INAYAH COMPLETE HAUSA NOVELINAYAH COMPLETE HAUSA NOVEL

INAYAH 1-10

1

please masu daukamun Sunayen books da Labarai suna sauyawa suyi nasu lamarin ina ganinku dan Allah ku daina ba kyau, kuma masu copying nagani allah ya kyauta ngd duk cikin Qaunace allah yaqaro kauna????

BismillahirRahmanirRaheem

Tasowa tayi ahankali tana takowa zuwa tsakar gidansu datake jiyo maganar mahaifiyarta da yayyunta maza tareda kishiyar mahaifiyartata suna magana duk a jujjuye sbd hankalinsa daya tashi lokaci daya cikin mummanan yanayi da tashin hankalin mugun labarin dayazo musu yanzu yanzun.

Ita kanta hankalinta baa kwance yakeba dama can sbd halinda take ciki na jinyar mijinta dake kwance asibiti Yana jinyar accident dasukai kwana biyu dasuka wuce a hanyarsa ta dawowa daga gurin daurin auren qaninsa dasuke uwa daya uba daya,

Kaman a fizge kunnuwanta suka jiyo mata abinda babban yayanta Umar ke fada saidai Sam takasa fahimtar abinda yafada din zahirance Dan haka tana buqatan jinsa da kyau,

Ta qaraso jikin kofar ta yaye labule ta fito tana kallonsu daya bayan daya fararen idanuwanta dasuka jima da shigewa ciki ciki sbd damuwar datake ciki kwanakin,

Suma ita suke kallo Kaman yanda take binsu da kallo kowannensu fuskarsa cike dauke da alhini dakuma tausayinta Dan kuwa Rashin miji a irin shekarunta abin tausayi

Ga Kuma ‘da da ciki dake jikinta.

Kallon mahaifiyarta tayi taga yanda tayi qasa da Kai cikin yanayi na hawayen dasuke Neman saukar mata takasa kallon Yar Tata

Dan haka ta kalli kishiyar mahaifiyarta kai tsaye tace”

Inna Menene duk kukai wani iri haka?

Lafiya kuwa?

Wani abin yakuma faruwa ne?

Maida kallonta tayi kan yayyunta dake tsaye suna kallonta tace”

Yaya Umar,Yaya kabiru?

Lafiya duk kukai shiru haka?

Jikin Abban Abdul ya tashi ne?

Ajiyar zuciya Yaya kabirun ya sauke tareda gyara tsayuwarsa ya kalleta da Dan alhininsa irin na maza masu taurin zuciya Kai tsaye yace”

Khadija bayan barowarki asibiti yanzu Allah yayiwa Salisu cikawa……..

Bai qarasa ba ta waiwayo gefensa tana kallonsa cikeda zallan mamaki da faduwar gaba muryarta na gwamutsuwa tace”

Yanzu fa na Barosa Yana barci,

Wanka fa kawai zanyi nakoma asibitin shine zaace ya rasu????

Yanzu yanzu fa?

Da sauri innar ta riqota cikin tausayawa tace”

Hadiza karkiyiwa ubangijin haka,

Tawakkali zakiyi tunda kinsan dai baa wasan mutuwa…

Idonta na sauya zuwa ja da hawayen dake kokarin cikowa saidai taurin zuciyarta ya hanasu fitowa

ta katse innar da cewa”

Inna bacci nabarosa yanayi fa,

Yaji sauki sosai yau,

Rasuwa fa akace,

Mutuwa fa kenan, ya tafi ba dawowa har abada,

Ta Yaya zanyi…….

Cikin Dan daga murya Yaya kabirun yace”

Ke Khadija Menene hakan?

Rasuwa fa akace Miki salisun yayi,

Ki nutsu ki fahimci ita rasuwa babu ruwanta da yanzu yanzun dakike fada,

Kiyi gaggawar bude hankalinki ki fahimci abinda yafaru dake,

Salisu ya rasu bazai taba tashiba……

Bakinsa take kalla kanta na juyawa

Zuciyarta na harbawa da mugun qarfi Kaman zata faso kirjinta,

Mamarta ta kalla idanuwanta na qafewa taga alamar gskiyar zancensa akan fuskan mamar,

Ta waiwaya ta kalli Yaya kabiru Shima hakan tagani.

Wani busasshen yawu ta hadiye wanda har yankan maqoshinta yake

Ta juya kai tsaye Takoma dakin mama ta dauki doguwar hijabinta data cire bayan shigowarta gidan ta zira ko waya da kudin adaidaita Bata daukaba ta fito ta zira slippers din mamarta daya Da nata takalmun daya batareda ta luraba ta nufi kofa tana jefa ka kawai dan bata cikin hayyacin kallon gaban nata

asibitin take buqatan isa kawai.

Inna ce tayi saurin janyo nata hijabin tabi bayanta tana Kiran sunanta,

Mamarta kuwa kallon Yaya Umar tayi tana cewa”

Bisu kabasu kudin adaidata ban Saka ran kowannensu ya daukaba.

Juyawa yayi ya bisu

A titi yayi saurin taddasu ya ciro 1000 ya miqawa Inna Yana cewa”

Ga kudin adaidata Inna

Ki lura da ita Inna kartaje asibiti tayita wainnan maganganun

Tawakkali akeyi kifada mata Inna.

Da sauri innar ta qarasa gurin hadizar daketa zuba sauri tana tafiya ta riqota ta riqe hannunta gam tana kokarin Kiran sunanta saiga adaidata gabansu ba Bata lokaci suka fada ciki

innarce tafada masa asibitin da zasu

Khadijan kuwa Banda rawa babu abinda qafafunta da hannuwanta keyi.

Isarsu asibitin ko Gama tsayuwa baiyiba Khadija ta sauka tareda wucewa da sauri ta nufi hanyar Emergency ward da har lokacin Salisu anan yake.,

Tun daga nesa Yan uwan Salisu din maza da mata suka hangota tana tahowa a gigice ko ganin gabanta batayi

Hankalinsu yakuma tashi da tsananin tausayinta dan haka da yawansu suka qara fashewa da sabon kukan Rashin Dan uwansu.

Tana qarasowa da kallo tabisu daya baya daya taga yanda mahaifiyar salisun ke rusa kuka take taji Rabin jikinta na neman mutuwa ta qarasa dakin tashige da gudu ta nufi gadonsa da gawarsa kawai ta tadda a rufe da zanin gadon data zo masa dashi yau da safen.

Tsawonsa ta kalla tareda hannuwansa da aka miqar,

Kasa gasgatawa tayi Saida takai hannu ta yaye zanin tayi arba da kyakkawar fuskarsa ta asalin fulanin Yola….

Mummanan bugawa zuciyarta tayi ba tsammani idonta yarufe tana kokarin zubewa Inna tayi saurin tarota tana Kiran sunanta Amma Sam batajinta sai neman somewa takeyi.

Da sauri hajiyarsu salisun ta qaraso tana cewa”

Ku koma gida da ita karta shiga wani Mummanan halin ga juna biyu a jikinta.

Qwacewa takeson yi Dan Bata tunanin zata bar gawar salisun ta tafi koina Amma batada qarfin motsawa bare magana Dan bakinta take ya manne Kaman an Saka mata glue.

Tana kallon gawar mijinta Salisu aka jata aka fice da ita har waje aka kuma sakata napep tareda Inna da qanwar salisun suka nufi can gidan iyayen salisun.

Suna isa ko tsakar gidan Bata qarasa shigaba ta yanke jiki ta fadi jini nabin qafafunta.

Hankali tashe sukai kanta tareda ciccibarta zuwa dakin hajiyarsu salisun Inna na Kiran sunanta hankali tashe.

Jini sosai take zubarwa Wanda ya tabbar musu da cikin zubewa ne yayi babu tantama Dan haka basuyi wani yunqurin maidata asibiti ba haka Inna da dattijuwar gidan qanwar mahaifinsu suka taimaka mata gurin ganin jinin yagama zuba ta Dan gyara.

Kururuwar koke koken da gidan ya dauka ne ya tabbatar musu da isowar gawar Salisu gida

Tana jin hakan ta rintse idonta cikin tsananin azaba sauran abin dake cikin nata ya qarasa zubowa sai alokacin wani irin gunjin kuka Mai tafe da radadin zuciya ya kufce mata.

Inna dake kanta ta qara matsowa tana dafata cikin tausayawa jin irin girman kukan datake,

Kuka takeyi sosai zuciyarta na radadin Rashin mijinta uban ‘danta dakuma wannan cikin daya qwallafa ransa akansa,

Ashe tareda cikin zasu bar duniya Rana daya shiyasa Allah ya saka masa tsananin kaunar cikin abokin tafiyarsa ne kenan.

Bata damu da yanayin datake ciki ba

Haka ta dafa ta miqe tsaye tareda qarasawa tsakiyar bayin dakin hajiyar ta wanke jikinta daqyar sbd tsananin rawar da hannuwanta da qafafunta keyi.

Fitowa tayi Kai tsaye ta karba zanin da inna ke miqo mata ta daura wani irin tsananin jiri da ciwon mara Mai tsananin gaske Yana nukurkusarta Amma taqi yarda tazauna Kai tsaye ta fito tsakar gidan sanyeda hijabinta tanajin yanda tako ina gidan ke amsa amon kukan Yan uwan Salisu.

Gawarsa dake shimfide a dakin da zaai masa wanka ta nufa ta zube gabansa tafara rero wani irin gunjin kuka tana Kiran sunansa.

Duk yanda akaso janyeta kasawa akai sbd kuka takeyi sosai zuciyarta na tsananin qunar Rashin mijinta datake tsananin so da kauna yau gashi ya tafi yabarta cikin duniyar da kowa babu abinda yasani sai kansa,

1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button