AL’AJABI part 1

Sati daya dai-dai da faruwar haka na fara
zuwa lecture a katafariyar makarantar AL-
KHRAMY computer training school, 2n daga
sanda na hangi makarantar a shigata ta farko
naji a raina tayi min sbd tsarinta. fasalin
gininta kawai abin kallo ne banda kuma zubin
cikinta.
Tana da ma2kar fadi da girma da kuma
wadatar dakunan kara2, akwai bangaren da
aka ware musamman don hutawa a lkcn da
ba‘a lacca wanda ya kunshi kujeru a jere daf
da wasu kyawawan bishiyu da kuma filawowi
dalilin da yasa iskar dake kadawa a wajen ta
zama me kamshi, wajen dai ya dace da
hutawa ga wanda ya debo gajiyar kara2.
Gefe guda akwai daki na musamman da aka
ware aka cikashi da littattafai kala-kala da
suka shafi darasin computer da mutum zai iya
zuwa ya bincika wanda yake so, nesa kadan
kuma akwai wurin cin abinci da aka ware
musamman ga masu bukata.
Da yake makarantar mallakar larabawa ce an
ware bangaren maza daban na mata daban.
Ga yadda ake kaffa da dalibai ake maidasu
y‘an gata.
kamar yadda aka saba ranar juma‘a 12:00pm
mun tashi zaune nake bisa wani dan
dandamali ina jiran mufida ta fito mu tafi
kaina na kasa na kurawa laptop din dake bisa
cinyoyina ido ina tayi, sallamar da naji anyi ce
tasani dakatawa kamar na dago kai na dubi
wanda yayi sallamar sbd muryar tasa ta
ratsani sosai amma sai girman kan ya motsa
na cgb da abinda nakeyi ko sallamar ban
amsa ba.
Kyakykyawan saurayin bai gajiya ba yace “ pls
na gaji da tsayuwa in zauna??“
Na cilla idona tare dago fuskata nace “ka
zauna mana idan ka gadama“.
Mai makon ya bata rai sai yayi murmushi yace
“godiya nake.“
Ya zauna bisa dandamalin nesa kadan dani,
kaina na kasa amma zuciyata na sake-sake, ji
nake kamar na dago kalli mu2min daya fara
birgeni karo na farko a rayuwata.
Jim kadan mufida ta fito ai kuwa tana kyalla
ido taga wannan saurayin dake kusa dani sai
ta bude baki tare da fadin “ Ah leader manyan
gari kaine anan haka??“
Yayi murmushin daya kara masa kyau yace
“nine wlh kinga su nazir nake jira basu fito ba
dama tare kuke da wannan??“
yayi nuni dani.
Eh tare muke da ita wlh ni take jira……
Na rufe laptop dina tare da diban littattafaina
dake ajiye a gefena na doka tsaki na wuce
nabarsu anan.“
mufida tabini da kallo kawai ta juya tare da
yin murmushi tace “sai gobe ko??“
Ya gyada kai kawai dai-dai lokacinne
abokansa su uku suka karaso wanda ya riga
kowa karasowar yace “kai wai ya akai harka
2nkari wccn yarinyar ta barka ka zauna kusa
da ita??“
Ya bishi da kallo yace “kasanta ne??“
Kwarai kuwa shugaban y‘an girman kai,
takama da gadara ta duniya kenan.“
duk sukai dariya, saurayin ya shafi gashin
kansa yace “kai! nazir yarinyar fa ba karya wlh
ta hadu“, wanda aka kira da nazir din yace “
ana fada maka matsalarta kana cewa ta
hadu??“
ya harareshi yace “ mace idan batai takama da
gadara ba waye zaiyi?? girman kan ne kawai
matsala…. ya sake bin inda muka bari a mota
da kallo.“
Ni kuwa 2nda muka tafi mufida nata bani lbrn
saurayin wai mu2min kirki ne kaza-kaza nidai
ban kulata ba, don kasa gane me take nufi da
hakan….
Ammafah….koda baxance komaiba..senaga
iya gudun grman kannata….
Yanxu ne aslin komai ze fara..sekucigaba
dabina.. amma fa bada gudu ba
Isata gida keda wuya na ketawa ma‘aikatan
gdnmu rashin mu2ncin dana saba harma sai
dana mari me baiwa fulawowi ruwa sbd yayi
sakacin watsa min ruwa duk kuwa da cewa ba
yana sane bane, kai tsaye dakina na wuce nayi
wanka naci abinci na jawo laptop dina hau
aikin dana saba.
Bayan kwanaki biyu da haduwa da
saurayinnan da ko sunansa ban sani ba ina
zaune a bakin harabar makarantar tamu a
wannan karon wayata ce kawai a hannuna
sakamakôn laptop dina tana hannun mufida,
zuwa da wurin da nayi ne yasa a gabana dai-
daikun dalibai ke isowa suna wucewa ba
ruwana dasu sai dai su wuce.
wasu lktn zakaga daliban na zuwa ne a group-
group kamar yadda al‘adar rayuwar makaranta
take.
Ana cikin haka ne group din da suka fi
kowanne shahara a makarantar suka zo
wucewa ai kuwa caraf idon saurayinnan a
kaina ya dakata tare da duban na kusa dashi
yace “nazir“.
Wanda aka kira da sunan nazir din yace
“na‘am leader.“
wuce min da jakar nan na hango mu2niyar,
nazir din ya amshi jakar ya kallo inda nake
tare da cewa “wlh leader kabi a hankali
yarinyar nan big class ce zaka sha mari fa
inkai wasa.“
ya rike kugu tare da cewa “Ta mareni?? haba
dallah sai kace a zamanin jahiliyya?? kudai ku
tsaya kusha kallo.
Ya juyo ya doso inda nake, dirar daddadar
muryarsa kawai naji a kunnena da fadin
“Amincin Allah ya tbbta a gareki ma‘abociyar
son kadaici da hutawa“.
Har ga Allah wani sanyi naji a raina amma da
yake ni din ce kawai sai kauda kai kamar
bansan me yace ba.
ya sake yin murmushi yace “kauda kanki lfy
tauraruwa me haske“, na sake hade rai na kalli
kasa.
woww!! gsky ke daban ce ban taba ganin
wanda fushi keyiwa kyau ba sai ke.
Ya fada yana kallona. Na cije lebena na
dubeshi zanyi magana yayi saurin cewa “ina
ma kiyi magana a ckn fushi daba karamin
kwarjini zaki kara ba.“
Na dan rufe idona a raina nace “BALA‘I“ na
kara hade rai nace “kaga nifa ba shashasha
bace da za‘a zo har inda nake a cikani da
suru2 idan ina son zama a wuri me hayaniya
mezai kawoni nan?
murmushinsa wanda adon fuskarsa ne ya karu
yace “gani nayi zaman kadaici bashi da dadi
shine nazo na debe miki kewa gashi kuma nayi
nasara 2nda a baya bakinki a rufe yake yanzu
kuma gashi yana motsi, na girgiza kai nace “to
bana so idan wurin ne yayi maka zan iya tashi
nabar maka“.
Ya mike tare da cewa “ kinfi karfin kina waje
ace wani ya tasheki amma ki sani babu wata
halitta dake iya rayuwa ita kadai dole tana
bukatar mataimaki Allah ne kawai yake guda
daya baya bukatar abokin tarayya amma bamu
y‘an adam masu rauni ba, yaja da baya tare
da dago min hannu yace “sai anjima“.
Na bishi da kallo ba karya fa gayen ya hadu
wlh, tun daga zubinsa har ya zuwa kalamansa
da halayensa ababan birgewa ne.
Ban jima a zaune ba na tashi na shiga class
ko break ban fito ba sai da aka tashi, abinda
ya kara bata min rai sai dana shafe min2na 15
da tashi direba na bai iso ba bare mu tafi na
zauna bisa dandamalin dana saba zama na
zaro wayata na kira direban yana dagawa na
balbaleshi da fada duk da hakurin da yake bani
sai da nayi na gaji sannan na kashe wayar
hade da doka tsaki, Allah ya wuci zuciyarki
yake tauraruwa me kyalkyali, na dago kaina
muka hada ido da saurayinnan na bata rai
naja tsaki na kauda kai.
Yace “ina bbr aminiyar taki ne na ganki ke
kadai??“
sakanni talatin na dauka sannan nace “ Ta tafi
koyo sallama “
Ya saki murmushi yace “sorry i took the
correction“
Amma me yasa duk ranar da ake kwallawa
baki nemi inuwa kin zauna ba kika zabi zama
a ckn rana??“
Cikin fusata nace “ina ruwanka? wai kai
wanne irin mu2m ne?“
Yace “bakar fata, musulmi kuma bahaushe,
bana fatan kice na takura miki don haka kinga
tafiyata, sai anjima.“
MAYE!!!!!! na fada a raina, dai-dai lkcnne
direbana ya karaso mufida ma ta fito kai tsaye
muka nufo gida, inata zabgawa direban ruwan
bala‘i ta inda na shiga ba tanan nake fita ba.
* Kwanaki uku da faruwar haka misalin
11:30am mun fito break da yake ban karya ba
naja mufida muka shiga restaurant aka kawo
mana abinci muka fara ci, bamu dauki tsawon
lkc ba muka gama.
Na kira dan matashin bakin saurayin daya
kawo mana abincin nace “yauwa nawa ne
kudinku??“ yayi yar gajeriyar dariya yace “No
ai basai kun biya ba“.
Na zabga masa harara nace “kai nifa bana
wasa da yaro nawa ne kudinku aka ce??“
nakai karshen maganar cikin tsawa.
ya girgiza kai yace “An riga an biya muku fa“,
na bishi da kallo nace “kai kada ka raina min
hankali kaga nayi kama da matsiyaciyar da
za‘a siya wa abinci?? To ai ni ko gaba daya
restaurant din naku nagadama ina iya siya
bare abincin mu2m biyu kada ka batamin rai
ka batawa kanka, nawa ne kudinku??“
fuskar saurayin ta canja yace “haramun ne a
aikina na karbi kudin mtm biyu akan abu daya
amma idan kina musu ga wanda ya biya muku
can, nabi hannunsa izuwa inda yayi min nuni
caraf idanuna suka dira akan saurayinnan me
lakabin leader na dauke kai tare da runtse
idanuna ckn takaici, shit!!! wai wannan wane
irin mtm ne?? Na tambayi kaina naja jakata
dake ajiye akan tebirin dake gabana na doshi
inda yake. Ko sanin nazo inda yake baiyi ba na
tsaya a kansa nace “mallam abin naka kuma
yana neman yayi yawa fa, daga ina dan
saurararka kuma sai raini ya shiga??
cikin rashin fahimta ya ajiye kofin juice dake
hannunsa ya dago kai yace “ raini kuma?? me
ya faru??“ Na dan harareshi nace “idan ba
haka ba meye na biya min kudin abu mafi
sauki da kowa ke iya siya irin abinci??“
Fuskarsa tayi saurin canjawa zuwa murmushi
yace “ wlh na zaci wani gingimemen laifi na
aikatawa sarauniyar matan wannan karnin,
ashe ma ba wani abu bane “ Na bishi da kallo
nace “ba wani abu ba?? kayi min wulakanci
irin wannan kace ba komai bane??“, ya juyar
da p-cap din dake kansa izuwa baya yace “Ni
banyi miki wulakanci ba a wajena kyautatawa
nayi miki sbd kin cncnci fin haka a wurina
bawai nayi hakan bane don kankantar dake
domin kin wuce haka, kuma ni a wurina kyauta
ai itace mafi girman karramawa!!
Ni kuma a wurina itace mafi girman
kankantarwa, nawa ka basu na biyaka??
Na fada dai-dai sanda na zaro wata yar
karamar jaka daga bbr jakata.
Ya dago da sauri tare da bina da wani irin
kallo tamkar bai fahimci abinda na fada ba
yayi saurin girgiza kai yace “baki yi kama da
wadda zata maida hannun kyauta baya ba sbd
nasan kinsan hakan bai dace ba, abinda nake
so ki gane shine don an baki abu kin amsa ba
yana nufin baki fi karfin abin bane.“
Na tabe baki nace “well!! naji 2nda kai
kagadama kaga zaka iya amma ka sani idan
wai kayimin haka ne don naji dadi to banji ba,
kuma bazan gode maka ba sbd bani na saka
ba.“
yayi saurin sakin murmushi yace “dama badon
ki gode min nayi miki sbd ba nema kikai ba
martabarki ce kawai takai ayi miki abinda yafi
haka.“
Na juya tare da cewa “kai dai ka jiyo“.
Sai dai a zuciyata ba karamin dadin kalamansa
naji ba sbd ni mtm ce me son a zigani.
Na nufi inda mufida take wacce har yanzu ke
zaune kawai tana kllnmu ta mike kai tsaye
muka nufi class muka cgb da lacca.
*** Wato 2nda nake a duniya ban taba ganin
mu2m irin saurayinnan ba, ya hadu ta ko‘ina
kuma ba shakka yasan abinda yake yi
kalamansa kawai ke tbbr da haka, abinda nayi
iya kokarina na gano na kasa shine me yasa
yake burgeni? me yasa yake da kwarjini a
idona? me yasa bana iya wulakantashi kamar
sauran mutane??? tambayoyin dana kasa
bawa kaina amsarsu kenan ***.
Bayan kwanaki uku da faruwar haka, na shiga
inda ban taba shiga ba library don duba wani
littafi me danake ma2kar bukatarsa da wuri,
al‘adata ban damu na duba littafi a library ba
domin waya kawai zanyi a kawo min shima
wannan din don ina bukatarsa da gaggawa ne.
Ni kadai ce a cikin wajen hakan yasa nake
neman nawa ckn kwanciyar hankali, motsin
shigowar da naji yasa nayi saurin dago kai
muka hada ido dashi nayi saurin dauke kai
daga kllnsa, yadan tsaya yana kllna lkc guda
ya tako tare da cewa “Amincin Allah a gareki
ya tauraruwar da haskenta baya disashewa“,
ko kllnsa banyi ba naci gaba da abinda nakeyi,
ya tako a hankali izuwa nesa kadan dani yace
“nayi sa‘a kenan yau zan taya sarauniyar
mata bincike me kike nema ne??“
ko kllnsa banyi ba nace “ Idon matambayi “.
Hmmmm lemme stop here kar mucika cikawa
kuce yayi yawa..!
Ya kyalkyale da dariya yace “ kema fa kina da
abin dariya gaki dai kamar ba zaki yi ba “, ya
zauna a kujerar dake nesa kadan dani ya dora
da cewa “nayi mamaki ma2ka dana duba kaf
makarantar nan ban hango tauraruwar dake
haska wannan makarantar ba ke kinga yadda
duk makarantar tayi duhu kuwa??
akwai bukatar ki fita ko don ki haskata“.
Na dauke kaina daga lttfan da nake dubawa
nace “kai!! ina yin abuna a nitse kazo zaka
rikitani wai kai wane irin mtm ne??
Kai baka rabo da NACI??
Baki, musulmi kuma bahaushe. Ya bani amsa
irin wannan a karo na biyu sannan ya dora da
cewa “ina da naci musamman idan ina so na
isar da wani sako aka kasa fahimtata.
Na tabe baki nace “sako?? wanne irin sako
kake so ka isar??“
Ya danyi shiru jimawa kadan ya mike alamar
wasa ta fita daga fuskarsa yanayi na fadar
magana da gaske ya shigeta ya taka a hankali
izuwa gaba yace “ Akwai wata kalma da ake
kira SO wacce a baya ban santa ba, ban
fahimceta ba hasalima ban yarda da ita ba.
Abinda na dauka shine ba zata iya tasiri
akaina ba sai gashi lkc guda na fahimci ashe
SO gsky ne domin tamkar kwayar virus yake
wajen saurin fadada, yana da ma2kar gudu a
cikin jini hakan kesawa yayi saurin bin sassan
jiki kwatankwacin yadda yabi jinina ya hana
min duk wani sukuni….“
Nayi saurin jan wani dan karamin tsaki nace “
To ni ina ruwana?? “
Ya juyo izuwa gareni yace “abinda kika kasa
fahimta shine na kamu da sonki duk da cewa
ban sanki ba bansan daga inda kike ba
hasalima ko sunanki ban sani ba, wannan na
daga cikin aikin SO ba ruwansa da kyau, muni,
asali ko kuma banbancin akida.
INA SONKI!!! kalmar da bana shayin fadarta a
ko‘ina domin na tbbtr shine abinda ke ckn
zuciyata.
Nayi saurin dago kaina idanuwana suka zaro
tamkar zasu fado, Kana sona??
Tambayar dana fara yi masa kenan na dora da
cewa “ Ban taba tsammanin jin wannan
kalmar daga bakinka domin wadanda suka fika
komai ma ba wanda ya taba 2nkarata da
wannan maganar…“
hakan na nuna miki irin son da nake miki
kuma yana tbbtr miki ni masoyi ne gaske bana
yaudara ba.
ya fada kyakykyawar fuskarsa na kaina.
Na ajiye littafan dake hannuna na mike da
dubeshi tare bata hade rai wanda ban taba yin
irinsa ba nace “ kaga leader kake kowa??
wasanka yana yin yawa yakamata kasani
akwai wasan da kakanni kawai ake yiwa
irinsa….
Ya katseni da cewa “Wlh ba wasa nake ba
idanuna kadai sun isa su tbbtr miki da haka,
amsa kawai nake jira daga kyakykyawan
bakinki wanda ta yiwu shine danbar fara
sabuwar rayuwata“.
Amsa kake jira?? na tambaya ina kllnsa nace “
kana tsammanin amsata zata zo a yadda kake
so ne?? to kayi kuskure, babu wata maganar
soyayya tsakanina dakai kayi gaggawar janye
wannan maganar ko don tsira da mu2ncinka a
idona.
ya gyara zamansa izuwa kallo na sosai yace “
Bazan taba janye kudirina ba sai dai idan har
zaki fada min shin wani mummunan hali
gareni da za‘a ki sona sbd dashi??
Na girgiza kai nace “ba wani mummunan hali
amma koba komai banbancin class… kuma ma
kawai bana ra‘ayin soyayya yanzu.“
amma………….
Nayi saurin katse maganar tashi da tsawa
nace “Bana sonka!! nace bana yi!! karka kara
zuwar min da zan2ka irin wadannan sbd nafi
karfin jinsu bare na yarda dasu.“
Fuskarsa ta sauya ma2ka ckn yanayin da ban
taba zaton akwai ranar dazai zama haka ba a
yadda nake ganinshi, yace “ Naji na amince
kuma na hakura amma zanso kiyi abinda idan
na tafi bazan zargeki ba sai dai na zargi
kaina.“
Kamar yaya?? na tambaya ina kllnshi.
Yace “ kiyi min duk irin jarabawar da kika
gadama a duniyar nan da kowacce nau‘in
tambaya kîka gadama idan har na fadi to
shikenan na hakura kuma bazan taba zarginki
ba sai dai na zargi kaina.“
Idan kuma ka amsa fa??
Nayi saurin tambayarsa.
Yace “sai ki dauki kaddara ki yarda muyi
soyayya.
Na bishi da kallo na koma inda nake a baya na
zauna nace “ ba tambaya daya zanyi maka ba
sai dai guda uku kuma cikin kwanaki uku a jere
idan ka fadi a daya ko kayi tsallaken rana daya
shikenan dole ka rabu dani.“
Na amince.
Ya fada ba tare da jinkiri ba….
Na bishi da kallo ckn mamakin yadda bai
tsorata da komai ba saima wani karfin gwiwa
da yake da ita, ya tsareni da ido jiran irin
tambayar da zanyi masa kawai yake.
Allah ya sani yana ma2kar birgeni sbd ya hadu
sai dai kawai ji da kai da takamata ta hanani
na amince da ainihin abinda ke zuciyata,
wacce tambaya ma yakamata nayi masa?????
Tambayar dake ta yawo a zuciyata kenan ckn
salo na nazari.
Zuwa can na dago kai nace “tambayar yau me
sauki ce ina so ka canki sunana wanda
mahaifina ya rada min, sau daya kawai zaka
fada idan ka fada ba dai-dai ba ka fadi.“
Yabi ni da kallo tare da gyara zama yace “
Sunanki?? Haba ranki ya dade ta ina kika taba
ganin an fadi sunan mtm daga ganinsa???
SUNAYE na daga abubuwan da suka fi komai
yawa a duniya don haka amsa wannan
tambayar is impossible a ko‘ina, a zatona
zakiyi min tambayane wadda kwakwalwa zatai
aiki wajen gano amsa amma ba canke-canke
ba.
Na danyi gun2n murmushi nace “daga farawa
harka fara karaya?? wannan itace mafi sauki
daga wadanda nayi maka tanadi, koka manta
kai kace duk irin tambayar da nake so??“.
ya kauda kai daga kallo na a hankali ya dan
jima baice komai ba zuwa can yace “bari
kwakwalwa tayi aiki“.
Ya mike daga inda yake zaune ya fara takawa
a hankali yana kaiwa da komowa hade da
kallona a wasu lokutan, yanayin na nuni da
zuzzurfan nazarin daya shiga, ni kuwa har
wani murmushi nake yi idan na kalli halwar
daya shiga, yau dai zan rabu da kaya.
Abinda naketa darsawa kenan domin ina da
yakini 100% bazai iya amsawa ba.
y‘an min2na kalilan ya kwashe ya juyo gareni
yace “A mafi yawan lkt suna nayin tasiri a
kamar mu2m da yanayinsa, idan har an sami
haka a kanki to ina da tbbcn sunanki ba me
guda daya bane irin sunan nan me guda biyu
ko ince tagwaye kamar “fatima-bintu, zainab-
abu, halimatus-sadiya! sai dai duk bakiyi kama
da wadannan sunayen ba.
Ya dan taka da kafarsa dake sanye da wani
kyakykyawan farin takalmi ya juyo gareni ya
kalleni na dan lkc yace
“AISHA HUMAIRA!!!!!!!“
Ya fada tare da sake mai-maitawa da fadin
“yes nafi yarda sunanki Aisha humaira….“ ya
zarce da kllna don jin abinda zan fada.
Ni kuwa 2ni idanuna sun kwalalo waje sbd
AL‘JABI, ya akai kasan sunana??
tambayar dana jefa masa kenan, fuskarsa
tadan fara saki yace “ kina nufin Na fada dai-
dai kenan??“
Bansan sanda na gyada kai alamar eh ba, ya
kawo gwauron numfashi hade da murmushi ya
koma ya zauna tare da cewa “Step one done
saura na gaba, ita dama SOYAYYA hadin Allah
ce idan yaso koke baki da ikon hanawa kuma
ina da yakini da karfin gwiwar yin nasara sbd
ina ji a jikina akwai alkhairi a tarayyarmu.“
Ya mike tare da ja da baya fuskarsa cike da
yalwataccen murmushi yace “Nima sunan
nawa me tagwayene UMAR FARUK!! sai an
jima farar tauraruwa me farin haske.
Ya juya ya fice.
Na daki tebirin dake gabana kamar na fashe
da kuka, gsky ya birgeni amma naji haushin
yadda yayi kaca-kaca da tambayata mafi
tsauri irin wannan domin ba canka kawai yayi
ba hankalinsa ne yayi aiki a wurin.
wai wannan anya kuwa mu2m ne???
dakyar na karasa abinda nazo yi na tafi class.
°ranar sai ya zamana duk na zama wata iri
2nanin irin zazzafar tambayar da zanyiwa
faruk kawai nake wacce zata gagareshi
amsawa, koda ace zan yarda da soyayyar
faruk amma bana so ya kureni, sai dai duk
tambayar data fado min sai naga kamar kwaf
daya zaiyi mata°
Washe gari 2nda na shiga makarantar bamu
hadu dashi ba har aka tashi na fito daga class
na hangi driver na sai dai dole na jira mufida
wacce bata fito ba har yanzu, na karasa jikin
motar na bude bayanta na zauna ba tare dana
rufe kofar ba saima kafafuna dana ziro waje,
salon sallamar dashi kadai keyi tasa nasan ya
iso, na dauke kai kawai.
Ya dubeni sosai yace “sorry for the late, Allah
ya taimakeni baki tafi ba da shikenan na fado
ina fatan dai baki manta tambayar da kika
tanado min ba??
Na kalleshi nace “bana so saina kayar dakai ta
karfin tsiya ka hakura kawai zaifi maka sauki
daga jin tambayar da miliyoyin mutane suka
gaza amsata masu ji da basirar, hikima da
hazakar da tafi taka..Mai-makon kalaman
yaudarar da nake amfani dasu suyi tasiri
akansa saima ya kyalkyale da dariya ya dan
taka kadan izuwa jikin kofar motar dana bude
ya dafashi da daddadar muryarsa me ratsa
zuciya yace “Humaira kenan kada kiyi
tsammanin kautar da 2nanina akan abinda
nake so kuma nake da yakinin zan sameshi,
na kasance ina da baiwar yin abubuwan da
miliyoyin mutane suka kasa, wannan kamar a
jinina ne don haka karki damu kiyi min kawai
ni abinda na dauka shine abinnan da muke yi
kamar istahara ne a gareni indai tarayyarmu
dake alherice to zan amsa tambayoyinki koda
sun kai 100, idan kuma babu alheri a ckn
soyayyarmu to bazan taba iyawa ba.“
Nabishi da kallo kawai nace:
*“ Akwai wata halitta a doron kasa wacce
yanayinta ke caccanjawa.
Idan tana karama tana tafiyane da kafa hudu,
idan ta girma kuma sai ta koma tafiya da kafa
biyu, yayin da kuma ta tsufa sai ta koma
tafiya da kafa uku, wacce halitta ce wannan???
*
Yayi saurin sakin kofar daya rike yabini da
wani irin kallon da ni kaina sai dana tausaya
masa, yaja da baya kadan lkc guda ya fara
kaiwa da kawowa a wajen hankalinsa in yayi
dubu ya tashi, na saki yalwataccen murmushi
nace “kaga faruk ba iya amsawa zakai ba
ka…….“
Ya daga min hannu yace “ karki katseni “.
Na daga ido tare da tabe baki a raina nace
‘ayi dai mugani‘.“
Ya dan dakata kamar zaiyi magana sai kuma
ya fasa ya shafi gashin kansa yace
“DANKARI!!“
Na kyalkyale da dariya kawai na dauke kai na
fara latsa wayar dake hannuna sbd a yadda
nake ji a jikina na gama dashi, sai dai ta ciki
na ciki don kuwa kirjina dif-dif kawai yake don
bansan yadda zamu karke dashi ba. tsawon
lkc muka shafe amma babu alamun ya karaya
da amsa tambayar saima dada kaimi da yake
wajen 2nani da nazari, jim kadan yadan yi nuni
da hannun tare da gyada kai ya saki murmushi
kyansa ya kara fitowa, ya tako a hankali izuwa
inda yake tsaye 2n dazu yace:
“ idan har 2nanina da nazarina sun bani dai-
dai-dai to ina da tbbcin ba kowacce halitta
bace wannan face MUTUM wato
bil‘adama.dalili kuwa mu2m sanda yana yaro
da kafa hudu yake tafiya shine RARRAFE,
gwiwoyi biyu hannaye biyu.
Yayin kuma daya girma ya iya tafiya sai ya
koma tafiya da kafa biyu kamar yadda ni dake
muke tafiya yanzu.
Lokacin kuma da mutum ya tsufa sai ya
zamana kafa biyu ba zata iya daukarsa ba sai
ya kara da sanda a matsayin kafa ta uku.“
Bansan sanda wani irin murmushi ya kwace
min ba wanda shine ya nuna ainihin abinda ke
zuciyata nake dannewa, yadda yake zano
abubuwan tamkar me karantawa a littafi ya
birgeni ma2ka.
Shima yayi murmushi tare da cewa “ zan iya
cewa wannan murmushin tayani murnar cin
nasara a karo na biyu ne??“
Na gyada kai tare da cewa “kwarai kuwa da
alama gaf kake da cina da yaki faruk akan
haka dole na jinjina maka domin kaine mu2m
na farko daka fara neman ka kureni,
murmushin da kaga nayi na tayaka murna ne
da kuma tausaya maka domin ka kai matakin
da dole kayo kasa domin gobe koda kai
aljanine baka isa ka amsa tambayar da zanyi
maka ba.“
Ya dago kansa ya fashe da dariya yace “kina
birgeni sarauniya sbd komai naki me tsari ne
kuma da karfin gwiwa hakan na daga ckn
abinda yasa muka dace da juna, idan wai kina
tsorata nine to sai ince miki kima hutar da
kanki don kuwa ma2kar ina tuna cewa
soyayyarki nake nema to zanyi abinda aljani
ma bazai iya yi ba.
Na gyara zamana dai-dai sanda na hangi
mufida tare da kokarin shigo da kafata ckn
motar nace “can dai da yawarka“.
Yayi dariya ya gyara doguwar jakar dake
rataye a kafadarsa wadda ta hadu da dressing
din jikinsa tayi masa kyau yaja da baya a
hankali yace “Ki shiryawa fara sabuwar
soyayya a gobe……“ Nayi saurin katseshi da
cewa “ko kuma ka shiryawa bakin cikin
faduwarka a gobe ba“. Ya dan dakata yace “
to shikenan zan iya cewa duk mu jira FINAL
din don ganin yadda zata kaya, ya dora
hannunsa a gefen goshinsa ckn alamu na
sarawa tamkar soja yace “sai gobe farin
ganina“…
Hmmm mumadai allah yakaimu GOBEn muji
wannan wata tanbayace haka..zata hada ko
zata raba..?!
Mufida na isowa direban wanda har ya fara
barci na daka masa tsawa ya farka ya juyar
da motar muka nufi hanyar da zata sadamu
da gida, Mufida ta dubeni tace “amma fa nayi
mamakin yadda naga kuna hira da faruk harda
dariya sai kace ba ke ba??“
Na kwantar da kaina kadan nace “manta da
wancan faruk din lamarinsa sai shi.“
mufida tayi dariya tace “Ah kidai fadi gsky
tbbs akwai wani abu“.
Ganin yadda take kokarin kureni yasa na
kautar da zancen ban bari yayi nisa ba, har na
isa gida.
Abinda na kasa ganewa game dani shine: Nidai faruk na birgeni ma2ka, komai nasa naban sha‘awa, shine kawai a duniya da bana iya tozartawa ko in wulakantashi koda nayi niyya sai hakan ya gagara yiwuwa a wajena. Ga yawan 2naninsa da nake yi a koda yaushe banda son kasancewa dashi a kowanne lkc da nake yi!! Shin wannan shine SO?? tambayar dani bansan amsarta ba kenan.
Washe gari misalin karfe tara na safe tsaye
nake a jikin wata faffadar bishiya dake harabar
makarantarmu nesa kadan da inda dalibai ke
zama, kasancewar yau an tashi da lullumi ga
iska me dadi na kadawa yasa nake jin dadin
wurin.
Gefe guda dalibai ne group-group masu hira
nayi masu kara2 nayi, Ni kuwa littafine a
hannuna ina karantawa hankalina gaba daya
tafi ga kara2n, jin sallamarsa yasa dole na
tsagaita daga kara2n da nakeyi duk da cewa
ban dago na kalleshi ba.
Amincin Allah a gareki ya ma‘abociyar son
kadaici da hutawa, Ya fada 2n yana nesa
kadan dani. Dan kwalisan saurayi kllm kara
kyau yake ya karaso inda nake tsaye yace “ina
fatan dai kin shirya tambayar dazan bige a
karo na karshe??? Nayi banza kmr banji
abinda yace ba. Yayi murmushi yace “ Kinyi
shiru kodai kin karaya ne??
Nayi yaken karfin hali nace “baka isa kasa na
karaya ba, yau so nake ka fada min ranar da
aka haifeni da watan da shekarar kayi jumulla
ka fada min shekaruna nawa??
da wata nawa??
kuma da kwana nawa??
Nayi karatu a kasar waje ka fada min wace
kasa ce kuma wacce university??
Na kumbura baki sanda nakai karshen
maganar ckn gadara da takamar cewa na
gama dashi.
Ya kura min ido kamar baisanni ba.
na kalleshi nace “yadai ka kasa cewa komai
kodai ka karaya ne??“
Yayi murmushi yace “gskyrki da kika ce ko
aljani yayi kadan ya amsa tambayarki tayau
sbd shima baisan gaibu ba amma ina so ki
sani SOYAYYA ba karya bace don haka duk
abinda naji a jikina game dake to gskyne,
zuciyata bata taba gaya min karya akanki ba
don haka zan jaraba idan har son gsky nake
miki na tbbt Allah zai bani nasara.
Ya taka kadan gaba da inda yake yace:
Irinku rayuwarku na tfy ne ckn tsari ba a
hargitse ba don haka ina da tbbs idan nace, an
saki a primary shekara shida sannan kika
samu shekaru shida a ita primary din, kin
secondary da shekaru 12.
kika gama secondary da shekaru 18 kika wuce
university kika yi shekaru 3, jumulla shekarunki
ashirin da aya (21) yanzu.
Tofa!! 2n daga nan idanuna suka zaro waje
sbd AL‘AJABI.
Ya kara gyara tsayuwa yace “idan har jikina
dai-dai yake bani an haifeki 1/6/1994 kuma
kinyi kara2 a OXFORD UNIVERSITY ta kasar
england domin itace burin duk wani dan gata
irinki.“
Hmm… Nifa tun kafin ma yakai karshen
zancen nasa bansan sanda duk abinda yake
hannuna ya subuce ba naja da baya a dan
tsorace, idan har faruk ba aljani bane to yana
harka da aljanu.
Kallo daya yayi min ya tbbr ya amsa dai-dai
ya tako inda nake tare da durkusawa ya
tattaro kayana da suka zube kasa ya mike
muka fuskanci juna yace “karki AL‘AJABI ko
mamakin abinda ya faru a maimakon haka ki
yarda Allah keson tarayyarmu, nasan kina
sona tun tuni don na dade da gani a idanunki
amma kina dannewa abnd kika manta shine
zuciya ba‘a yaudararta akan soyayya yau dai
wasa ya kare zamuyi soyayya abar kwatance
indai da tsawon rai.
na karbi laptop dina da littafina harma da
wayata daya miko min yaja da baya yace “Yes
ki shirya daga yau an fara, I LOVE YOU.“
ya juya izuwa ga abokansa dake can gefe
nesa sosai da inda nake, nabishi da kallo
kawai na kwantar da kaina a jikin bishiyar da
nake, wani murmushi ya kwace min Allah ya
sani ina so kauce-kauce ne kawai irin nawa
yau kuma karya ta kure.
Nadan dade ina cgb da tsayuwa a wurin har
zuwa sanda lkcn shiga class, ko break yau ban
fito ba yau sai da aka tashi na samu naja
mufida bamu bata lkc ba muka tafi, kai tsaye
gd muka nufa bayan da muka sauke mufida a
gdnsu.
Isowata keda wuya da yake da yunwa na
dawo kai tsaye kitchen na wuce na zubo abinci
naci nayi sallar azahar sannan na jawo laptop
dina na shîga aikina. Zaune nake bisa
luntsumemiyar kujerar falon namu na
tankwashe kafafuna laptop din na ajiye bisa
cinyoyina gaba daya hankalina ya tafi ga
laptop din sai shiga da fita nake, television
dake yi ma kasheta nayi sbd karar ta dameni.
Tunda na fara ba kakkautawa sai naji an kira
sallar la‘asar sannan na rufe na sakko tare da
shimfida darduma na jawo katon hijab dina
dana tanada musamman don yin sallah nasa.
Idarwa ta keda wuya momi ta fito falon ta
zarce izuwa kujera ta zauna ta danna remote
din dake rike a hannunta tafkekiyar T.V din
dake manne a jkn bango ta dawo taci gaba
dayi. Gamawata keda wuya na mike na koma
kan kujera na zauna na jawo laptop dina na
budeta, momi tace “aikin kenan bakya gajiya
bakya daga kafa.“ Na danyi dariya nace “momi
ai computer tayi, uhm don Allah momi dan
rage karar t.v dinnan tana takura min, momi
tace “don kina wannan shiriritar sai nabar jin
abu me muhimmanci irin wanda nake kll
yanzu??“
Nadan kumbura baki nace “ momi shiririta
kuma??“
Eh an fada shiririta ai ni wannan makarantar
taki da ita da shirme duk dayane a wurina.“
Na dan hade rai nace “ai kuwa momi ba
shirme bace don kara2n computer na daya
daga ckn mafiya tsada a duniya, kuma wlh
yadda nake jin dadin makarantar nan ko
OXFORD banji dadinta haka ba.“
Momi ta kauda kai tace “karyar banza!! yanzu
dai ki tashi kije banki ki ciro min kudi zanyi
baki gobe ba kudi a hannuna kinsan dadynki
sai jibi zai dawo,“ Na dan cilla hannu nace
“kayyyy!! momi kina gani aiki nake yi
kuma…..“
Ta katseni tana kallona da cewa “OK ba zaki je
ba kenan???“
Na mayar da kaina ga laptop din dake gabana
nace “Zanje“
to ki tashi maza ki tafi kinga yamma nayi, na
rufe laptop dina na nufi dakina kai tsaye
bathroom na shiga nayi sabon wanka na wuce
ma‘ajiyar kayana na saka wadanda suka dace
dani a yanzu na dawo ga tafkeken madubina
na zauna kujerar dake fuskantarsa zagaye dani
kayan kwalliya ne bila-adadin kala-kala.
Bayan dana gama shiryawa na kalli kaîna
bansan sanda wani murmushi ya subuce min
ba, hmmm… wato ba karya ne ba ni nakai
mafi kololuwa fagen kyau bama kyau kawai ba
komai nawa daban ne domin abinda kesa
wasu muni ni kuma kyau yake kara min bare
kuma nasa abu me kyau, Na zama
kwatankwacin zarah a ckn taurari gasu da
yawa amma daka daga kai ni zaka fara gani.
Na fito izuwa harabar kasaitaccen ygdn namu
ina takun isa, takama da gadara.
Direba ya taso da gudu tare da cewa “ranki ya
dade ina zuwa haka??“
Na harareshi nace “Ba ruwanka da yinda zanje
bani mukullin waccan motar,“ nayi nuni da
CR-V din dake nesa kadan dani.
A tsorace ya miko min tare da cewa
“amma…….“ Nayi saurin katseshi da tsawa
nace “Yau nizan tuka kaina inda nake son
zuwa ka koma kuci gaba da zaman
munafuncinku, na warci mukullin daga
hannunsa na shige motar na juyar da ita na
fice nabi titin dazai sadani da inda zanje.
Tafiyar min2na 15 nayi na iso katafaren bankin
nayi parking motata a inda aka tanada na
wuce ckn bankin, Al‘adata duk sanda nazo kai
tsaye wajen manager nake wucewa ya 2ra a
ciro min abinda nake so in juyo na fito sbd
asalinsa yaron dadyna ne.
Zuwana ofis din nasa dai-dai inda ya saba
zama nayi turus don yau wanda nake
tsammani bane ba abinda yafi kenan ba wanda
ke zaunen 2n daga zamansa dress dinsa da
komai nasa ma nasan ko waye.
Na tsaya akansa nace “ Ah!! Ya haka kuma??
Dalibi a wani wuri ma‘aikaci a wani wuri??
Faruk ya dago kai koda ganin nice sai ya saki
murmushi ya gyara zama yace “ kina mamaki
ne??
Na gyada kai dai-dai sanda na zauna a kujerar
dake fuskantarsa nace “yes!! dole da mamaki
mana kodai faruk din biyu ne bayan wanda na
sani??“
Yayi dariya yace “Nine dai wanda kika sani
don ba sunana husaini ba bare kice hassan
dina kika gani, dama kina zuwa nan ne?? Ba
tare dana dubeshi ba nace “shi yasa ma nake
mamakin ganinka don ban taba ganinka anan
ba sai yau.“
Eh gsky ba zaki ganni ba sbd ba anan
bangaren nake ba yau ne kawai na dawo nan
as temporary time kafin me kujerar ya dawo
ya karbi wurinsa, ya dago idonsa yace “cire
kudi, turawa ko kuwa kawai yawon
shakatawa???“
Na dan yi dariya nace “Ah haba yawon
shakatawa a banki kuma?? Bama dai zaka ji
abinda ya kawoni ba……
Me yasa?????
Ya tambaya yana dubana.
Nace “sbd ba wajen ka aka turoni ba wanda
aka 2roni wajensa baya nan kaga kuwa a
matsayina na y‘ar aike dole na koma na fada
idan ance na dawo wajenka na dawo!!“
Yayi murmushi yace “Nima zanyi farin ciki ki
koma din 2nda na tbbr idan aka tambayeki wa
kika tarar zaki ce masoyinki FARUK kika gane
a wajen, kinga ko tanan na fara samun shiga a
wajen momi da dadynki.“
Na zaro cak a jakata da biro na dora a tebirin
dake gabana na fara rubutawa nace “Tayaya
kake tsammanin zan fadi haka???“
Sbd nasan ba zaki taba yin karya ba.
Na tura masa cak din bayan dana gama
rubutawa ya kira wani jami‘in banki ya
umarceshi daya je ya ciro min kudin muka cgb
da hira ckn nishadi, Na dubeshi nace “Lallai
bayan kokari ma harda daukan dala ba gammo
kake yi, AIKI irinna banki + KARATU irinna
computer ba hu2 kenan???“
Ya kwantar da kansa jikin kujerar da yake kai
yace “Aikin ne ya jawo kara2n kuma duk tare
suke tafiya basu shiga lokacin hutu ba, Muna
da rauni ta bangaren masu ilmin computer
shine dalilin da yasa aka 2rani na karo sani
akanta don cgbn wannan bankin, kinji dalili.“
Na bishi da kll nace “yanzu na gano dalilin da
yasa bana ganinka in nazo, wato dan lele ne
kai a bankin.“ ya daga kai yace “of course
kamar yadda na zama dan lelen zuciyar
humaira.
Nayi saurin girgiza kai nace “Waye ya gaya
maka? Baka samu wannan damar ba ba kuma
zaka taba samu ba har abada sbd ni zuciyata
FARUK ne kawai a cknta kuma daga shi na
rufe ba wanda zan sake bawa dama ya shiga
bare ma har yayi tasiri.“
Ya dan lumshe ido ya dago kai yace “ faruk na
godiya hade da alkawarin rike amana bata
shekaru kawai ba ta HAR ABADA.“
Na jinjina kai nace “A wasu lktn alkawari nada
saukin dauka amma saukewa nada ma2kar
wahala“.
Ya gyara zama yace “Ina da tbbcn duk nauyin
alkawari ma2kar ke na daukowa shi to zan
sauke sbd ni akan SOYAYYA….. ni kaina
mamakin kaina nake yi.“
Na bishi da kallo kawai, nima na dade da
yarda yana da zafin soyayya, jim kadan jami‘in
nan ya dawo ya dora leda bisa tebirin dake
gbnmu tare da cewa “Sir, gasu an ciro.“
Ok thank you, koma bakin aikinka.
Ya 2ro minsu yace “An cika aiki.“
Na kauda kai nace “OK a takaice dai kora ta
kake ko??“
Ya girgiza kai yace “Mezai sa na koreki??
Alhalin kece fitilar dake haskawa zuciyata
hanyar daya kamata tabi?? Gani dai nayi
kawai kin samu abinda ya kawo ki.“
Na juyar da kujerar da nake kai izuwa gefe
nace “Amma ban gaji da klln faruk ba“.
Yayi murmushi yace “Shima bai gaji da ganinki
ba sai dai idan kuka kwantar da hankalinku
wannan rabuwar ta wucin gadi ce domin zaku
hadu a rayuwa ta har abada.“
Na saki murmushi kawai.
Yayi saurin matsowa gaban kujerarsa yace
“yauwa ni kuwa na manta ban karbi lambar
sarauniyar tawa ba, na dago wayar dake
hannuna kaina na kanta nace “ Ai da farko na
zaci itama zaka canka ne 2nda shi yafi komai
sauki a wajenka.“
Yace “Eh don dai kawai idan kika bani da kanki
zata fi martaba ne a idona, amma da sai dai
kawai kiji kira.
Na 2ra wayata izuwa gabansa nace “ai ko
ifritu ba yadda zaiyi ya canki lambarnan
dai~dai.“ Yayi dariya kawai ya 2ro min wayoyi
biyu na dauki tashi lambar na mike tare da
rakiyarsa na fito daga bankin.
Na dubeshi nace “kaga me girma manager nifa
bance kayi min rakiya ba.
Yayi murmushi yace “bai dace ba ace
sarauniya kamarki tana tafiya babu dogari ko
daya a gefenta.“
Na girgiza kai nace “A yanzu ai ba sarauniya
da dogari bane ke tafiya, SARKI da SARAUNIYA
ne.“
murmushi ya fadada a fuskarmu har zuwa
sanda muka karasa jikin motata, ya bude kofar
gaba tare da dora hannunsa a goshinsa ckn
salo na sarawa tamkar wani soja yace “shiga
da lfy tauraruwar taurari.“
nayi murmushi kawai na shiga na zauna ya
mayar da kofar ya rufe da yake glass din a
sauke ya dafa kofar da hannunsa biyu yace
“murmushinki ya dace da fuskarki
kwatankwacin yadda ni dake muka dace da
juna, sai mun hadu next time farin ganina.“
Ya juya ya koma ckn bankin nabishi da kallo
murmushi na tashi a fuskata har sanda na
daina ganinshi a hankali na daga glass din
motar tare da takata na nufi gd.
Wannan shine tarihin asalin fara soyayyata da
FARUK.