COUSINS NENOVELS

COUSINS NE 5-6

PAGE….. 6-7

DAN ALLAH KURINKA MIN HKR DA TYPING DINNAN SBD KUNSAN DAN KOYO SAI AHANKALI❤❤

Aliyu tunda ga ranan yake kirga days din yanagani kaman bazaizo ba amma gashi yau he is so excited gobe zai ga wacce a duniya in ya ganta farincikinsa nadabanne……

Alhaji usman ne yafara mgn kunsan dalilin dayas nakirawo ku nan, bawani abubane kaman yanda kaka take muku mgn akan mijine, kowacce asannan zuciyanta tahau bugawa bare khadijerh da ita samarinma bawai sunda meta bane balle har akaiga mgn aure, fatima kuwa tunani takeyi in Akace su ciro miji yanzu

ai angama da ita, dan wanda takeso asalima yanzu yayi 2yrs a india yana karanta medicine, Baba ne ya katse tunaninsu dacewa kunga kaka ta matsa ga sa’oinku dasuke can gombe kowacce da rana akanta da sun kanmalla karatu za’a aurar dasu, amma ku kunanan ko gaisuwa bbu wanda yazo. Mamace takatse shi

dacewa nibanyi tunanin ko samarinma suna dashiba tunda mama tafara mgn dukansu jikin yayi sanyi, sannan baba yace nabaku daga yau zuwa kugama jarrabawa kowa ta fito da wanda takeso dan dakungama insha Allah mukeso duk mukoma can gda ahada bikin ayi gabadaya… Shirune yabiyo baya

kafin baba yace ko akwai mai mgn acikinsu kowacce acikinsu jiki yayi sanyi da kyar suka girgiza kai yace to Allah yamuku Albarka ya kawo mana surukai nagari Ameen mamah tace suka tashi jiki bbu kwari kowacce da tunanin dayake ranta suka fita… Suna fita mama tace amma alhaji kanaganin yarannan danake ganin

ko samarin basu dashi kaganin watannin dayarage aka dibar musu bamushiga hakkinsu ba? Babane yakatseta dacewa to kina yawo dasune dazaki san sunadashi ko bbu, aa alhaji gani nayi bbu wanda yataba zuwa gunsu zance ne, nifa naga alaman kina biyewa yarannan dayawa zamani na waya dolene sai sunzo

sunyi zance agda kingani. Aa alhaji Allah yakawo musu miji nagari gaba dayansu ainima basan zaman nasu nakeyi ba ai lokaci yakai suyi. Ameen yace suka cigaba da hiransu…..

Alhaji Ahmad ne yashiga gun mahaifiyarsa dakaya su lemu da ayaba a hanunsa da sallama yashiga tana zaune tana kallon saudi da sheikh maheer yaketa zuba kira’an Alqur’ni, nan yashiga ya gaisheta ta ansa cikin fara’a dan duk ayaranta tafisonsa, sannu mama yajikin kinsha mgni eh nasha yan itacena kuma naji

sauki, to amma mama aida kin hada dana asibiti a’a bbu yanda yayanka baiyi ba nace naji sauki a’a mama yanzu zanjeni inkarbo miki mgn kisha dakyar ya lallabata tayarda yazo da likita ya dubata yarubata mgni dazatasha, yana fita Alh Ahmad ya bishi yaje yasayo mgn da dakyar ta yarda ta karba tasha…

Allah yakara sauki mama zanje insha Allah zandawo nabaki mganin anjima to Allah yakaimu… Kafin yafita sanda yatambaye ta bbu wani damuwa ko wani abuda take so shiru tayi kafin ta fashe masa da kuka tanacewa nidai nagaji da mgn dan kunga bani da lfy ace ina mgn acikinku bbu mai saura rata nace

yarannan amusu aure lokacinsu yakai har yana neman wucewa amma duk bbu mai kokarin musu mgna to wlh barinaji sauki bbu ruwana da karatunsu zanje can gda na zaba musu mazaje, Alh Ahmad saida zufa ta karyo masa dan yasan kullun rikicin mahaifiyar tasu knan kuma wannan karan dole adauka mataki, dakyar

ya tattaro karfin hali ya rarrashe da alkawarin zai samu yayan nashi tunda sunkusa gama karatu su ciro miji suna kammalawa sai ayi bikin.. Mu ai lokacinmu muna kamansu ai munhaifi ya’ya komu ba’asonmune aka aurar damu da kyar yabata hkr akan lalle za’asa dau mataki nanda sugama makaran

ta da hka sukayi sallama yatafi akan zaije gdn wannasa suyi mgn…..

Suna shiga daki kowa da tunanin datakeyi wlh nikam banshirya aure daga gama karatuba amma dagajin wannan mgn wlh daga bakin kaka tafito dan nasan da dantasu baba ne har jami’a saimunje inji khadijerh

tab kedakike tunanin jami’a nidama alkawari mukayi da sadam akan yana gama karatunshi inya dawo 9ja zamuyi aure amma yanzu kuma mgn tasha banban ni wlh yanzu nashiga cikin damuwa, tab ai dole kidamu tunda kikaga baba yashiga cikin zance ai sai addua ranan dai hka suka wuni kowacce bbu walwala

dan kowa da tunanin da takeyi…. Wayan khadijerh ne yayi ringing tana dagawa tayi ajiyan zuciya da itakanta batasan na menene ba dagawa tayi kamar yanda tasaba sallama tayi ta gaishe shi ansawa yayi cikin zazzakar muryansa da sanda ta lumshe ido ta bude, yace dafatan kina lfy naso nakira tunsafe sainayi

tinani ko kinje sch eh tace masa yace to mekika karanta kikoya min kinsan ni dalibinki ne dariya mgn tabata sannan tace ai yanzu kullun mukaje muna zama a library ne sbd kasan munkusa fara waec laa kice matar dazan aura takusa gama karatu mamaki yaba khadijerh jinyace matarsa amma zahiri sai murshi tayi,

kice gobe inzo da book da biro nayita koya miki karatu nantaji zuciyanta ya buga dan ita tama manta da tamishi alkawari, laa ashe gobe zakazo wlh namanta Allah yakaimu tonayi fushi tunda baki damu dani ba harkin manta dazuwana shiru tayi kafin tayi karfin halin cewa a’a ba hka bane kasan exams din damuke

dashi so bamuda wani tym, amma Allah kaimu gobe tunda tafara waya Fatimah ke kallonta tanason sanin dawa take waya amma bbu hali shiru tayi tana jira sugama waya taji kwakwaf…sallama khadijerh sukayi da Aleeyu wanda ita kanta bata taba tunanin zata yi hira hka dashi ba sai gashi ta tsinci kanta da farin cikin

dabata san daliliba.. tana kashe waya Fatimah tace waidawa kike waya hkane harda wani murmushi kaman kamal aina fadamiki tunda nace banayin kamal banayine dama da yaya na saurareshi ai darajarki yaci kuma yayi barin garinsa dakansa, tebe baki Fatimah tayi tace towaye shiru khadijerh tayi kafin tace to

waini dakike tamin tamba yoyi hka inkinsan waye mezakiyi Allah yahuci zuciyanki. Ameen tace kafin tace to Aleeyu ne damuka hadu nama manta da wai gobe zaizo shine yakeda d’a tunamin Allah yakaimu Fatimah tace tana fita adakin tebe baki khadijerh tayi tabita da kallo tacigaba da assignment dinta…….

Aleeyu na kashe waya yatashi yashi closet dinsa yarinka ciro kaya waishi gobe zaije tadi… Hhh saban shiga knan barawo da sallama…
[11-19 2:00 AM] Nana Khady Novel: ????????❤COUSINS NE ???? ❤

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button