AL'AJABI

AL’AJABI part 1


Daga ranar ne kwanci tashi alakarmu na kara
karfi har takai soyayya me karfi ta shiga
tsakanina da FARUK wadda tafi gaban a
kwatanta, har takai mun zama ababan misali
domin bawai tsakaninmu kawai ba kowa
yasan alakarmu da kuma karfin syyrmu.“
Musamman a makarantarmu wanda kowa yayi
mamakin ganinmu tare rana tsaka muna
soyayya tamkar bani ba, daga nan ne kuma na
zama ta mutane muka fara kulla abota da
mutane daban-daban ta silar faruk.
Ban taba jin son wani bil‘adama a duniya kmr
FARUK ba kuma ban zaci zan tsinci kaina a
hakan ba, takai ga bana iya yi masa musu a
duk abinda ya fada, bana ganin rashin dai-
dainsa a duk abinda yayi, Sa‘a daya da nayi
da shima yana ma2kar sona domin idan son
da yake min baifi nawa ba to nawa bazai fi
nasa ba.
Kasantuwar kusanci da karfin syyrmu yasa har
aka fara kiranmu da sunaye daban-daban
wasu suce LAILA da MAJNUN, wasu suce
ANGELICA da MACIOLA dadai sauransu.****
FARUK ya kasance haifaffen garin kano kmr ni,
ckkken sunansa UMAR FARUK MUHAMMAD
yayi primary, secondary da university duk a
garin kano, ya karanci irin abnd na karanta
mathematic economics a BUK. Lbrn rayuwarsa
daya bani wanda nafi tausaya masa shine
kasancewarsa maraya.
Ya rasa mahaifansa 2n yana karami ta silar
hatsarin mota, ya taso ne a hannun kishiyar
mahaifiyarsa me suna hajiya amina, yana
yawan ambaton sunanta a koda yaushe domin
a cewarsa itace gatansa a duniya ita zame
masa uwa da uba ta rikeshi tamkar dan data
haifa a cknta har izuwa yanzu.
Ni kaina na yaba da halayenta da kirkinta
ranar farko da faruk ya kaini gdnsu muka
gaisa da ita, ba shakka yayi sa‘ar samunta
matsayin wacce ta rikeshi har izuwa grmnsa.
A duk ma‘aikatan gdnmu ba wanda baisan
FARUK ba domin sai da takai idan direba yakai
ni makaranta FARUK ne ke dawowa dani a
motarsa sannan ya wuce, kai harta da momi
ma tasanshi kuma tayi farin ciki da ganinsa ta
yaba dashi sosai duk da ban fada mata ba
amma ta fahimci abinda ke tsakaninmu.
Kwanci tashi har lokacin gama makarantarmu
yayi bayan tsawon lkc da muka shafe, ranar
karshe ta rufe laccarmu bayan mun fito na
nemi faruk banganshi ba mufida kuwa na can
ckn kawaye suna irin sallamar nan tasu ta
kawaye, nima nayi sallama da iya wadanda na
sani da yake yunwa nake ji kai tsaye
restaurant na dosa domin gani nake kmr
bazan iya kaiwa gd ba, zamana keda wuya na
umarci dan matashin saurayin dake jigilar
kawo abinci na gaya masa abinda nake so ya
kawo min.
A hankali FARUK ya karaso tare da zama a
kujerar dake fuskantata ya dubi me kawo
abincin tare da cewa “kai kawo min abinci da
sauri.“
Na dubeshi nace “wane irin a kawo maka
abinci baka ga na riga ka bane??“
Ya dubeni ya tabe baki yace “ina ruwana ni??“
ya juya gareshi yace “ kai aje a kawo min ka
taho da juice me sanyi.“
Na kara hade rai nace “baya yiwuwa wlh na
riga ka don haka dole ni za‘a fara kawowa.“
Me kawo abincin ya tsaya kawai ya kasa tfy
ya dubemu yace “to ai ni na rasa yadda zanyi
daku ai duk kun rudani, pls daya ya hakura a
fara kawowa daya mana.“
Faruk yace “kai manta da ita dallah jeka kawo
mana.“
na kauda kai nace “a manta dani ko a manta
dakai.“
Ya kalleni ya bata rai yace “karki ce zaki raina
ni fa don bana wasa da yarinya ranki zai baci
yanzu.“
Na zabga masa harara nace “sai dai naka ya
baci wlh.“
Ya hade rai tare da mikewa ya nuna ni yace
“KE!!“
Na mike nima na nunashi nace “KAI!!“
Muka dan dubi juna na tsawon lkc jimawa
kadan muka kyalkyale da dariya yace “gsky kin
iya fa sai kace gaske??“
Na zarce da dariya nace “Na iya koka iya gsky
dakai actor ne zaka kwashi yan kllo“.
Kai! dama ba fadan gaske kuke ba???
Me kawo abincin ya fada ckn AL‘AJABI.
Faruk yace “kai dai je ka kawo mana abinci
don sarauniyar tawa yunwa take ji.
Har aka kawo mana abincin hira muke kafin
mu gama mu tashi.
Daga ranar mukai sallama da makarantar
domin mun kammalata sai dai koda NI da
FARUK kllm sai munyi waya ta tsawon lkc, ko
mu kasance muna hira ta WHATSAPP wataran
kuma har gdnmu yake zuwa.
Haka muka cgb da rayuwa ckn jin dadi kafin
KALUBALE ya biyo bayan soyayyarmu wanda
yayi sanadin zubar hawaye na HAR ABADA.
Wannan wani QALU BALENE..?
Bari in barku haka kar kuce nacika surutu
**** BAYAN WATA BIYU DA KAMMALA
MAKARANTARMU ****
Ranar wata juma‘a da bazan manta ta ba tun
misalin 4:30pm dana kwanta a dakina na
kishingida kaina bisa lallausar katifar gadona
sanyin A-C na ratsani ta ko‘ina daga na‘urorin
sanyaya dakin, fuskata fresh ba wani abu dake
damuna musayar sakwannin soyayya kawai
muke yi ni da faruk. Murmushi ne kawai ke
tashi daga fuskata a wasu lktn ma nayi dariya
har da samba2na ni kadai, FARUK nada
barkwanci sosai abune mawuyaci kuyi magana
ta min2na dashi bai saka dariya ba.
2nda muka fara hirar ba wanda ya gajiya a
cknmu sai da aka kira sallar magariba sannan
mukai sallama a hakan ma ba‘a son ranmu ba,
Na tashi nayo alwala na fito falo momi na
zaune har ta idar da tata sallar na jawo
darduma nima, kiran sunana da tayi yasa na
dago kai tace “wai lfy naji ki kina samba2
harda dariya ke kadai?? Na danyi kasa da
kaina nace sambatu kuma??
Ah momi da Fa..ruk… muke hira….“
Nakai karshen maganar a kunyace.
Tadan harareni ckn murmushi tace “OK hira ce
tayi dadi ko??“
Na danyi dariya kawai na tayar da sallah ta.
Bayan na idar baifi da min2na biyar ba daddy
ya shigo da sallamarsa duk muka amsa masa,
zamansa keda wuya muka zarce da hira ckn
nishadi da walwala.
Zuwa can daddy ya kwantar da kansa bisa
kujerar da yake kai ya dubeni sosai yayi
murmushi yace “My daughter yanzu ne lkc
yayi da yakamata ace kin samu mijin aure
domin mutane sun dade suna cece-kuce
akanki amma na toshe kunnuwa na,
Alhamdulillahi kin samu duk kulawa daga
garemu da kuma gata lkc kuma yayi da dole
muma zamu aurar dake domin ke macece
babu wani gata na karshe daya rage muyi miki
kamar aure.
Momi tayi murmushi ta dubeni tace “gskyne
musamman da yake takai munzalin da ba
abnd ya rage mata sai aure.
hmm… Kwanci tashi kenan ba wuya yau
daddy da kansa na zancen ya aurar dani, a
raina sai naji wani dadi domin damar da nake
jira kenan gata tazo burina na daf da cika.
daddy ya gyara zama yace “akwai babban
abkn kuma aminina wanda tsohon shugaban
kasar nan ne to yana da dansa me suna tijjani.
bansan a inda ya ganki ba to dai yasa uban ya
fada min wai yana sonki kuma harma mun
tsayar da rana gobe zai zo ku tattauna ko
Allah zaisa ku fahimci juna.
Kirjina ya buga da karfi na dago kai na dubi
daddy kawai nama kasa cewa komai har ya
tashi izuwa dakinsa, na koma kan kujera na
zauna na tabe baki nace “Momi me yasa ba
zaki gaya masa ba??“
In gaya masa me???
Ta tambaya tana dubana.
Nace “amma kuma kinsan ni ina da wanda
nake so ta yaya…..“
Ta harareni tace “rufa mana baki mara kunya
da akai ki tashi kije ki fada masa mana, ko ni
kin taba fada min kina son wani??
Na kara mirgina kai nace “amma dai nasan kin
gane ai don Allah ki fada masa kinji“.
Momi ta mike tace “KE! nifa a wannan harkar
taku ba ruwana kinji.“
Ta wuce tabar falôn, nabi ta da kallo kawai na
zamar da kaina na kwanta bisa kujerar da
nake kai, to ma wai meye zaisa na dami
kaina?? Nasan dai daddy ba yadda za‘ai yayi
min auren dole.
Na dauko tantsamemiyar wayata kirar
blackberry, zuwa can na kauda wayar daga
idona a abinda daddy ya fada ya dawo min,
nayi y‘ar gajeriyar dariya.
hmm… tab! wai dan tsohon shugaban kasa,
to ai ni ko dan shugaban kasa me ci yanzu bai
isheni kll ba.
Na lalubi lambar FARUK muka dora daga inda
muka tsaya.
**Washe gari 2n misalin karfe 11:30 na safe
jerin gwanon motocin alfarma har kusan guda
goma suka shigo harabar gdnmu kowacce na
takewa y‘ar uwarta baya, a dai-dai lkcn ina
can sashin saman bene sbd inda na saba
hawa kenan duk sanda nake bukatar kadaici a
gdn namu.
Na bude labulen tagar dakin da nake ciki na
hangi fitowar wanda na tbbtr shine tijjanin sai
wani shan kamshi yake yake yana hura hanci
cabinets na take masa baya, bansan sanda na
zabga masa harara ba 2n daga nan inda nake
alamar fara jin haushi da tsanarsa 2n yanzu
kenan.
Na mayar labulen na koma kan katafaren
gadon dake madaidaicin dakin na kwanta
Allah-Allah nake kawai barci ya daukeni.
Jim kadan wata y‘ar aikin gdnmu ta hawo
izuwa inda nake ta karaso tare da cewa “Ranki
ya dade momi ce tace a gaya miki bakon ki
yazo.“
ji nayi kmr na bigeta don haushi.
Inda a dah ne da tasha tsawa da fada intayi
wasa ma harda mari amma da yake yanzu na
canja daga kwance nace “salama kyaleni kinji,
je kice mata kawai barci nake.“
Ba wata gardama kuwa ta juya.
Na jawo filo tare da gyara kwanciyata a raina
nace ‘indai nice ya hada kansa da wahala‘, ko
2nanin na fito ma bana yi. Sai bayan akalla
min2na 30 dan ni har na fara barci ma naji
momi na kiran sunana.
Na dago kai na dubeta a jikin kofar dakin ta
tsaya hannunta a kugunta ta hade rai zuwa
can tace “baki san tijjani yazo fiye da min2na
talatin yana jiranki ba?? ko ban aiko a fada
miki ba?? wato sbd wulakanci shine kinsan da
zuwansa kikayi kwanciyarki ko?? To ki tashi
maza ki sauka kasa yana falo ke yake jira.“
Momi nifa….. Zaki fito ko zaki fito ba??
ta katseni tare da tsareni da ido.
Dole tasa na mike na sakko daga kan gadon
na wuce ta gbnta kai tsaye dakina na dosa
maimakon nayi wata kwalliyar kirki saina
dakko katon hijabina wanda mafi yawa sai
zanyi sallah nake sashi nasa har jan kasa
yake ina ma ina da nikab wlh sai nasa haka
dai na fito falon fuskata ba wani annuri nayi
kicin-kicin, shi kuwa yana ganina sai ya wani
bude baki wai murmushi yayi yace “sannunki
da fitowa uwar kyawawa, ai ance min kina
shiryawa ne nace a barki ki gama a nutse.“
Na girgiza kai nace “Ba wani shiri da nake yi
kawai yanzu nayi niyyar fitowa ne.“
Ya dan daga kai tare da cewa “hakan ma ya
birgeni, Ah kamar yadda nasan an gaya miki
sunana TIJJANI nazo ne domin na sanar dake
irin son da nake miki ina fatan zaki karbi syyta
hannu bibbiyu.
hmm.. soyayya! na fada tare da dubansa sosai
nace “kaga mallam tijjani ba wani boye-boye
ko bata lkc da zamu tsaya yi, indai don
wannan ne to ba zaka taba samu ba ka ngd
da zumunci a matsayinka na dan aminin
mahaifina ka tashi ka tafi kawai.“
Nakai karshen maganar tare da kauda kai.
Da alama yayi ma2kar mamakin maganar ya
bini da kallo kawai zuwa can yace “Ah humaira
ni kuma sai nake ganin duk duniya idan ta
fuskar dace ne nafi kowa dacewa dake.“
Na dan saki murmushin rainin hankali nace
“hm.. a hakan??“
of course!! ya fada tare da dorawa.
“Idan kika duba dukkanmu y‘ay‘an masu hali
ne, mahaifina tsohon shugaban kasa ne kuma
yanzu haka yana wakiltar kasar nan a zaman
koli na majalissar dinkin duniya, ke kuma
mahaifinki shahararren dan kasuwa ne aduk
fadin afrika.
Kinga kuwa ko tanan mun dace da juna.
Na dan jinjina kai nace “Ok! dama sbd dukiya
zamu so junanmu kenan daga ranar da
dukiyar ta kare mun rabu kenan??“
Na rufawa tambayar baya da harararsa.
Abin ya kulad dashi sosai ya dago kai sosai
yace “yakamata ki sani nifa babban mu2m ne
a kasar nan me dimbin dukiya ya zama dole ki
girmama ni.“
Dukiya?? Na tambayeshi tare da dorawa da
cewa “da motoci goma ka shigo nan a
matsayinka ma na dan wanda dukiyar
al‘umma ya rike, idan ka fita ka tambaya ina
ma‘ajin gdnnan ya baka mukullin ma‘ajiyar
motoci ka debi 100 idan kana so wadanda da
zunzuru2n kudin halak ma aka siye su.“
Idanunsa suka zaro waje yace “kina nufin ni
mahaifina barawo ne??“
Na kara gyara zama nace “maganar mu2nci
kuwa babu 2nda aka wanko kafa aka taho
barar abinda ba za‘a samu ba sbd alfarma ba
zata samar dashi ba gashi kuma kudi basa iya
siyanshi shine SOYAYYAR HUMAIRA.“
ya danyi shiru jim kadan yace “yakamata muyi
magana ta fahimta pls karki manta daga nesa
nazo duk domin ke.“
Nesa?? sai ka koma ka fadawa nesa da yan
nesa abnd kaje nema baka samu ba, na mike
na dora da cewa “bata lkcn ya isa haka zan
shiga daga ciki“.
Ya dan marairaice yace “bai kamata kiyi min
haka ba yakamata ki bani dogon lkc muyi
magana ko dôn kasancewar nayo doguwar tfy.
Na juya tare da cewa “yanzu ma ai ba korarka
nayi ba, ga T.V nan kayi kllnka son ranka
amma idan ka gama karka kashe can an jima
zan kalli wani program.
Na wuce kai tsaye na doshi dakina kan ma
nabar falon shima ransa a bace ya mike ya
fice, na juya na kyalkyale da dariya KORA DA
KALAMAI kenan na tbbr bazai taba yin
marmarin dawowa ba, dama ba SON gsky ya
kawoshi ba kalarshi ma tafi kama data
munafukai don duk abinda yake fada babu
alamun har zuciyarsa hakane.
Na wuce dakina ban kara komata takansa ba
** Misalin karfe 8:00 na dare ina zaune bisa
dardumata byn na idar da sallar isha‘i, kwala
min kiran da naji ana yi kuma yasa na saurara
dakyau.
Bisa mamaki daddy ne abinda bai taba faruwa
ba kenan sai yau na jefa dardumar kan gado
na tare da nufo falon, daddy na tsaye ckn
fusata ya hade hannunsa biyu ta baya.
Na zauna tare da cewa “daddy barka da
dawo…..“
Tun kafin na karasa Ya katseni da cewa
“Menene dalilin da mu2m zai taso 2n daga
katsina domin ke, kuma na gaya miki
matsayinsa da kuma ko waye shi amma
maimakon ki karramashi saima ki
wulakantashi??
Me kika fishi??
Anji ma bakya sonsa ki mu2ntatashi mana
idan nazo sai ki fada min baiyi miki ba insan
yadda zanyi na sanarwa mahaifinsa amma sai
ki bishi da bakaken maganganu??
Shekararmu 40 da mahaifinsa ke baki isa ki
shiga tsakaninmu ba.“
Na danja da baya a kujerar da nake zaune
nace “kayi hakuri idan hakan ya bata maka rai
gsky bana sonshi ne ina da wanda nake so
kuma shima ai da laifinsa don me zai……“
Tsawa daddy yayi min a karona farko a
rayuwata da fadin “Ki rufa mana baki, ki shirya
TIJJANI ne mijinki nan bada dadewa ba za‘a
saka ranar aurenku.
Sbd girgiza bansan sanda na mike tsaye ba
kaina yayi wata juyawa sau daya, na maimaita
abnd daddy ya fada “TIJJANI ne mijina??“
Kwarai!! daddy ya fada.
Nace “koda hakan na nufin bakin cikina da
tbbt a takaici na har abada??
Daddy ya amsa da “koda hakan na nufin
mutuwarki da tbbt a kabari na har abada.“
Duk da matsananciyar damuwa data bayyana
a fuskata, idanuna suka fito waje kamar zasu
fado.
ba AL‘AJABIN mgngnunsa kawai nake ba,
amma yadda idonsa ya rufe yake zazzaga min
ruwan bala‘i ta inda ya shiga ba tanan yake
fita ba.
Ya kara da fadin “da bakinsa yake fada min
kince masa MUMMUNA, BANZA, DABBA!!
kmrsa ki fada irin wadannan maganganun??
Kawai ji nayi kmr an sare min gwiwoyi, lallai
TIJJANI munafuki ne lamba daya abin nasa
harda kage da sharri kenan??
Wasu hawayen takaici irinsu na farko a
rayuwata suka gangaro min, Na gyada kai
nace “ eh na fada masa haka sbd ya cncnci
fiye da haka ma kuma zan kara gaya masa
haka duk inda muka hadu, ckn sheshshekar
kuka nace “daddy karka manta ka bani ilmi me
yawa wanda yasa nayi wayewar da nafi karfin
ayi min auren dole.
Bana sonsa!! Bana sonsa!!
Ina da wanda nake so kuma shi zan aura bana
jin akwai wanda zai hana ni don addini ma ya
bani dama.
Kuka na ya karasa fitowa na juya izuwa
dakina, ina zuwa a hankali na zauna a gefen
gadona na hada kaina da gwiwa naci gaba da
ku kan da nake yi. Tijjani ne mijinki….
Koda hakan na nufin mu2warki da tbbt a
kabari na HAR ABADA.
Kalaman dake kara yawo a zuciyata kenan,
ashe har akwai ranar da daddy zai fada min
maganar da zata sani damuwa? Akwai ranar
da zai aje dunbin son da yake yimin a gefe ya
fada min bakaken maganganun da zasu sani
kuka??
Na dade a zaune a haka har zuwa sanda naji
an dafa ni, nayi saurin dagowa muka hada ido
da momi. Na kwantar da kaina bisa cinyoyinta
ckn kuka nace “momi daddy ya daina sona
yanzu,“ Ta dago fuskata muka fuskanci juna
tayi saurin grgz kai tace “ba haka bane ransa
ne ya baci kuma kema da laifinki bai kamata
ki yiwa TIJJANI haka ba“.
Wlh momi abnd yace na fada masa duk karya
yake yi ban fada ba.
momi tabi ni da kll tace “amma me yasa kika
cewa daddynki kin fada??“ na goge hawayena
nace “Sbd ya tbbr bana son TIJJANI.“
momi ta jinjina kai tace “yanzu dai kiyi shiru ki
share hwynki, dadynki ba wanda yake so a
duniya kmr KE duk abnd ya fada nasan bazai
taba aiwatar dasu ba.“
Na karasa goge dukkan hawayen dake idona
nace “ba lallai ya saurareni yanzu ba momi“.
Tayi murmushi tace “nafi kowa sanin halinsa
bashi da wuyar sakkowa duk irin fushin da yayi
jeki kinji??“
Na bita da kallo kawai a hankali na mike na
doshi dakinsa gwiwata a sanyaye, Zaune na
tarar dashi a tsakyr dakin bisa dardumarsa ya
idar da sallah, na karasa inda yake na zauna a
gbnsa tare da sunkuyar da kaina kasa ckn
sanyin murya nace “Daddy don Allah kayi
hakuri nasan ban kyauta ba kuma na bata
maka rai dana……“
Nayi shiru sakamakon daga min hannu da yayi
yace “Ya isa haka my daughter koda baki roka
ba ya zama dole na yafe miki kan KUSKURE
DAYA TAK!!.“
Nagode my dad na fada dai-dai sanda nayi
yunkurin mikewa.
Ya dakatar dani da cewa “wanene wanda kike
so din? kuma yaushe kuka hadu?
Ya akai bansanshi ba kuma??“
Na danyi shiru kmr bazan ce komai ba zuwa
can nace “sunansa FARUK, A makarantar
koyon kwamfuta muka hadu dashi kuma har
gdnnan yana zuwa momi ma tasanshi tfyr da
kayi ce ta tsawon watanni yasa baka sanshi
ba.“
Ya kada kai yace “Wajibi nane na baki wanda
kike so amma ki sani mafi girman gatan da
zanyi miki a yanzu shine na tbbr na zaba miki
miji nagari idan har na samu wani matsala
game dashi bazan amince dashi ba.“
Na gyada kai tare da cewa “Insha-Allahu zaka
sameshi duk yadda kake so,“ Shikenan kice
masa yazo ina nemansa“.
Na amsa da fadin “To, Sai da safe my dad.“
Kai tsaye na fice daga dakin nasa na koma
nawa, har yanzu momi na zaune bata tafi ba
na zauna gaf da ita na saki murmushi tare da
dakko hannunta na hada ckn nata nace “Momi
kinsan me?? yace in fadawa FARUK yazo yana
nemansa“
Tayi murmushi tace “Humaira kina son faruk
da yawa fa!! kina barci ma fa kiran sunansa
kike yi.“
Na danyi dariya nace “Ah haba momi a barci
kuma??“
kiyi ta fadin FARUK! FARUK!! FARUK!!!“
Na kyalkyale da dariya, momi ta mike tare da
cewa “idan zaki kwanta ki rinka kashe kwan
nan haskensa yayi yawa.“
Ok gud night my mum.
Na fada ta juya ta fice.
Na karasa kwanciya kan gadon sosai na zaro
wayata na nemi lambar faruk.
Mun dade muna hira dashi har sai da dare ya
tsala sannan mukai sllma dashi byn na sanar
dashi sakon daddy.
***FARUK bai zo gdnmu ba sai byn kwanaki
biyu misalin 5:00 na yamma, daddy na gd a
lkcn da kaina na fita na yi masa jagora izuwa
falo inda daddy ke zaune bisa kujera.
ya amsa sallamar da mukai sai dai daga
shigowarmu na lura da wani kllo da naga
daddy na yiwa faruk anya kuwa….
Ya zauna a kasa daga jkn kujerar dake
fuskantar daddy, ni kuwa mikewa nayi nabar
falon har na shiga dakina hankalina ya gaza
kwanciya na dawo da baya don jin hirar da
zata gudana tsakanin FARUK da DADDY.
daga inda na tsaya ina hangensu tare da jin
abnd suke fada.
*dai-dai sanda na tsaya faruk ne ke cewa
“…cikakken sunana Umar faruk jibrin,
mahaifina mllm jibrin dalhatu da mahaifiyata
hajiya Hauwa‘u sun rasu 2n ina karami
hakan….
Daddy yace “sunan mahaifinka mallam sunan
mahaifinta Alhaji banbanci na (1) kenan,
mahaifanka sun mu2 nata nada rai banbanci
na (2) kenan, ina sauraronka.“
Ba tare da wani damuwa ba faruk yace “na
sami yin kara2 kurewarsa shine degree dana
samu anan bayero university…
Daddy ya gyara zaman hularsa yace “Ita kuma
masters gareta a OXFORD UNIVERSITY
england, another deference kenan.“
Faruk dai bai kula ba ya karasa da fadin yanzu
haka ina aikin banki nakai matsayin activities-
director.
Daddy ya kwantar da kansa ckn kasaita bisa
kujerar da yake kai yace “Akwai banbanci me
yawa tsakaninka da y‘ata wanda ya wuce a
misalta, kasan ko danbe ake akwai wanda kll
daya zaka masa kasan yafi krfnka!! Don
haka………
Jirin da naji yana neman dibata ne yasa nayi
saurin dafe kaina nabi fuskar masoyina faruk
da kll kawai na juya da sauri na shige dakina
domin kunnuwana ba zasu jure jin
maganganun da daddy ke fada ba, don na riga
na gane inda suka sa gaba.
Ina shiga kofar na mayar na rufe nabi jikin
kofar daga sama har kasa hawaye suka
gangaro min, wai me daddy ke nufi ne?
Nima tan bayana kenan ga masu karatu..!
Medaddy kenune..?¿ Allah sa kuna fahinta..!
SABAHUL KHAIR..!
Tambayar dana fara yiwa kaina kenan
tambayoyin suka cgb da yawo a zuciyata.
wai me yasa daddy ke yimin haka ne??
Sai yanzu a lkcn da yakamata ya samar min
farin ciki fiye dana ko yaushe yake kokarin
dakile hakan??
Na dade a haka zan2kan na karo da juna a ckn
kwakwalwata, dakyar na rarrafa izuwa kan
gadona na kwanta kawai idona a bude karrr
amma 2nanin dana tafi yana kama da ace
barci nake yi, ni kaina bansan yadda zan
kwatanta ynyin da na shiga a wannan lkcn ba.
Allah sarki faruk kawai nake 2nawa wanda ban
taba ganin mu2m irinsa ba, hakurinsa kawai
ya isa yasa na kara kaunarsa dubi yadda
daddy ke fada masa bakaken maganganu
amma ko kadan ba saima ya zamana kmr
kara masa karfin gwiwa yake yi.
Ni dai duk ranar ban ma koda yi sha‘awar
fitowa daga dakina ba. washe gari kuwa da
wani azababben ciwon kai na tashi wanda ina
tsammanin ban taba yin kmrsa ba, sai duk da
wuyar da yake bani ban damu ba don ba shine
a raina ba abinda ya dame ni daban, momi
cema ta rude ta takura min akan lallai mu tafi
asibiti amma naki don ni nasan meye dalilin
ciwon. Can misalin karfe uku na rana ina
kwance abin duniya ya isheni ina son na kira
faruk amma na kasa, ringing da wayata ta
dauka yasa na dago kaina na mika hannu na
jawota ina me runtse ido sbd yadda kaina ke
sarawa.
hmm.. DAN HALAK na fada a zcyt sanda nabi
secreen din wayar da kll a hankali na daga tare
da kaita kunnana sautin muryarsa ya ratsa
jikina na kwantar da kaina bisa gadon na
amsa sllmr da fadin “W salam farin wata sha
kallo.“ Nayi saurin zarcewa da fadin “Don Allah
ya kuka karke da daddyna jiya??“
Ya danyi dariya yace “kina so kiji na jiraki
30minutes koki dan rakoni, na kira wayarki har
sau uku baki daga ba?? sannan baki kokarin
kirana ba a tsawon awannin da aka shafe da
faruwar abin??
Na dan kauda wayar daga kunnena dama a
jiyan ya kirani?? Lallai na shiga wani yanayi
da yawa. Na mayar da ita tare da cewa “uhm!
faruk kayi hakuri da wannan, amma dai don
Allah ka fada min ya akai??“ Yayi murmushi
tare da cewa to kin shirya??
Da sauri harda gyada kai nace “EH“.
Ya fara zano min hirar 2n daga farko duk
yadda na jita haka yake fada sai da yazo kan
gabar da nake so nayi saurin mikewa zaune
duk da karuwar da sarawar da kaina keyi
amma na jure duk don naji abnd banji ba, ya
karasa daga dai-dai inda na tsaya da ji da
fadin:
“…..don haka bawai zan yarda ka auri
humaira don kun dace bane ta bangaren
dukiya ko alfarma ba sai dai don kun dace da
son junanku, dôn haka lallai ka 2romin
magabatanka ckn kwanaki uku rak!! domin
muyi magana.“
Idona yayi saurin budewa kaina dake
mummunar sarawa ya daina, bugawar da
zuciyata keyi na fargabar abnd zanji ya daina,
Nayi saurin gyara zamana nace “Faruk da
gaske??“
“Kwarai“ ya amsa tare da fadin “kina mamakin
daddy ya bani ke ko da kina tsammanin zai
hanaki wanda kike so??“
Wani yalwataccen murmushi ya fadada a
fuskata farin ciki sabo ya ziyarci zucita na
koma kan gadon na kwanta tare da cewa
“Baka san yadda akai bane!!“
Sai dai idan kin fada min, yace.
Na kada kai nace “To ai ni jiya labewa nayi ina
sauraron hirarku farkonta kawai naji hankalina
ya tashi 2n jiya ba‘a dai-dai nake ba wlh.
Faruk yayi dariya yace “To banda ke wa yake
hukunci da farkon abu ba tare da yaji
karshensa ba?? Ashe ni ban sani bama
tauraruwata bata ckn walwala?? Nifa duk nayi
2nanin farin ciki ne yayi miki yawa.“
Na gyara kwanciya nace “INA!! ban taba yin
barci harda mafarki alhalin idona yana a bude
ba sai jiya, Ga wani ciwon kai da nayi me taba
kwakwalwa.“
Ya sake yin gajeriyar dariya yace “TO!! amma
ina fatan kin warke??“
Na gyada kai nace “Eh mana kana fada min
lbrnnan naji na warke.“
Dukkanmu mukai dariya.
Kina sona da yawa fa!!
Ya fada.
Na dan zunburo baki nace “kai kuma fa??“
Yace “Ni? hm.. bawai SO kawai ba akwai
KAUNA da SHAKUWA da BEGE gareki a koda
yaushe gami da ALKAWARI wanda bazai canja
ba duk rintsi duk wuya ba wani dalili na
rabuwa har mu2wa.
Na lumshe idona kawai muka cgb da hira ckn
frn ciki da walwala na tsawon lkc sannan
mukai sllma.
Sai sannan naji wata YUNWA ta taso min
domin duk yinin yau dama banci komai ba.
lallai na dawo hyycn na fada sanda na mike na
wuce izuwa kitchen.
*duk da cewa ina da shakka akan daddy amma
lkc guda duk wani bakin ciki ya fita daga
zuciyata naci gaba da harkokina ckn walwala,
2nanin zan iya rabuwa da faruk kawai na
sawa in kwanta rashin lfy ina kuma ga an
rabamu din?? Shine kawai abnd na tbbtr bazan
iya jurewa ba.
** Kamar yadda daddy ya nemi faruk ya 2ro
haka kuwa akai bayan kwanaki uku da daddare
suka zo, ina dakina na kishingida bisa tafkeken
gadona fuskata fresh ba kyalkyali kawai take
tana walkiya, zuciyata tayi fari, wayata nakan
WHATSAPP messenger muna hira da faruk.
Ina jin alamun hirarsu sama-sama sai bana
iya fahimtar abinda suke cewa, har sanda suka
gama tattaunawarsu suka tafi.
Farin ciki kmr ya kasheni idan na 2no gaf
muke da fara sabuwar rayuwa wadda nake
hangowa 2n daga yanzu, farin ckn nawa bai
yanke ba sai washe gari da naji abinda ya
wakana tsakanin daddy da iyayen faruk.
Faruk ne ke fada min ta waya, 2n da naji yana
cewa in nutsu kada hankalina ya tashi nasan
da matsala, ashe daddy rufe ido yayi ya
zabgawa iyayen faruk rashin mu2nci hade da
bakaken maganganu tare da yin alkawarin
yarsa tafi karfin tozarcin auren talaka kamar
dansu (FARUK).
Tunda ya fara fada min maganar na mike
tsaye, sanda yakai karshen lbrn kuwa zcyt ta
gama harzuka, kwakwalwata ta dimauce,
idanuna suka kada sukai jajir duk a ckn kasa
da sakanni 30.
Wayar ta subuce daga hannuna izuwa kasa ta
tarwatse komai nata ya rabu da jikinta amma
ban kula ba.
Abin kuma harda yaudara??
Wato daddy na ganin idan ya biyo ta haka
iyayen faruk su zasu fara tilastawa ya rabu
dani.
Nayi dawurwura a guri daya na juya da karfi
na bangaji kofar dakin ta bude na fito da gudu
na izuwa falon momi na tarar a zaune bisa
kujera tayi saurin dago kai tace “Lfyrki
kuwa??“
Na tsaya a gbnta nace “wai momi me yasa
daddy keyi mana haka ne??
Koda yana son rabamu ne bai kamata yaci
mu2ncin iyayen FARUK ba!!
Ashe daddy na falon rufewar da idona yayi ne
yasa na gaza ganinsa.
Yace “kaji shashasha talaka har yana da wani
mu2nci ne???
Nayi turus kawai nabi daddy da kallo wani
takaici da bakin ciki suka rufeni, wlh badon dai
ubana bane a wannan lkcn Allah ne kadai
yasan abnd zanyi.
Na dawo da baya a hankali izuwa tsakiyar
falon duk da cewa ckn fushi nake ma2ka
amma nayi kokarin sanyaya zuciyata na saita
harshena ckn salo na marairaicewa nace
“amma daddy bai kamata ka gyyto mutane da
kanka kuma ka tozarta su ba, idan har kasan
haka zakayi 2n farko gara ace FARUK din ka
fadawa amma ba iyayensa ba.“
Daddy ya matso da hularsa gbn goshinsa yace
“Ok! kina nufin muyi sulhu dashi kenan na
bashi hakuri ko??
Ai hakan da nayi shine kawai abnd yafi a
gareni domin iyayensa sunji zafin wutar
maganganun dana watsa musu dole ma su
tilasta masa ya rabu dake.“
RABUWA!!!
kalma mafi daci a gareni kenan har sai da
takai na kauda kaina kadan lkc guda na dawo
da fuskata gareshi nace “daddy talauci, arziki
ko wata daukaka duk na Allah ne shike bada
su ga wanda ya gadama a sanda yake so
kuma ba abnd ke tbbt face kudirar ubangiji
muma arzikin da muke takama dashi Allah ne
ya bamu kuma badon munfi kowa bane.“
Daddy ya kwantar da kansa jikin kujerar da
yake kai yace “EH!! nafi ki sanin wannan ai.“
Na dan matso gaba kadan nace “Ashe kenan
ba wata hujja da za‘a ce yar me kudi ba zata
zauri dan talakawa ba? tunda duk Allah ya
haliccesu ya…..“
Kaji shashanci banza!!
Daddy ya katseni tare da cewa “har akwai
wata alaka tsakanin mai arziki da talaka da
har zata kai ga aure??
Ai a doka ma hanyar jirgi daban ta mota
daban ba yadda za‘ai na siyar da akuya ta
dawo tana cimin danga ba.“
Na danyi yaken takaici nace “Indai don
wannan ne to karka damu domin dai-dai
gwargwado FARUK nada rufin asiri zai iya
sauke duk wani nauyi na dake wuyansa kuma
koma ba wannan ba ni faruk ko kasa ya kawo
min zan dafa mana mu ci.“
Bawai daddy ba har momi sai data dago kai a
firgice, daddy yayi saurin duban momi yace
“wai yarinyar nan da hankalinta kuwa??
Anya talakawan nan ba asirceta sukai ba??“
Na girgiza kai nace “bawai asiri bane hakan na
nuna zunzuru2n SON da nakewa faruk.
na durkushe bisa gwiwoyina na canja izuwa
ynyn da dole a tausaya min nace “Daddy don
grmn Allah ka taimaki rayuwata wlh faruk
nake so domin ina da tbbs akansa kayi min
komai 2n daga kuruciya har izuwa girmana
wannan shine abu na karshe da zaka samar
min wanda zan cgb da rayuwa ckn farin ciki
har abada, FARUK bashi da wani aibu na
yarda kayi duk binciken da kake so akanshi
indai ka samu aibu tare dashi nayi alkwrn zan
hakura.“
Daddy ya gyara zaman bakin glass din dake
idonsa yace “bincike??“
yayi nuni da hannunsa da cewa “Talaka har
yana bukatar wata ne?? Halin talaucin da yake
ciki kadai ya isheshi hujja, Bansan sanda kika
lalace haka ba kika manta ko y‘ar waye ke!! to
idan ke baki da hankali ni bazan biye miki ba.
Ranar auren y‘ata ina saran shugaban kasa
da kansa zai halarta, gwamnoni, sanatoci, yan
majalissu uwa-uba manyan y‘an kasuwa a
kasarnan zasu halarta kawai sai ace ina ango
aga wani talaka ya shawo kwana??
Kema kinsan bazai yiwu ba akwai masu sonki
da yawa y‘ay‘an gata ki zabi wanda kike so a
cknsu amma dole ki hakura da wannan FARUK
din.“
Ban taba sanin daddy haka yake ba sai yanzu,
a wannan lkcn ji nake duk duniya ba wanda
yakaishi rashin imani, zuciyata tayi harzukar
dana kasa dannewa na mike kawai nace “ni
kuma bazan rabu dashi ba kuma bazan auri
wani ba face shi ma2kar dai ina numfashi a
dorôn kasa, hakki nane a barni na auri wanda
nake so tunda bashi da wani aibu, hawayen
idona ya karasa zubowa ckn sheshshekar kuka
nace “wlh ko a kotu saina kwaci hakkina ba
wanda ya isa yayi min auren dole!!!!“
Na juya nabar falon, daddy yabini da kll tare
da mikewa, momi da bata tsoma mana baki ba
tace “amma Alhaji….“
Ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu
yace “tace ba wanda ya isa ko? ya kada kai
yace To zata ga isar tawa.“
Ya gyara babbar rigarsa ya wuce dakinsa.
*Daga ranar komai ya sake sakwarkwacewa
dady ya shiga amfani da damarsa da krfnsa
wajen rabani da faruk.
sai da takai ya hana faruk zuwa gdnmu, kullin
da yayi na cin mu2ncin iyayen faruk yasa
shima suka masa lamba akan lallai sai ya
rabu dani.
Soyayyarmu na karuwa kalubale na daduwa,
takaicin safe daban na rana daban na dare
daban.
Soyayya nada koguna da yawa nikam na
ruwan zafi na fada, ga tarko ya rike min kafa
hagu da dama na rasa yadda zanyi na kwance,
sama da sati daya ko a waya na daina samun
FARUK hakan ya gigitani ma2ka har sai da
takai abinci ma ya gagareni ci duk na rame
tamkar bani ba, rayuwar da ban taba zaton
zata juya min ba.
Cikin bakin ciki kmr yadda na saba nake zaune
a yau ma, zaune nake ni kadai a tafkeken
kayataccen falon gdnmu wanda yanzu ya
zame min tamkar kurkuku na zauna bisa
doguwar kujera dan karamin filo na dora bisa
cinyoyina tare da dafashi sbd 2nani idona ma
baya kiftawa hankalina 100% baya jikina.
Dafa nin da momi tayi yasa nayi firgigit
tamkar wacce ta farka daga barci nabi momi
da kallo da jajayen idanuna tamkar gauta,
nasan danniya kawai takeyi ita kanta amma
abin ya dameta.
Ta zauna tace “Humaira me yasa kike
hakane??
Kefa ba karamar yarinya bace da zaki mayar
da kuka mafi tasiri akan komai naki.
wannan 2nanin da kike yawan yi baki san
babbar illane a gareki ba??
Akan hakan gara kiyi addu‘ar Allah ya zaba
miki abnd yafi alheri.
Momi in auri faruk kawai shine alheri.
Tabini da kll tace “FARUK!! FARUK!!! FARUK!!!!
Kllm maganarki kenan???
Uhmmm nima allah ban wadda xatasoni
kaman haka..koda wata tacemin she love me
morther dt bet amma bataso wai asan tana
sona agidansu..its a true love..?lolxxx
AJABI part 13
NA ABUBAKAR A.MUH’D
tare dani—>Aßu Fer’ezerh
Duk maganar da za‘ai dake sai kinyi kokarin
dangantata da FARUK??
zaifi yi miki kyau ki hakura da soyayyarsa…
Fuskar momi ta canja ma2ka irin yanayin da ban
taba gani ba tace “amma Alhaji rashin tausayin
da rashin imanin yayi yawa wlh, a ina aka
taba….“
DAKATA!!
ya fada sanda canja fuska, yace “ince dai y‘ata
ce ko??
nina haifeta??“
Auren dole fa kake shirin yi mata!! Haka na
gadama.
Daddy yayi saurin mayar da martani. Nabi daddy
da kll wasu hawaye masu zafi tamkar
tafashashshen ruwa suka gangaro bisa kuma2na,
na mike muryata na rawa nace “Kayi zabinka da
kake ganin yayi maka, amma hkn ba lallai ya
zama zabin ubangiji ba wanda zabinsa shine
mafificin zabi don haka har yanzu banji a jkna na
rabu da FARUK ba.
Na taka a hnkl izuwa dakina.
Momi Ta kada kai tare da cewa “wannan matakin
naka Ba komai kake sonyi ba face cutar da ita
wlh, ta tashi 2n daga kuruciya bata san meye
takaici ba bata san meye damuwa ba lkc guda
kana kkrn tusa mata su toka sani idan humaira
ta haukace karka zargi kowa face kanka,“ Ya
hade rai yabita da kll kawai ya doka tsaki ya
koma kan kujera ya zauna ya zaro jaridarsa ya
fara karantawa.
*A kwana a tashi kwanaki sai kara matsowa
suke, Abu kmr wasa yana nema ya zama gaske,
ckn kankanin lkc zance ya karade ko‘ina cewar
bikina saura y‘an kwanaki ai kuwa duniya ta
dauka kmr guguwar yaki.
Ban kara tbbtrwa abin gaske bane sai da ya rage
sati daya, wasu akwatina dana iske sunyiwa
falonmu tsinke da ni kaina bansan adadinsu ba
aka ce wai kayan lefe nane, hakan ya girgizani
ma2ka lallai daddy da gaske yake.
Kmr a mafarki haka nake ganin abin gashi kuma
yana nema ya tbbt gaske, kuka 2n hawaye na
zuba har sun daina ma zuwa.
Ba komai nake hangowa ba sai rayuwar da zata
zo min a gaba ta shekaru masu yawa da zanyi
ckn takaici da damuwa watakila na har abada,
abinda na dauka shine aure shine last distination
na duniya a wurin mace walau ta dace da
rayuwar farin ciki ko takaici na har abada.
Illolin mace ta auri wanda bata so sun wuce a
misaltasu, a yadda nake jin tsanar TIJJANI wlh a
duniya ma bana son ganinsa yana rayuwa ina
kuma ga ace mu zauna har abada???
Wadanda ke waje basu san meke faruwa ba gani
suke ai hadin ya dace har tayani murna akeyi ta
waya, ciki harda wadanda bansansu bama abnd
ke kara min takaicin kenan.
Wasu ma ganin da suke yi ni na juyawa faruk
baya sbd dan uwana me kudi yazo, dadai sauran
zan2ka ire-iren wadannan.
ba wanda yasan gskyr abinda ke faruwa sbd ba
wanda na sanarwa, abune da nake zaton cewa
nafi karfinsa yazo yafi karfina, abnd nake ganin
bazai yiwu ba yake nema ya yiwu.
Lkcn daya rage saura kwanaki uku sai ya zamana
duk gdn T.V ko radio daka kamo ba sai ka samu
ana sanarwar DAURIN AURENMU, jaridu da
mujallu duk an baza gari ya dauka auren y‘ar
gata AISHA HUMAIRA ISMA‘IL yazo, harabar
gdnmu har ta fara cika da mutane anata kafa
runfunan alfarma na manyan baki da kanana.
a dai-dai sanda ya rage saura kwanaki biyu da
safe ina kwance nayi nisa a duniyar 2nanin dana
saba ban sani ba ashe mufida tazo ta shigo har
dakina kuma ta zauna ban sani ba, ta dade tana
kllna sannan ta tabani da cewa “KE“.
Na kakalo yake wanda yafi kuka ciwo nace “Ah
mufida yaushe kika zo??“
Ta bini da kll kawai tace “HUMAIRA 2nanin me
kikeyi haka??“
Nayî kasa da kaina kawai zuwa ca na girgiza kai
tare da cewa “ba komai“.
Karyane wlh, ta fada tare da dorawa da fadin
“Naji sanarwar aurenki rana tsaka, kuma abin
mamakin da wani me suna tijjani ina faruk din
kuma?? nidai a sanina shi kike so.“
Nayi kokarin hana hawayen da suka taho zuba
amma na kasa, “bakisan abnd ya faru ba??“
na tambayeta.
Tayi saurin mayar min da amsar “Na sani amma
zatona ke kika canja ra‘ayi da kanki don banyi
zaton duk duniya akwai me tilastaki ba.“
Na girgiza kai nace “Daa kenan amma yanzu ta
canja daddy ya daina kaunata ya tsaneni yafi son
mu2 da bakin ciki akan na rayu…..“
Tayi saurin rufemin baki tare da rike hannuna ckn
nata tana me grgz kai tace “karki ce haka, may
be a ganinsa gata yake sonyi miki, addu‘a
yakamata kiyita yi kawai a yanzu amma ba kuka
ba sbd ba maganin dazaiyi miki a ynzu.“
taci gaba da tsara kalamanta wasu na gane inda
ta dosa wasu ma na kasa ganewa har dai mukaî
sallama.
y‘an min2na wayata tadau ringing
Na jawota a hankali nayi arba da sunan TIJJANI!!
me kuma ya bugo ya fada min??
kmr bazan daga ba amma Na daga tare da kaita
kunnena, dariyar da yayi ce ta fara dukan
kunnuwa na, yanzu fa kin hakura ko har yanzu
kina da ja??
abnd ya rage dai bai fi awanni 48hrs ki tbbt
amaryata“.
Duk yadda naso na danne kuka na sai daya fito,
tijjani yayi dariya yace “irin dan kukan nan na
al‘ada a gurin amare ba sbn abu bane“.
Amma kai mugu ne wlh ba tausayi ko imani a
zcyrka ko kadan, Ya kara fashewa da dariya na
saki wayar ta fado bisa katifar makeken gadon da
nake kai, nayi ruf da ciki kawai na rufe idona
sautin kukan ma baya fitowa.
Tsawon lkc na kwashe a haka har sai da wayar
dake kusa dani ta sake daukan sabuwar kara,
Nayi wata irin dagowa a fusace na warto wayar a
zatona tijjani ne sai kuma fuskata ta canja.
Faruk ne nayi saurin dagawa tare da kaita
kunnena sautin sheshshekane kawai ke kaiwa da
komowa, dakyar nace “faruk shikenan mun rabu
ko??
ki jirani zanzo har gdnku yanzu.“
A firgice na dago kirjina ya buga da karfi, gdn
suwa?? karka zo zasu cutar dakai fa!!
FARUK!!
sai dai ina! tuni ya kashe wayar.
Ina ckn frgbr ne kasa da min2na ashrn naji
hayaniya na tashi a hrbr gdnmu, na tbbtr shine
bansan sanda na zabura da gudu na fita daga
dakin ba maimakon na nufi wajen rikicin amma
ba dama kai tsaye saman bene na nufa na tsaya
gaf da farfajiyar saman ina hangen abnd ke
faruwa.
Turewa, hantara harma da dukan da daka-dakan
samari majiya karfin suka farmasa ne yasa na
dafe bangon dake kusa dani ina me miko hannu
hawaye na kwarara daga idona, Tausayinsa yai
bala‘in kamani.
Faruk me yasa kazo?? Nayi tambayar badon a
bani amsa ba.
Da yake umarnin da aka basu kenan a knknn lkc
sukayi masa lilis!!
Wani layi da naga yana yi ne ya kara rikitani
karfa su kasheshi, zuciyata ta fada min.
nayi wata irin juyawa da gudu na biyo hanyar da
zata sadani izuwa inda abin ke faruwa sai dai
bisa tsautsayi dora kafata bisa matattalar benen
keda wuya na zame tare da rikitowa 2n daga
kololuwar saman benen zuwa kasa……Zamewar
ce tasa ba shiri na rikito gadan-gadan izuwa
kasa, a maimakon na mirgino ta matattakalar sai
jikina ya zamo nayo kasa kacokan. Tazarar dake
tsakanin kasa da sama nada yawa na kwarara
uban ihu wanda shine iya abinda na sani ban
kara bude ido ba sai a gadon asibiti.
Awanni masu yawa ne suka shude ina ckn yny na
suma, lktci sunyi nasarar ceto rayuwata daga
halaka bayan tsawon lkcne kuma na farfado.
A hankali idanuna suka bude tamkar wadda ta
farka daga barci ni kaina abinda ya fara fado min
kenan barci nayi, nayi saurin karasa bude idanun
nawa a sanda na tbbtr nan ba inda na sani bane
a ina nake meya faru dani??
Nayi yunkurin tashi naji an danneni a sannan ne
nabi inda nake da yanayin da nake lkc guda duk
abinda ya faru ya fado min, Na dubi kafafuna
dake mike a dai-dai gwuwoyina ansa wani
kurunbon roba daban san ko meye ba.
Sai fuskata dake kunshe da ciwuka na kujewa
dama sauran sassan jikina, Na daga kaina mukai
ido hudu da momi sai kuma MUFIDA dake zaune
a gefena.
bana jin bakina zai iya furta komai hakan yasa
banma yi yunkurin cewa komai ba, naci gaba da
jujjuya idanuna ina kallon faffadan dakin asibitin.
A wane hali faruk ke ciki kada dai ace sun
kasheshi?? Abinda yayi saurin fado min kenan,
Wasu hawaye suka gangaro min.
budewar da kofar dakin tayi da saurine yasa
muka kalli hanyar shigowar daddy ya fado a
firgice, nayi saurin dauke kaina daga kllnsa.
Ya karaso inda nake yana ganin yanayin da nake
ciki ya dafe kai tare da doka salati ya juya ga
momi a rude yace “wane hali ake ciki??
me likitan yace muku??
momi ta girgiza kai tace “Ba abinda ya fada
mana yadai ce kawai idan kazo yana son
ganinka.“ Inna-lillahi wa inna ilaihir-raji‘un.
Daddy ya sake nanatawa ya gyara zaman babbar
rigarsa tare da juyawa ya wuce izuwa ofis din
babban likitan dake kula da sashen.
Zaune lukutin bakin mu2min yake yasa faffadan
tebirin dake gabansa a gaba sai rubuce-rubuce
yake, shigowar da yaji tasa ya dago kai.
Sannu da zuwa Alhaji ya fada tare da mikewa don
girmamawa.
Doctor wane hali yata ke ciki?? meya sameta??
fuskar likitan tayi saurin canjawa ckn nuni yace
“bismillah Alhaji zauna“
Ya fada dai-dai sanda shima ya zauna.
Koda daddy baiso ba dole tasa ya zauna a
kujerar dake fuskantar likitan ckn tsananin
zakuwa da son jin abinda zai fada masa.
Likitan ya gyara zama yace “Alhaji kasan ita
fadowa daga sama irin wannan na zuwa da
abubuwa daban-daban wani lkcn a sami karaya,
rauni koma a rasa rai dungurungum.
Anyi sa‘a bata rasa ranta ba ba kuma a samu
karaya ko daya ba, hakan ya farune sbd sanda
tazo kasa da gwiwa tazo shine yasa….“
Shine yasa me…..
Daddy yayi saurin tambaya a firgice.
Likitan ya gyara zaman farin gilas din dake
idonsa yace “ Kasan a yadda gwiwa take ita ke
daukar dawainiyar iya taka kafa gaba daya ko
kuma iya karyata a zauna daidai sauransu.
Magana da gsky kokon gwiwarta dukkansu sun
sami matsala munyi kokari mun dai-daitasu daga
gocewar da sukai amma sunyi sanyi ma2ka sbd
buguwar ba y‘ar kadan bace hakan yasa zata
dau dogon lkc bata iya taka kafarta kamar yadda
kowa yake yi ba.
Doc..tor me kake…nufi ne??
Daddy yayi saurin tambayar.
Abinda nake nufi shine a yanzu kafafunta basu da
maraba dana karamin yaro don haka za‘a dau lkc
bata iya taka su ba.“
Ckn kallo me kama da harara daddy yace “kada
dai kace min ta zama gurguwa??“
Kayi hakuri alhaji amma ta zama, sai dai kawai
na wani dan lkcne zata dawo taci gaba da tafiya
kmr kowa.
Daddy baisan sanda ya cire hular dake kansa ba
ya sake doka salati tare da goge gumin dake
kwaranyo masa ya matso gbn kujerar tare da
dafa tebirin dake tsknnsa da likitan yace “doctor
yanzu ba yadda za‘ai?? kasan kudi ba matsalata
bane ko nawa ne zan iya biya kada ta zama
nakasashshiya doctor.“
Wannan ba magana bace ta kudi 2nda kokai
nasan baka taba jin inda akai dashen gwiwa ba,
dole sai dai ayi hakuri ba abnd za‘a iya yi kuma
duk inda kaje ina da tbbcin haka abin yake.
Kuma da yake ynyn larurar tata ba wadda dole
jinyarta sai a asibiti bane nan da wasu y‘an
awanni idan komai ya dai-daita muna iya
sllmrku.
ku koma gida aci gaba da kula da ita a kula kada
ku sake tayi yunkuri na taka kafar sbd a yanzu
kafarta tamkar ta jariri take.
Daddy ya dago tare da dafe kai yace “ynz
shikenan ckn y‘an awanni y‘ata ta zama
gurguwa???“
Sai dai hakuri.
Likitan ya fada.
A sanyaye daddy ya dawo dakin da muke, ina
kwance nabi fuskarsa da kll har izuwa sanda ya
zauna yaune karon farko da naga hawaye a
idonsa.
Kmr yadda likitan ya fada haka kuwa akai domin
a ranar aka sllmemu, abnd yafi bani mamaki
shine nidai bana jin wani ciwo a kafata sai dai
kawai ji da nake tamkar kafafuwan ba ajikina
suke ba.
Ko kadan bazan iya motsa su ba, KADDARA
kenan idan tazo babu me iya canjata kasa da
awa 12 na zama gurguwa.
Rayuwa ta kara juye min bangare mafi baki da
muni, na shiga kangi na bala‘i da masifa da ko a
mafarki ban taba 2nanin zan shigesu ba.
WASHE GARI tijjani yazo har gdnmu ko dakina
inda nake bai karaso ba a falo ya zauna anan
daddy yazo ya tarar dashi ya zauna tare da cewa
“TIJJANI kaga abnd ya faru ko??“
Wlh naji Alhaji.
Ya fada fuskarsa a daure, babu alamun walwala
tare dashi.
Daddy ya gyara zama yace “amma KADDARA baki
iya zuwa ba, um-u-um!! yanzu ya za‘ai tijjani??“.
Game da me fa??
Ah game da harkokin bikin nan mana kasan
duniya ta gama sanin gobe ne ga manyan baki
sun hallara an gama shirya komai bai kamata ace
anji kunya ba.“
Ban gane ba Alhaji.
Tijjani ya fada.
Daddy ya gyara zama tare da matsowa gab da
kujerar ckn kasa da murya yace “a bari a daura
auren nan idan yaso koda tarewar ne sai a daga
ya zama dai an fita kunya…“
Allah ya kiyaye!!
Tijjani ya fada tare da dorawa da fadin “wani
zancen aure gsky a barshi Alhaji me za‘ai da
HUMAIRA bayan ta zama NAKASASHSHIYA?????“
hmmm ALLAH YASA KUNA KARANTA SHIRINMU
NA “BANBANCIN SHA’AWA DA SOYAYYA”wata
kila kugane meyasa tijjani keson humaira
uhmm allah hadamu damasoyanmu nagaskiya
badon wani abu namuba..!
Dan samun posting dinmu akodayaushe
sekashiga blue rubutunnan kayi like(y)
Like(y)ßADI ßA RAI.
Tijjani yacigaba da cewa Ina dai jajanta maka
na
abnd ya samu y‘arka amma ba2n aure babu
gsky ba yadda za‘ai kamar ni ace na auri
gurguwa, da harkokina zanji ko kuma da
jiyyanta?
Kafin na taho munyi magana da dad dina
kuma ya fadawa da duk wadanda a
bangarenmu muka gayyata cewan an fasa
bikin nan.
An fasa??
Daddy ya tambaya ckn kaduwa.
kwarai na hakura da ita don bazan iya zaman
KADDARA ba, daddy ya kara sanyaya murya
yace “haba TIJJANI abin fa ba wani me muni
bane likita ya tbbtr min zata dawo normal ckn
y‘an lkt kankani.“
Tijjani ya mike tare da cewa “Alhaji kaga
tafiyata, na isar maka da sakon daya kawoni.“
Ya gyara zaman suite din jikinsa ya juya ya
nufi hanyar ficewa duk da kiran da daddy ke
masa TIJJANI!! TIJJANI!!!.
Amma ina! ko alamun waiwayowa baiyi ba
dai-dai lkcnne nida momi muka fito ina zaune
bisa keken guragu irin na zamani a hankali
momi ke 2rani har muka karaso tsakiyar falon
momi tabi kofar fitar da kll ta dawo da kllnta
ga daddy tace “Tayaya kake tsammanin zai
dawo??
Bayan dama ba don Allah yake sonta ba??
Koda ma ace anyi auren idan kaddara irin
wannan ta sameta juya mata baya zaiyi!
Amma abin tambayar me yasa shi mahaifinsa
ya ki tilasta masa ya aureta a haka??
Shi ya manta amincin dake tsakaninku??
Na tbbtr yana sane amma zai iya danne
wannan ya nunawa dansa syy abnd kai ka
kasa yi kuma ka kasa ganewa kenan.“
daddy ya 2nbuke hular kansa ya jefata kan
kujera gaba daya ya rikice dakyar ya karasa
kujerar da tafi kusa dashi ya zauna ya dago
kamar ya fashe da kuka yace “kinga shugaban
kasar CHAD yanzu haka ya sauka a hotel
kuma don daurin auren nan yazo, banda
wadanda suka 2ro wakilansu, ga sanatoci ga
gwamnoni banda abokaina manyan y‘an
kasuwa na duniya duk sun hallara abin
kunyane na 2nkaresu da maganar an fasa
bikin nan, inna-lillahi wa inna-ilaihir raji‘un….“
Yakai maganar dakyar.
Hmm… Zaune kawai nake ina binsa da kallo
bama ta tawa yake ba ta yadda zaiyi ya fita
kunya kawai yake, ba a wanne hali nake ciki
ba.
Hankalinsa ya tashi ma2ka fîye da ko yaushe
sbd abnd baiyi zaton zai faru ba ya faru,
Amma ni a wurina hkn yafi yaimin don gara na
tbbt a yanayin da nake ciki da na auri tijjani.
o-o-ooo!! Ina zansaka raina???
Daddy ya sake fada kamar zai rushe da kuka
don takaici.
Budewar da kofar tayi da karfi yasa duk
hankalinmu ya koma gareta, kamar daga sama
FARUK ya fado da saurinsa caraf muka hada
ido dashi duk da a yadda yake ba‘a farin ciki
yake ba amma bai hana annuri tashi daga
fuskarsa ba.
Yanayin tfyrsa ya canja ya fara takowa a
hankali muna klln juna.
Nayi saurin cewa “FARUK meya kawoka?? me
kazo yi??
Kayiwa Allah ka juya ka tafi karka yarda ka
kara kusanto inda nake sbd ni yanzu bani
kadai bace tafe nake da rakiyar KADDARA,
yayinda BALA‘I da MASIFA ke take min baya.
Yayi saurin girgiza kai yace “Ba wata kaddara
da zata iya sawa na gudu na barki, karki
manta Alkawarinmu na kasancewa a tare duk
tsanani duk wuya.
Da ace ba wata masifa da zata iya riskar dan
adam toda har abada ba za‘a taba iya gane
masoyi na hakika ba, sai kaddara ta afku ne
kawai ake iya gane soyayya ta zahiri da kuma
ta karya don haka yanzu ne yafi ko yaushe
cncnta na nuna miki soyayya.“
Na daga kaina sama wasu sanyayan hawaye
suka gangaro min, ya tako izuwa inda nake ya
durkusa ya dafa keken da nake kai yace
“Sannan idan zaki 2na na taba gaya miki cewa
ba ina sonki don wani abu naki bane ko don
moruwar wani abu daga gareki, ina sonki ne a
matsayinki na humaira kuma zanci gaba da
sonki har abada.“
Ya mike tare da duban daddy yace “Idan har
ka amince ni zan auri HUMAIRA a haka, zan
zauna da ita domin bazan taba guje mata ba
har abada.
Babu bukatar duniya tasan abnd ya faru da ita
bare makiyanmu su sami bakin yi mana
dariya.
Fuskar daddy tayi saurîn washewa, wani sbn
annuri ya saukar mata ya mike tare da cewa
“Lallai faruk ba‘a banza ba humaira ta yarda
da kai yau na gani da idanuna don nayi imanin
ko ni ban fika son humaira ba, laifi nane da
nayi yunkurin hana abnd Allah ya kadarta.
Nagode da kayi yunkurin rufa min asiri da
kuma masoyiyarka.
Lallai samun masoyi kamarka za‘a dade ana
tonawa.“
Faruk ya gyara tsayuwa yace “Don na rufawa
HUMAIRA asiri ba wata bajinta nayi ba domin
kaina nayiwa.“
Daddy ya gyara babbar rigarsa yace “idan
kuwa har kayi min haka nayi Alkawarin baka
dukiya me tarin yawa kuma zan dauki
nauyinku kai da ita ba abnd zaku nema ku
rasa.“
Faruk ya girgiza kai yace “bana bukatar komai
daga gareka indai akan HUMAIRA ne sbd daga
ranar da na samu humaira hakkin kula da ita
da samar mata da farin ciki akaina yake kuma
dole na saukeshi.“
Daddy yayi saurin cewa “uhm!! kaji masoyin
gaske masoyi na hakika yanzu kai kana ganin
a shirye kake??“
Faruk ya gyada kai yace “kwarai kuwa!! abinda
kawai nake so a dauke daurin auren daga
gobe a matsar zuwa jibi idan zai yiwu.“
Ah! kwarai kuwa sosai ma!!
Don dai kwana daya kawai??
Faruk ya kada kansa tare da juyowa muka
kurawa juna ido, ni kaina ya bani mafi girman
mamaki a yau, domin duk yadda nake hango
HALACCIN faruk ya wuce nan.
DAN HALAK farar fuska farar zuciya.
Har yanzu hawaye ke kwararowa daga
idanuna har na fara hango yadda sabuwar
rayuwarmu zata kasance duk da cewa bata zo
mana a yadda muke so ba.
Ya goge hawayen dake idonsa har ya taka
izuwa bakin kofa sai ya juyo yace “kayi hakuri
amma Sai kasa an kwashe wadancan
gardawan banzan daka tara a bakin gate
izuwa asibiti sbd ta karfin tsiya na bigesu na
shigo nan.“
daddy yayi saurin gyada kai yace “KARKA
DAMU KAYI DAI-DAI.“
Ya juya tare da yimin klln karshe ta wani irin
salo kmr zaiyi magana amma sai ya fice, nabi
daddy da kll na durkusar da kaina na fashe da
kuka kmr raina zai fita.
Kukan na abubuwa da yawa ne da suka
cunkushe zuciyata, ko yunkurin rarrashina ma
ba wanda yayi zuwa jimawa MUFIDA tazo a
lkcn ina daki ta zauna a falo momi ta zayyane
mata duk abnd tijjani ya fada da tsananin
mamaki ta dago kai tace “amma TIJJANI anyi
tsinannen mu2m mara mu2nci da bashi da
imani a zcyrsa, ynz momi shikenan komai ya
rushe???
Ta girgiza kai tace “FARUK yazo kuma yace
yaji ya gani ya amince ba abnd za‘a fasa, sai
dai nifa ina jin tsoron al‘amarin nan sosai.“
MUFIDA tadan yi gun2n murmushi tare da
girgiza kai tace “babu abin tsoro momi, 2nda
nake ban taba ganin soyayya irin ta HUMAIRA
da FARUK ba, wlh momi yadda kika san da
son junansu aka haliccesu 2n fil‘azal.
A kyalesu kawai tbbs da abinda Allah yake nufi
a tryyrsu.“
Momi ta kauda kanta kawai ba tare data sake
cewa komai ba, mufida ta mike ta nufo dakina.
Kwance nake na kishingida akan makeken
gadona na zubawa kafafuna ido hawaye na
zuba daga idanuna, mufida tadan rufe min ido
tare da bina da kll tace “haba HUMAIRA meye
haka??
kuka bashi da wani muhimmanci a gareki sbd
bai isa ya dawo miki da abnd kika rasa ba, a
zatona farin ciki zan tarar kinayi Allah ya
kadarta abnd kike buri.“
ckn sheshsheka nace “Dole nayi kuka sbd shi
kadai ne abnd zan iya yi a yanzu, ba haka
naso rywr aurenmu tazo mana ba.“ Shi kuma
Allah haka yaso.
Tayi saurin fada tare da dorawa “Allah na
tsara abubuwansa ne yadda yaso ba wanda ya
isa ya canjasu, amma dai na tbbtr ko a yayane
zakiyi dauwamammen farin ckn zama da faruk
wannan kawai ya wadatar.“ Haka dai kalamai
irin nata na RARRASHI tayi ta jerowa.
*Faruk kuwa isarsa gida keda wuya ya fadawa
wadda take uwa da ubansa kudirinsa da kuma
taimakon da yake so tayi masa, duk da cewa
bata fiya fushi ba amma a wannan karon sai
data canja.
Tabishi da kll tace “A zatona kana da hankali
amma ka canja.
HUMAIRA ce kadai mace a duniya??
ka manta abnd suka yi maka kenan??
sai yanzu da suka shiga wani yanayi sun kada
gabas da yamma basu da me rufa musu asiri
shine suka taho wurinka kai sbd kafi kowa
wauta ka yarda ko??
kai wannan bai zama abin kunya bama a
gareka??
Mutumin nan bakai kawai ya wulakanta ba
harda iyayenka wadanda su zasuyi maka
wakilci su kuma dame zaka 2nkaresu da yarda
su dawo su shige maka gaba??
2n wuri ka cire wannan daga ranka don bame
yiwauwa bane.
Fuskarsa ta canja kmr ya fashe da kuka yace
“amma ummi mahaifinta ne yayi mana laifi ba
humaira ba, ni kuma yanzu humaira nace zan
aura ba mahaifinta ba laifin wani yana shafar
wani ne??
Ta dan zaro masa ido tace “EH yana shafa!
indai ina na isa na fada ka dauka to ka rabu
dasu da y‘arsu idan a jibin kake son auren ni
ina da wadda zan baka gasu nan da yawa
ma.“
Faruk yayi saurin girgiza kai yace “ni
HUMAIRA nake so ita zan aura kota yaya ni
naji na gani 2nda ni zan zauna da ita.“
Ta daga kai sama tace “TO!! tashi daga kasa
ka dawo kan kujera muyi magana 2nda ka
zama abokina.“
Ummi ba haka nake nufi ba amma…
Ta katseshi da fadin “wai Yaushe ka koyi
musu da gardama irin wannan to bani da lkcn
musayar zance akan maganar banza tashi ka
tafi.“
Dole tasa ya mike ckn nuni da hannu yace
“don Allah ummi ki…..“
Ka bacemin nace ko??
Ta katseshi.
Ya saki hannunsa kawai ya bita da kallo
kawai.
“Allah ya wuci zcyrki.“
Ya fada sanda ya wuce izuwa sashinsa,
bangarene me zaman kansa da falo guda gefe
guda kuma ga dakinsa gdn nasu dai-dai
gwargwado na rufin asiri ne.
Ya zauna jim kadan ya zaro wayarsa ya lalubi
lambar bbn abokinsa NAZIR yana dagawa yace
“kazo gida don Allah yanzu ina son ganinka,
…………
Ah lfy kadai zo yanzu.
…………….
OK sai kazo.
Ya mike ya wuce dakinsa min2na kadan yaji
motsin zuwan nazir yana fitowa nazir wanda
2ni ya dare kujera yace “HUMAIRA!!
HUMAIRA!!! kllm zancenka kenan wai da gaske
kai ahaka zaka aureta…?
Faruk yadan tsaya a hankali ya tako tare da
bata rai yace “Eh a hkn ko zaka hana nine??“
Yayi tambayar sanda ya wuce izuwa karshen
falon ya dauko lemon juice da kofi ya juyo
izuwa inda nazir ke zaune yace “idan
munafuncin daya kawoka kenan ka tashi ka
tafi.“
Nazir ya warto kofin da faruk ya dora a dan
karamin tebirin dake gbnsa ya zuke lemon
cknsa yace “haka akeyi? ka gyyceni kuma ka
koreni??
kawai dai nayi mamakin yadda kayi haka anya
baka nuna rashinzuciya ba??“
Faruk ya grgza kai yace “Nazir ba haka bane
ni HUMAIRA bata taba yimin laifi ba, bada
yawunta, sonta ko yardarta abubuwan da suka
faru suka faru ba hasalima jajircewa tayi sai ni
sbd tana da yakini akaina, don haka idan na
juya mata baya yanzu ita nayiwa ba wani ba.“
nazir ya jinjina kai yace “kazo da zance kaima,
ynz dai me kake so ayi??“
Faruk ya gyara zama yace “So nake pls ka
sanar da kowa jibi daurin aurena kowa ya
shirya ba, nasanka da zafin nama a shirya
komai ckn lkc nasan zai yiwu??“
Ah! kwarai me zai hana?? ai ko gobene
bazamu kasa kintsawa ba bare jibi.
Faruk ya dago yace “Na sani, zan 2ra maka
isassun kudi a account dinka yanzu so nake
komai ya kintsu ckn kwana biyu kmr anyi shkr
biyu ana shiri, ga mukullin nan (ya jefa masa)
na gdna ne nasan kasanshi shima a gyarashi
gyara bana wasa ba a shiryashi a kintsashi
kada ya rasa komai da ake bukata.“
Nazir ya mike tare da sarawa yace “an gama
‘leader‘ yayi kasa da murya yace “amma dai
UMMI fa dole…“
faruk yace “karka damu shawo kanta a guna
bame wuya bane kai dai ka zartar da aikinka
ka barni da nawa ka hanzarta kaga dare ya
taho yi .“
Nazir ya taka kmr zai fita sai kuma ya juyo ya
rike baki yace “um!! gskyne gaf kake da kafa
record fa saurayin daya zama ango ckn kwana
biyu.“
kana gaf da zama MAI GIDA…..
Faruk ya nunashi yace “kai! bana son iskanci,
na…. yayi kmr zai bishi.“
Nazir ya kyalkyale da dariya ya fice da sauri.
Faruk ya koma dknsa.
*WASHE GARI da safe faruk ya fito byn ya
gama duk abnd zaiyi a falo ya tarar da ita
zaune a kujera ya gaisheta ta amsa sama-
sama.
Faruk ya gyara zamansa yace “Ummi gameda
maganar nan ne ta jiya ina so….“
Kace game da maganar banzan nan ce ta jiya,
ta mike tare da juyawa zata bar falon, faruk
yayi saurin mikewa ya tsaya a gbnta ya saki
hawayensa data fi tsanar gani fiye da komai
ya durkushe bisa gwiwoyinsa yace “Don
girman Allah ummi ki taimakeni ki fahimceni,
kin sani ban isa na aiwatar da komai ba sai da
izininki kuma bazan taba bijirewa umarninki ba
domin kece komai nawa.
Ina so nayi wani abu ne guda daya dazai
gyara abubuwa da yawa kuma ya samar da
alkhairai da yawa, ciki harda ladan taimakon
wanda yake bukatar a taimaka masa wanda
kin dade kina kwadaitar dani akan haka,
kinsha fada min na zama me juriya da yafiya a
koda yaushe.
Humaira batayi mana laifin komai ba hasalima
keda kanki yabonta kike kuma itama bata so
akai mana haka ba idan na gujeta a yanzu ba
wani nayiwa ba ita nayiwa, na tbbtr idan na
barta zata shiga kangi da takura fiye da ko
yaushe a rywrta nasan kuma kema ba zaki so
a gujeni don wata kaddara ta fada min ba!!“
Jin tayi shiru yasa ya kara tausasa lafazi yace
“2n ba yanzu ba kin dade kina fada min yadda
karshen rayuwar masu HALACCI, CIKA
ALKAWARI da RIKE AMANA take yin kyau ki
taimakeni na zama daya daga cksu don Allah.“
Ta bishi da kll da alama kalamansa sun
ratsata ma2ka, da dawo da baya izuwa kan
kujerar jim kadan tace “kai yanzu wane shiri
kayi??
Shirina bame wuya bane umarninki kawai nake
jira.
Ina ka shirya kaita to byn auren??
Ta sake tambayarsa.
Ya bata amsa da fadin “Gidan da kika fada
min cewa shima nawa ne dana gada a wurin
mahaifina kuma kika bani mukullinsa da komai
nashi da hnnki can zan kata mu zauna idan kin
amince.“
Shikenan ya zanyi da yin Allah?? Na amince
Allah yasa hkn shi yafi alkhairi.
Fuskar faruk tayi gaggawar washewa yayi
saurin mikewa ya dawo gbnta ya zauna tare
da cewa “Abinda nake so ki fada kenan ummi
nasan kuma zaki amince shi yasa nake
godewa Allah daya bani ke NA GODE sosai
ummina, amma kina ganin su kawu zasu
amince kuwa??“
Ba dole ba??
Tayi saurin fada.
Kaifa maraya ne kowa so yake yayi maka
abnd zaisa kayi farin ciki ko don ya sami lada
ka bari zamuyi magana dasu kaje kawai.
ckn farin ciki faruk ya fita daga gdn.
Hakika abnd Allah ya kadarta faruwarsa babu
abinda ko wanda ya isa ya dakatar dashi.
Da ana SO da ba‘a SO, Ana kuka ko ana
dariya, dole aka daura aurena da faruk a ranar
da lokacin a kuma inda aka shirya.
Ranar da bazan manta da ita ba a rayuwata,
daga waje biki yayi armashi ma2ka sbd ba
wanda yasan halin da ake ciki, kai ko a gdn
wadanda ya zama dole su sani ne kawai suka
sani.
A gdnmu kam naira jknta ya gaya mata, daddy
masu sakin famfon kudi haka kawai ma bare
da dalili.
Kowa yayi mamakin faruk da irin abubuwan da
yayi a sannan ne daddy ya tbbtr faruk ba irin
talakan da yake tsammani bane!!
Washe gari byn komai ya lafa dare nayi aka
kaini gdn faruk, gdn sabuwar rayuwa, gdn farin
ciki, gdn jin dadi da walwala.
Ba wasu mutane masu yawa bane suka rakoni
hakan yasa ba jimawa kuwa kowa ya watse
ya zamana daga ni sai MUFIDA, ina zaune
bisa shimfideden gadon da a yanzu nake jinshi
fiye dana sarauta ma daya zarce na alfarma.
Mufida na zaune sai zuba take ta inda ta
shiga ba tanan take fita ba, da yake uztaziyya
ce a nasihar tata harda ayoyi da hadisai,
maganganun nata na ckn ratsani naji tayi shiru
jim kadan ta mike tare da jawo mayafinta da
jakarta zata fice, nayi gaggawar dago kai na
damko hannunta wasu hawaye sukayi saurin
gangaro min nace “MUFIDA kema tafiya zakiyi
ki barni ni kadai??“
Ta bini da kallo tausayina ya bayyana karara
fuskarta, ta dawo ta zauna gaf dani tace “dole
zan tafi sbd nan gdnki ne ba namu ba, gasu
can a waje ni kadai suke jira mu tafi FARUK
yananan tafe KIYI HAKURI.“
Ta banbare hannunta daga nawa ta fice tana
waigena.
Daga nan sai naji ni a wani irin yanayi, ba
wanda zai zauna??
Wace irin rayuwa na shigo kenan??
Kodai basa sona shi yasa kowa ya tafi??
Tunanin da yayi ta yawo a zcyt a wancan
lokacin..!
Hmm da kina tunanin xasutayaki xamane…
Koya wannnan zaman aure zekasance..? Se ku
biyoni INSHA ALLAH..!
Ina nan zaune ni kadai bisa tsakiyar makeken
gadon da nake kai, jikina na sanye da kaya na
alfarma kaina na kasa kirjina na dukan uku-
uku na rashin sabo.
Sallamarsa da naji tasa naji wata nutsuwa
tazo min sautin muryar tasa ya daki
kunnuwana kai tsaye ya fara zagaye a
kwakwalwata, ban dago kai ba shi kuma baiyi
magana ba ya zauna ta salo na fuskantar juna
ya kura min ido kawai.
Na dan dago kai a hankali na dubeshi nayi
saurin mayar da kaina, yayi murmushi tare da
cewa “yes dago mana ya kika fasa my
AMARYA!!
kodai tsorona kike ji??
Na girgiza kai nace “Koda ace za‘a wayi gari
kowa ya zama abin tsoro a gareni na tbbt
banda kai.“
To ki dago kanki.
Na yace mayafin dake kaina tare da dago kai
fuskata wadda hawaye ya gama jikata sharkaf
ta bayyana.
FARUK yadan yi baya da kansa kmr yaga abin
tsoro yace “Kuka kuma?? Maimakon murna da
farin ciki??“
Na girgiza kai ckn sheshsheka nace “ni nafi
cncnta nayi kuka fiye da kowa, mafi yawan
amare nayin kuka amma na munafunci ne ni
kuwa nawa kukan na dolene sbd rayuwa bata
zo mana a yadda yakamata ba, laifin me
mukaiwa duniya da tayi mana wannan horon
FARUK…??
ya kauda kansa tare da cewa “ki daina fadan
haka HUMAIRA ba muka iya da yadda Allah ya
kaddara, Ai dai gamu a tare matsayin
MA‘AURATA wannan shine bbn abu mafi jin
dadi daya kamata ki rinka 2nawa. Na kara
kasa da murya nace “ma‘auratane mu amma
ba kmr saura ba 2nda mu muna da nakasu ta
bangarori da yawa kowacce amarya takan
zauna ne a tankwashe amma ni kafuna kaga a
mike suke daga sama har kasa ba wani motsi
da zasu iya yi, kaga kenan ni nakasashshiya
ba wani amfani da zanyi a garek……“
Yadan zaro min ido tare da katseni yace
“HUMAIRA!!“. yabini da kallo ya dora da fadin
“don Allah ki daina fadar haka, idan baki
manta ba a baya na taba sanar dake cewa ba
ina sonki ne don bukatuwar samun wani abu
daga gareki ba, ina sonki ne a mtsynki na
humaira gnnki a kusa dani kawai ya wadatar
dani.
Kuma ai larurarki ta iya wani lkc ce ba‘a ce ta
har abada ba don haka zaki warke kuma muyi
rywa kmr sauran MA‘AURATA.
Tarayyarmu bata wani dan lkc kankani bace ta
har abada ce, babu wani dalili dazai rabamu
har abada.
Ki rinka 2na wannan a koda yaushe.“
Ckn sheshsheka nace “a baya na dade ina
hango yadda rayuwar aurenmu zata kasance
ckn farin ciki walwala da jin dadi sai gashi
tazo mana akasin haka, tazo da babban
nakasu.“
faruk yace “ki daina kawowa zamanmu babu
farin ciki sbd kawai kina da larura, duk inda
HUMAIRA da FARUK suka kasance tare akwai
tbbcin farin ciki a wajen a kowanne irin yanayi
ne.“
nadan bishi da kallo nace “Me yasa ka hana a
bamu y‘ar aiki da zata taimaka mana, alhalin
sanin kanka ne ba abnd zan iya yi.
Yayi saurin girgiza kai yace “babu bukatar
wani ya shigo ckn rayuwarmu ya taimaka
mana mu zamu taimaki rayuwarmu da kanmu
kuma mu tafiyar da ita yadda muke so, zamuyi
zama irin wanda ba‘a taba yin irinsa ba.
Na tbbt Allah daya haliccemu zai taimakemu.“
“girki, goge-goge, share-share, wanke-wanke
duk waye zaiyi wadannan ayyukan??
Na tambaya ina dubansa.
ya mayar min da amsa da cewa “duk nine.“
Idanuna sukayi saurin tafiya yawo sbd
AL‘AJABI!!!!!
kai kuma??
Naka aikin kuma fa ko shikenan a gida
zakayita zama??
“A‘A! aikina yana nan amma bazai shafi
wannan ba.“ Wasu sababbin hawaye FIL suka
sulalo min.
Lallai bana jin za‘a samu mu2m irinka duk
duniya!! ka sarayar da hakkinka da duk wani
ango ke buri idan yayi aure sannan ka dauki
alhakin aiki mafi girma akanka duk sbd ni.
Ina rokon Allah ya kawo sababin da nima zan
nuna maka HALACCIN da kayimin duk da
nasan zaiyi wuya nayi maka irin abnd kayi min
sai dai na kwatanta.“ Na kwantar da kaina
bisa cinyoyinsa na fashe da kuka.
Mun dau tsawon lkc a haka dakyar faruk ya
rarrashe ni na iya yin shiru, da kansa ya tashi
ya zubo min abnc ya tilasta min sai da naci
sosai.
Ya dauke plask din da sauran kayan ya mayar
dasu wajensu ya tako a hankali yace “To kinga
yanzu lkcn kuka ya wuce ki kwanta kiyi barci
isashshe kada kiji komai a gdn masoyinki
FARUK kike..
yakai karshen maganar dai-dai sanda ya
zauna a dan karamin tebirin dake gefen gadon,
nabishi da kallo har yanzu hawayen idona
basu kafe ba saima kara gudu da sukeyi.
Na dubeshi nace “amma wannan rana tazo
mana ba yadda yakamata tazo ba, me yasa
ma haka zata faru??…“
Faruk ya dan kauda kai ya dawo ya dubeni
yace “ki bari!! zakiyi sabo fa! idan kika ce me
yasa, kai tsaye Allah kenan fa kike tambaya.
Haka Allah ya kadarta mana koda a haka
zamu tafi har mu2wa ni bani da kaico, kada ki
karya zuciyarki da yawa duk wanda yasanki
yasanki akan dakakkiyar zuciya me zai hana ki
dawo ki cgb da zama a haka??“
Na girgiza kaina nace “zaiyi wuya koda zai
yiwu badai a ynz ba.“
Ya bini da dogon kll yadan zunburo baki yace
“Zamu bata idan baki daina kuka ba.“
Na goge hawayen idanuna.
Yace “yauwa ko kefa??
Sai ki kwanta kiyi barci ki samu isashshen
hutu kinji??
Na gyada kai kawai nabi gadon na kwanta
nace “kai kuma ina zaka??“
Zanyo alwala nazo nayita sallah na godiya ga
ubangijina daya bani ke.
Zan bika muyi tare.
Na fada ina dubansa.
Ya girgiza kai yace “A‘A my amarya aike kina
da lalura barci shine mafi dacewa a gareki a
yanzu.“
Ka daina kirana da amarya sbd lalura ta hana
na amsa wannan sunan, ban kuma san sanda
zata barni na warke harna amsa sunan ba.
Na fada.
Yayi saurin cewa “manta da wannan“ ya jawo
bargo ya lullubeni har zuwa wuyana yace “kiyi
nutsatstsen barci da safe zaki fada min kalar
mafarkin da kikai.“
Yakai maganar murmushi na tashi daga fskrsa,
fuskata ta fadada da murmushi nima na gyada
kai kawai.
Ya juya ya dauro alwala akan idona ya fara
sallah sautin kara2n da yake yi yana ratsa
kunnuwana har barci ya kwashe ni.
*WASHE GARI da asuba faruk ya tasheni nayi
sallah a zaune kmr yadda na saba yi barci na
koma sbd akwai shi a idona sosai.
Misalin 8:15 na safe faruk ya tasheni a karo
na biyu, cak ya daukeni ya dôrani bisa kekena
ya seta kafafuna a matokarar keken dake kasa
ya 2rani a hankali muna hira kai tsaye muka
fito falo ya wuce dani gefe falon inda aka
tanadi wani faffadan tebirin cin abinci zagaye
kujeru ya 2rani har izuwa gbn kayataccen
tebirin ina zaune bisa keken da aka halitta sbd
irinmu.
faruk yace “yauwa kinga ke y‘ar baiwa ce ba
ruwanki da kujera, ni kuwa bin tebirin kawai
nake da kll zagaye yake da abinci kala-kala
irinna breakfast kuma dafawar yanzu sai tiriri
suke kana gani kasan yanzu aka hada su.
ckn AL‘AJABI nace “waye ya dafa duk wannan
abubuwan??“
Yayi murmushi yace “Nine!! kina mamakine??“
Ya fada dai-dai sanda ya ajiye kofin tea a
gefena tare da cewa “bismillah! sai ki fara da
duk wanda kike so.“
A ido kawai nasan duk abinda ya dafa zasuyi
dadi ma2ka sanda nakai bakina dazan hadiye
har wani lumshe ido nayi, na bishi da kll nace
“a jami‘o‘in koyon girki wacce kayi??“
Yayi dariya yace “A jami‘ar ummina mana, 2n
ina yaro tare muke yin komai gashi kuma
yanzu hakan ya fara amfani.“
Haka dai muka cgb da cin abincin ckn nishadi
muna hira har muka gama, faruk ya fara shiga
dani loko da sakon na gidan.
*Haka dai muka cgb da rayuwa har hu2n faruk
ya kare ya koma wajen aiki sai ya zamana
kafin ya tafi duk abinda zan bukata ya aje
minshi bisa faffadan tebirin dake gaf da
makeken gadona.
Abinci, ruwa, magungunana da komai suna
kusa dani sai kuma uwa-uba wayata wadda
da ita muke tare a ko yaushe.
kllm sai ya dawo ya koma, da la‘asar tayi
kuma ya dawo gida ya shiga kitchen da kansa
ya dafa mana abinci.
A wasu lktn tare muke shiga ina zaune bisa
dan kekena muna hira har mu gama hada
abnd muke so, rayuwarmu abin sha‘awa ckn
sauki muke gudanar da ita cike da walwala da
aminci wanda hakan ya samu ne ta silar
tsantsar SOYAYYA ta gsky.
Anya kuwa…za daure..
A wasu lktn idan na dubi a yadda rayuwarmu
ke tafiya sai naga kmr a mafarki don ban taba
zaton zan tsinci kaina a hali kwatankwacin
haka ba, da ace shekaru biyu kacal da suka
wuce wani zai fada min cewa haka zata faru
koda zai nutse a kasa don rantsuwa bzn yarda
ba.
Amma gashi na tsinci kaina a wata irin rayuwa
daba haka nayi zato ba, sai dai ko ba komai
wasu darussa ne na koya na rayuwa da
bazasu taba gushewa daga kwakwalwata ba.
*da yake zancen duniya baya buya a ckn dan
kankanin lkc maganganu suka fara zagaye
gari, nan fa kasuwar gulma da tsegumi ta
bude masu mamaki da rike baki nayi masu
salati da sallallami nayi, masu jinjinawa faruk
nayi masu tausaya masa nayi.
A fahimtar wasu kuskure ya tafka babba
dazaiyi dana sani a gaba, wasu kuma na
kllnsa wanda kuruciya tayiwa yawa.
Amma ko kadan bai kula da hkn ba saima
kwarin gwuiwa da yake kara samu na kyautata
min da nuna min soyayya iyakar iyawarsa, hkn
yaba mutane mamaki ma2ka da gaske. Wato
ni kaina idan na kalli faruk ina mamakinsa
musamman yanzu dana kara kusanta dashi
banyi kuskure ba idan nace ba kmr kowa yake
ba tbbs shi daban ne wanda samun mu2m
kmrsa zaiyi wuya.
A kwana a tashi kwanaki sai kara garawa suke
zaman mu na kara daukan lkc, syy da kulawa,
kauna da shakuwa na daduwa.
Mu kadai muke gudanar da rayuwarmu kmr
yadda faruk yace haka yake so mu kasance,
ko ziyara ba wanda ke kawo mana harta da
momina sai dai kawai muna yin waya wasu
lktn, ba‘a zancen daddy dama amma banga
laifinsu ba da wane ido zasu kll faruk??
Wanda suka batawa da mummunan sharri ya
saka musu da mafi kyawun alkhairi.
hmmm… Abin da kunya ai.
**kmr kllm yauma zaune nake bisa gadona na
kishingida misalin karfe 4:45 na yammaci
tsammanin dawowar faruk kawai nake nama
yi mamakin yadda yau bai dawo da wuri ba
don mafi yawa ana kiran sallar la‘asar yake
dawowa, a hakan har barci ya kwasheni.
ban jima da tafiya nahiyar baccin ba faruk ya
shigo da sllmrsa yayi shiru sanda ya tbbtr ba
yadda zanyi na amsa don bansan yana yi ba.
ya dan tsaya ya bini da kallo kawai murmushi
ya tashi daga fuskarsa ya rankwafo tare da
sumbatar goshina ya dago yace “ohh!! my
lovely wife Allah ya kara miki lfy.“
bai tasheni ba Ya juya ya wuce izuwa
bathroom.
Byn wasu y‘an min2na na farka, na dubi
agogo 5:05 lallai yau faruk ya dade bai dawo
ba na fada a zuciyata, ta yiwu wani muhimmin
abu ne ya tsayar dashi.
Nayi saurin bawa kaina tbbs akan haka domin
bisa al‘ada baya kaiwa haka don wasu lktn ma
ana kiran la‘asar yake shigowa.
Kmr na kirashi sai kuma na fasa, da yake da
wata kishirwa na farka matsowa nayi bakin
gadon na jawo ruwan SWAN dake ajiye bisa
dogon tebirin dake gefen gadon gaf da fuskar
gadon wanda ke dauke da abubuwa da yawa.
Irin daukowar gaggawar da na yiwa robar
ruwan yasa ta subuce ta fadi kasa tare da
gangarawa nesa sosai da gadon, gashi ina
bukatar ruwa sosai hakan yasa na matso
bakin gadon tare da kwantawa na mika
hannuna don dauko robar, sai dai ina!!
hannuna ya gaza kaiwa inda take.
Nayi iya kokarina na mika hannuna iyakar
mikawa amma ya gaza kaiwa, 2nanin dana
fara yi shine wai yau nice ga abu ina so amma
na gaza iya daukarsa kuma ba wanda zai
bani.
Musamman idan na 2na rywr baya yadda zan
hantara inyi tsawa a aikata min koda ba‘a so
sai gashi yau wanda zan yiwa magiya yayi min
ma babu shi a kusa.
Nayi wani spring ta gefe na koma zaune
hawaye wadanda suka zama sabo na suka
gangaro min, na zuba tagumi na rasa abnd
kemin dadi a duniya.
Dai-dai lkcn ne FARUK ya dawo daga inda ya
shiga izuwa dakin fuskarsa tayi saurin canjawa
ya bini da kallo, jimawa kadan yace
“HUMAIRA!!“
firgigit nayi kmr wadda ta farka daga barci
muka hada ido, kll daya nayi masa nasan ba
yanzu ya dawo ba nayi saurin goge idanuna
nace “Uhum!! dama ka dawo??“
Lfy?? meye ya faru kuma??
ya tambaya yana dubana.
na girgiza kai nace
“uhm..uhm ba komai meka gani??“
Ya tako a hankali yace “koda banga hawaye a
idonki ba kll daya zanyi miki nasan da wani
abu, abin mamakin min2na 15 da suka wuce
ma dana shigo barci kike yi ko kinyi wani
mummunan mafarki ne??“
Na girgiza kai alamar a‘a.
Ko don ban dawo da wuri ba??
Sake tambaya yana dubana.
Nayi saurin sake girgiza kai a karo na biyu.
ya bini da kll da fadin “meye ya faru to??“.
na dan kauda kaina a hankali nace “ba komai.“
na fada idona nakan robar ruwan data fadi 2n
dazu, faruk yabi inda idona yake da kll idonsa
yakai ga inda take ya kalleni ya kalli robar tare
da takawa ya daukota, ya dawo inda nake da
fadin “mu2m najin kishirwa yana ganin ruwa
ya gaza samu abin da ciwo kam.
Ya zauna a tebirin dake gaf da gadon muka
yadda zamu fuskanci juna sosai ya juya ya
dauko kofi ya tsiyaya min ruwan tare da miko
min, ba gardama kuwa na amsa tare dakai
kofin bakina na zuke ruwan.
yace “abinda yasa ya fada kasa wai yanayi
miki nuni da cewa na shigo ne, wanda
yakamata ya baki da hannunsa ya shigo don
me zaki wahalar da kanki don Allah ki bari
faruk ya baki da hannunsa. abinda naji robar
na fada kenan yanzu dana daukota.
Duk da gun2n hawayen dake idona saida nayi
murmushi har dariya ta kwace min.
hmm… me kwantar da hankali yayinda ya
tashi kenan.
Ya gyara zama yace “idan kina kuka ko sai in
rinka ganin kamar ba humairar dana sani a
baya bace, HUMAIRA y‘ar kwalisa me jin kai
da girma da martaba komai nata da isa take
yinsa, ga taurin zuciya da juriya komai na
kasaita ne.
Bata taba karaya bare har tayi kuka
hawayenta su zuba, me yasa kika canja????
Na bishi da kll kawai nace “rayuwa ce ta canja
ni sbd naga abubuwan AL‘JABI masu yawa da
suka koya min darasi a rayuwa wanda indai
zan rinka 2nasu hawayena ba zasu daina zuba
ba har abada.“
Zasu daina mana.
Ya fada tare da cewa “Dole sai kin manta
abinda ya wuce zaki samu nutsuwar fuskantar
abnd zai zo a gaba, kefa daban ce kuma
babba ce, mahaifinki babban dan kasuwa me
arziki ma2ka, ke kuma kina da baiwar ilmi,
fahimta da alfarma me yawa.
Na kada kai nace “OK na zaci girman ta
bangaren hikima, hazaka, tausayi, alkawari da
amana kake nufi dasai ince sai dai kai!!
Domin kai sai bayan shekaru ashirin ake sake
haihuwar irinka a duniya.(hmm anya kuwa
koni abdool aina fishi.)
Ya dan daga gira kadan tare da mikewa yadan
taka, nace “ina zuwa??“
Ya juyo tare da cewa “zan shiga kitchen baki
ga nayi dress din girki.“
nabi y‘ar karamar rigar dake jknsa da kll hade
da wando wanda da kadan ya wuce gwiwa, irin
kayan nan ne masu yanayin jersey da basu da
nauyi sai P-CAP dake sanye akansa 2n daga
sama har kasa duk launin yellow ne dasu nayi
murmushi nace “To a fito lfy amma ka tbbtr
ka kula da wuka sbd tana da kaifi, snn ka kula
da wuta sbd tana da zafi.“
Ke kuma ki kula da ruwanki sbd kada ya kara
fadowa. Ya fada tare da juyawa.
Nabishi da kll kawai nadan kada kaina dariya
ta kwace min.
Ya yaje bakin kofa sai kuma ya juyo tare da
takowa yace “my queen me kike sha‘awar ci
ne yau??“
kmr bazan ce komai ba sai kuma nace “Fried
rice idan ka iya.“
Yadan kara takowa a hankali tare da
maimaitawa “fried rice! fried rice!! kai gsky…..“
Rabu dashi kawai kayi koma meye.
Nayi saurin fada. Ya girgiza kai tare da cewa
“ba za‘ai haka ba 2nda shi kike so to sai mun
cishi yau, abnd za‘ai ba dake zamu je kitchen
idan ni ban iya ai ke kin iya, sai zama director
kina zaune a kekenki na sarauta kina bada
umarni.
Daga yau kinga nima sai na kara ilmi ko??
Ya karasa fada sanda ya karasa inda kekena
yake ya 2roshi dai-dai bakin gadon.
Haka kuwa akai a hankali ya 2rani bisa keken
izuwa kitchen muka fara aiki.
Ina daga zaune ina yi masa nunin abubuwan
dazai hada don yin fried rice ckn nutsuwa, idan
bai gane bama 2rani yake har inda abin yake
nayishi da kaina. A haka har muka gama
hadawa tare muka dawo izuwa falonmu.
Irin wannan shine taimakon kanmu da kanmu
da mukeyi kuma muyiwa kanmu komai ba
wanda yakeyi mana.
Kwanaki nata zuwa suna shudewa sannu a
hankali, kulawa daga faruk babu alamun
raguwa saima karuwa a koda yaushe.
*BAYAN SHEKARA DAYA*
zai yiwu bazai yiwu ba, zamu jure ba zamu
jure ba, zai iya faruwa ko bazai iya ba da
wasu keta cece-kuce duk sai yazo ba yadda
da yawan mutane suka zata ba.
sai da muka shafe tsawon shekara daya cif a
haka yadda muke.
Abin sha‘awar babu korafi ko canjin yanayi a
tare damu sai ma karin karfin gwiwa da muke
samu da kuma tbbs soyayyarmu da tbbs na
rayuwa tare har abada.
Wato mun riga mun zama daya na zama faruk
ya zama ni domin idan na fahimta dai-dai ko a
fuska kamanninmu sun juye sun zama daya.
dangane da larura ta A kllm jina nake akwai
alamar sauki a tattare dani sai dai bana yarda
da hakan, a yanzu ina jin cewa akwai kafafu a
jikina sabanin baya.
A kllm kuma sai nake jin suna kara karfi har
nakanyi 2nanin me zai hana na gwada mikewa
amma idan na 2no da gargadin likita acan
baya sai na hakura.
Abinda na tbbtr shine akwai ranar da zata zo
zan mike na tafi akan kafata don na dade da
fara jin alamun haka.
*Kamar kllm yadda ya saba fita misalin karfe
10:00 na safe ina zaune bisa kekena faruk na
tsaye jakarsa na hannuna ya gama shirinsa
tsaf zai fita na bishi da kll nace “you look very
fresh my life, amma zaman hularka da gyara.
Ya tsugunno dai-dai da fuskata tare da cewa
“gyara min dai-dai da yadda kike so.“
Na cire hular a hankali tare da gyara karinta
na mayar kansa tare da daidaita zamanta naja
hannuna baya tare da lankwasa dan yatsana
alamar jinjina.
Ya mike na mika masa jakarsa da fadin “fatan
alkhari, sa‘a, da nasara a gareka mijina.“
Ya karba tare daja da baya yana kllna yace
“ameen matata, zadai ki iya tuka kanki ki
koma daki ko???“
Na gyada kai nace “Eh kasan ai keken na
zamani ne wanda yake kaima zai iya
sarrafashi nayi sa‘a ni gurguwar zamani ce
bata daa ba.“
Kidai bi a hankali kinsan KARFEN NASARA….“
Ya fada yana me nuno ni da dan yatsa.
Nayi dariya nace “nafa yi karfi yanzu nayi
kwari sosai don ni a yanzu ji nake kmr ma zan
iya mikewa nayi tfy da kafata.“
FARUK ya girgiza kai yace “habawa!! da saura
kada ma kice zaki jaraba don bazai yiwu ba,
ko kuma kima gwada 2n yanzu a gabana don
ki tbbtr bazaki iya ba kada ma in tafi ki gwada
hakan.“
Na bishi da kll nace “kaban izinin hakan??“
Ya gyada kai tare da matsowa wai kozan fadi
ya taroni.
Na jinjina kai nadan runtse idona tare da yin
bismilla na yunkura a karo na farko na tashi
tsaye, ni kaina bude idona kawai nayi na ganni
a tsaye kyam!!
Kmr daga sama lkc guda naji karfi ya shiga
ckn kafafuna ko don dama rashin motsasu na
sawa bana jin karfinsu??
Nan fa fuskar faruk ta fara canjawa yana kllna
kawai ckn mamaki.
Ni kuwa kawai sai na motsa na daga kafata
tare dayin tafiya nayi taku uku akan kasa
sannan ne tbbtr da abinda nake zato, tbbs
kafafuna sun dade da dawowa dai-dai nice
kawai ban sani ba.
Sbd AL‘AJABI idanun faruk zarowa sukayi
waje kamar zasu fado sai kllna da yake yi ya
kasa magana, na dubeshi nace “faruk na
warke fa.“
Kara takawa mu gani!!
Na daga kafata na taka nayi tfyr dani kaina
banyi zato ba naji ni damurmur akan kasa ko
alamar layi banayi bare na fadi, jina nayi a
yanzu tamkar ban taba samun wata matsala
ba.
Faruk yayi wurgi da jakar hnnsa izuwa kan
kujera ya tako izuwa gabana a hnkl bakinsa
ya furta sunana “HUMAIRA!!!“
muka rungume juna sbd farin ciki da murna,
wasu sanyayan hawaye suka gangaro bisa
kuma2na.
muka fuskanci juna sautin dariyar farin cknmu
me hade da hawaye ta fara tashi, faruk ya
goge hawayen kuma2na da hannunsa ya
girgiza kai yace “ba lkcn kuka ne yanzu ba,
asibiti zamu tafi yanzu don mu sami tbbs
daga bakin doctor shirya maza.
Faruk har wata y‘ar karamar rudewa yayi,
kayan jikinsa ma canjasu yayi yasa wasu.
Muna fitowa motarsa muka hau wanda ke kula
da gate din gdn ne yake jan motar sbd murna
ba zata barshi yayi 2ki ba, da mun hada ido
murmushi ke tashi daga fuskokinmu.
Ban taba tsintar kaina a farin ciki kmr na yau
ba, sai da takai magana ma bama yiwa
junanmu sai murmushi sai dariya har muka
iso makeken asibitin da shekara daya kenan
rabona dashi.
Duk inda na kalla a cknsa baya nake 2nowa.
salih Ka dan jiramu zamu fito bada jimawa ba,
faruk ya fadawa wanda ya jawo motar.
To ranka ya dade.
Salih ya fada ckn ladabi.
Muka juya izuwa ckn asibitin kai tsaye.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Leave a Reply

Back to top button