta ke ciki don ta san da fuskar da za ta rayu da ita.
Daddy ne ya iso kofar ya katse kallon kudan matan nasa biyu. Shi ma kansa a darare yake, amma ya karfafi kansa ko don ya zama cikakken miji a gidansa ya ce, “Sun dawo ne? Gumsu shige ciki su shigo, ina zuwaâ€.
Ta wuce ta koma ciki.
Mummy Zulaiha ta kalli Daddy cikin ido, yawu ya kafe a cikin bakinta. Kin shiga ta yi kamar yadda yaran ma suka ja tunga a bayanta. Ta ce, “First, tell me who is she?â€
Da sassauci a kan fuskarsa ya ce, “A bakin kofa, a gaban yara ki ke so mu yi magana irin wannan? Ki shigo ciki tukunnaâ€.
“Magana irin wacce?†Ta tambaya cikin danne ko ma wane irin tunani ke son shiga zuciyarta a lokacin. Hannunta kawai ya kamo ya janyo ta cikin falon su Aalimah suka biyo bayansu.
Bai cika hannun Mummy ba (upstair) ya haye da ita don su kauce ma idanun yaransu. Yayin da amarya Gumsu ta wuce dakin da Daddy ya ba ta tun zuwansu, dakin Mu’az na da, kafin ya sama mata matsugunni.
Duk wani bayani irin na nuna concern, wanke kai da kawo dalilai Ishaq Raazee ya yi ga Mummy Zulaiha don ta karbi kaddarar aurensa kamar yadda ya karbe ta, ta yarda bai yi da niyya ba, bai yi don ya tozartata ba, bai yi don ya daina sonta ba. Zulaiha ta ki fahimtar ko guda daya. Wani dan karamin hauka ne ya same ta a wannan lokacin. Ta gaya masa ta bar gidansa kenan, har abada ba zai burge ta ba sai ya auro matan Niger Republic bakidaya sannan za ta amince danginsa ba sa sonta. Ga gidansa nan, ga ‘ya’yansa nan, ya manta ya taba saninta a rayuwarsa.
Su dai su Aalimah suna zaune jigum-jigum kowacce da jakar matafiyanta a gabanta a falon kasa, tun bayan da suka shigo Abulkhair bai zauna gidan ba, ya shiga cikin gari ne tun bayan ya gaisa da amarya Gumsu da bai wan wace ce ba. Ya dai fahimci Daddy ya zo da ita ne daga Niger, sai ganin saukowar Mummy suka yi a sukwane tana hada steps biyu-uku, ta ja jakarta da suka dawo da ita ta yi waje, sai ga Daddy ya biyo bayanta da sauri shi ma. Yesmin ta bi ta da gudu, ya ce Khaleesat kada ta barta ta fita. Ta je ta riko ta tana kuka tana kiran Mummy. Wayarsa ya fiddo ya kira Abulkhair ya ce, “Kana ina?â€
Abulkhair ya amsa da cewa, ya dan fita ne amma ga shi nan ma ya shigo kwanar gidan.
Ya ce, “Ka kula da Mamanka, ga ta nan za ta dau mota ta fita. Kada ka barta ta yi tuki. Take care of herâ€.
Abulkhair ya amsa, “Don’t worry Daddyâ€.
A take kuma ya shiga hasashen abin da yake faruwa da matar da ya gani daga Nijar.
“This cannot be possibleâ€. Ya fada a fili.
Karawa motar gudu ya yi ya karaso gida, daidai Mummy na sanya jakarta a but din motarta tana rufewa. Ko daidaita parking bai yi ba ya kashe motar ya fito har da gudu ya hada ya bude mazaunin direba ya shige ya rufe. Kofar kusa da shi ta bude ta zauna tana fadin.
“Please go out, tafiya zan yiâ€.
“Ina so in raka ki ne Mummyâ€.
“Wannan karon tafiyar ba ta dawowa ba ce, please go to your Dadâ€. Sai a lokacin ne ta samu hawaye suka zubo mata.
Abulkhair ya ji wani iri a zuciyarsa, tissue din motar ya zara ya shiga tsane mata hawayen fuskarta.
“Mummy kun wuce wannan level din ke da Daddy, don Allah ki koma ku sulhunta kanku albarkacinmuâ€.
Girgiza kai ta shiga yi tare da fadin, “Ni da Babanku har abada! Kishiya ya yi min a shekarun girmana da furfurarsa da komai. Me zan yi da danginku? Tsakanina da su sai Allah ya isa!â€
“Hasashena ya tabbata gaskiya kenan?†Abulkhairi ya fadi a zuciyarsa, “Na fahimta Mummy. Amma yanzu komai zan gaya miki ba za ki fahimce ni ba. Kina bukatar nutsuwa. Yanzu ina zan kai ki?â€
Da sauri ta ce, “Las Vegasâ€.
Murmushi ya yi. A ransa yana fadin, “Wurin sanyin idaniyarta, mai share mata hawaye, mai fada mata ta ji kamar iyayenta. Kai ka ce shi ne uban ita ce ‘yarsaâ€.
A fili kuma ya ce, “Mummy, ni ma ki so ni yadda ki ke sonsa!â€.
Duk halin da Mummy Zulaiha ke ciki sai da maganar Abulkhair ta sa ta murmushi. Anya za ta so wani Da cikin ‘ya’yanta irin son da ta ke yi wa MU’AZZAM?
Bayan fitarta da kamo Yesmin da Khaleesat ta yi, Daddy dakin da Gumsu ta ke ya shiga. Kiranta ya yi suka fito tare. ‘Ya’yan na nan zaune yadda suke tun shigowarsu. Cikin yanayi na zugum-zugum sai Yesmin da ke ta kukan an hana ta bin Mummy.
Zama ya yi a kujerar da ke fuskantarsu, Gumsu za ta zauna kusa da Aalimah ya ce, ta dawo kusa da shi ta zauna. A nutse ta bi umarninsa cikin tsananin ladabi. Ya dube su bakidaya, ya ce, “Ga Antinku Moiram na taho da ita. Ina ganin hakan zai fi min sauki a kan na baro ta a can na dinga zarya. Inyaso duk karshen shekara sai mu je hutu. Basma, Aalimah da Khaleesat dukkanku na san masu hankali ne, kuma masu adalci a tsakanin iyayenku. Ban auro Gumsu-Moiram don bana son mahaifiyarku ba, sai don cika sunnar manzo sallallahu alaihi wasallam, da biyayya ga iyayena. Moiram uwarku ce, kuma gaba ta ke da ku, don haka na hore ku da da’a da biyayya a gare ta. Ku bi ta yadda za ku bi mahaifiyarku. Ke kuma Moiram ga amanar ‘ya’yana nan ki zauna da su yadda za ki zauna da wadanda ki ka haifa. Wanda ya yi miki ba daidai ba, ki sanar da ni, balle kuma dai na shaide su dukkansu masu kaunar Daddy ne ba za su taba kin abin da ya kawo ya ce nashi ne ba. Haka ne ko ba haka ne ba?†Ya maida maganar cikin sigar tambaya, ta wani bangaren lallashi.
Basma ce ta fara amsawa da, “Haka ne Daddy. Aunty Gumsu muna miki barka da zuwa cikin family dinmu. Insha Allahu za ki same mu yadda Daddy ya shaide muâ€.
Khaleesat ta dan ja fasali kafin ta ce, “Welcome Aunty Moiramâ€.
Kallo daya za ka yi mata ka san cewa tafiyar mahaifiyarta ta taba ranta. Gab ta ke da fashewa da kuka tana dai daurewa ne.
Aalimah Daddy yake kallo, yana so ita ma ta yi magana. Da farko ba ta yi niyyar cewa komai ba don a ganinta wannan abu ne da ya shafe su su kadai, ita ai ba ‘yar gidan ba ce. Amma ganin kowa ita yake kallo da saurare, sai ta ce,
“Sannu da zuwa Aunty Gumsu. I’m Aalimahâ€.
Daga nan kowacce ta fadi sunanta. Yesmin ma ta share hawaye jin kowa na fadin suna, ta ce, “Aunty I’m Yesmin, Mummy’s loveâ€.
Sosai ta ba wa kowa dariya. Gumsu ta matso ta janyo ta jikinta ta dora ta a cinyarta, cikin faransanci ta ce, “Ni kuma sunana Aunty Gumsu. Yesmin’s Auntâ€.
Yesmin ta girgiza kai cikin rashin yarda, “I’ve my Aunty, her name is Aunty Aalimahâ€. Ta fada tana nuna mata Aalimah.
Daddy ya ce, “Sun zama su biyu Yesmin, Aunty Aalimah da Aunty Gumsuâ€.
Cikin hikima Gumsu ke jansu da hira cike da kulawa da nuna kauna. Ba ta iya Hausa ba sai faransanci, abzinanci da turanci, don haka da turancin kadai suke magana da ita. Suna jin faransancin amma sama-sama amma. Tun suna dan jan jiki har suka ware musamman da ta ce kowacce ta je ta canza kaya ta zo ta daura apron su shiga kitchen tare. Abin da kowacce ta ke so shi za ta dafa mata, daga yau sun daina cin abincin mai aiki sai nata, tsakaninsu da mai aiki yanzu share-share da wanke-wanke ne kadai. She has a degree in Pastry-Art (tana da digiri kan girke-girke) kuma a gidansu za ta bude ofis dinta (tana nufin a kicin dinsu). Duk kinsu da shiga kicin kasa musa mata suka yi.
Aalimah ta ji dadin hakan sosai, don ita duk yadda za ta yi da su ba sa yarda. A ganinta da a gida Nigeria suke, duk sun isa aure. In aka aurar da su me za su tabuka a gidan miji?
Washegari suka koma makaranta dukkansu, Aunty Moiram kawai ake bari a gida, sai ko Easther in ta zo aiki, da ta gama ta ke tafiya. Abulkhair tunda ya kai Mummy gidan Mu’azzam bai dawo ba. A kwanaki uku da suka biyo baya sabo ne mai tsanani ya shiga tsakaninsu da Auntynsu Gumsu, wadda ke kula da komai nasu tsakani da Allah. Shi kansa Daddy yanzu da wuri yake dawowa gida don ya san in ya dawo zai tadda mai jiransa, abinci lafiyayye sai wanda ya zaba. Tun Gumsu na jin kunyar hawa upstairs turakan Daddy sabida idanun su Basma, har ta gaji ta zubar, inda ta fahimci yaran daban suke da irin wadanda ta sani a Nijar, wadannan masu budadden ido ne, kowa rayuwar ‘yanci yake yi babu takura. Sannan ginin benen ya fi na kasan girma da fadi sosai, a can dakin Mummy Zulaiha yake, na Daddyn da na su Basma. Inda aka batan karami ne, Mu’az ne ya zauna a dakin farkon dawowarsu gidan, kafin ya tafi jami’a a Las Vegas. Daddy ya ce zai kama mata apartment na haya a nan kusa da su, amma ta ce in dai hakan ba zai zama matsala ga Maman su Basma ba ita ta fi so ta zauna tare da su, dakin ya ishe ta, don hade yake da bayan gida, ba ta iya rayuwar kadaici ba, sai dai in zai ba ta yaran bakidaya. Shi ma zai fi son hakan, sai dai ya san Mummy ba za ta taba amincewa da kowanne a ciki ba (ba ta ‘ya’yanta ko zama tare da ita).
Ranar kwana na hudu ya yi musu sallama, ya ce zai bi bayan Mamansu. Abulkhair ne ya yi masa waya kan ya daure ya zo, don sun kasa tankwara ta shi da Mu’azzam, tana shirin barin America.
6/28/21, 7:33 AM – Buhainat: HARUNA TANKO