BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO 26

        Washe gari Daddy ya sakasu komawa can gidan Fadwa na ɗacin ran kasancewa da Anam. Khaleel ne ya ɗauke su su huɗu har mai aikinta dan maigadi shi tun jiya ya koma. Anam tai murmushi tana kauda kanta gefe ganin uwar hararar da Fadwa ke zuba mata kamar idanunta zasu zubo ƙasa. Sosai murmushin ya ƙular da Fadwa, sai dai batai magana ba har suka iso. 
        Kiran da Abie yay ma Anam a waya ne ya sata dakatawa su suka shige su uku. Itako ta tsaya anan jikin motar Shareff dake lulluɓe tana amsawa. Ta jima tana wayar kafi. ta nufi ciki itama fuskarta ƙawace da murmushi. Matar gidan kawai ta samu a falo zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya tana jijjigawa da yanka apple. Sai mai aikinta dake gyaran falon. Yi tai kamar bata ganta ba tai ƙoƙarin wucewa……..✍????

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button