Bakar InuwaNOVELS

BAKAR INUWA 23

Typing📲

Episode 23

…………A É“angaren Ramadhan kam yama manta da wani batun aurensa balle Raudha. Harkokin gabansa kawai yakeyi na shirye-shiryen rantsarwa da zaman meeting-meeting da suke yawanyi da Ć´an jam’iyya a gidan gwamnati. Shi kansa ma haushi meeting É—in ke basa a mafi yawan lokaci, dan wasu yakan rasa gane kansu balle inda suka dosa. Sai dai yana nutsuwa dai wajen maida kansa yaron da suke kallonsa yana karantar komai da nanufofinsu.
     Sai dai abinda Ramadhan bai sani ba a garesa ne kawai ya manta da abatun aure, ga jama’ar gidansu da masu so da masu Ć™i duk abin na ransu. Domin shiri su Anne keyi na musamman akan auren, lefe ya kammala haÉ—uwa tsaf, hakama abubuwan da duk za’a buĆ™ata ga taron biki.

          A É“angaren su gimbiya Su’adah ma dai suna nan akan bakansu na hana tabbatar wannan aure, sai dai kuma tun randa Pa ya ritsata tana waya da Asma yaji kuma mi suke faÉ—a yaja mata dogon gargaÉ—i, tare da alwashin inhar wata matsala ta shigo a auren nan ta shirya amsar matsala a nata auren itama. Wannan ne ya tada mata hankali ya kuma ja mata birki, sai ta koma zungurin Ramadhan akan auren. Sai dai kuma rashin zamansa a gidan ya taimakesa da masifarta.
    A yanzun kullum cikin Ć™ulla yanda zasuci uban Raudha suke inhar ya tabbata sai anyi auren. Tare da É—aukar alwashin aurama Ramadhan Aina’u koda daga baya ne.

     A hutawa ma dai Mal. Dauda ya shirya tsaf, dan gyara na haĆ™iĆ™a yayma gidansa tamkar bashi ba. Ya baza É—inkuna yayma kuma kowa na gidan. A yanzu haka Innarsa da Ć™aninsa da iyalinsa suma sun dawo nan gidan da zama. Hakan yasa Larai ta rasa kataÉ“us dan Inna cin uban surukai take babu É—aga Ć™afa. Balle ma yanzun da take ganin É—anta yay arziĆ™i, ai koda wasa babu wanda ya isa zagin Asabe a gabanta duk da bata nan. Takance Asabe ai farar uwa ce tunda gashi sanadin ta haifi Raudha suna hutawa. Takanji takaicin saki ukun da ta saka Mal. Dauda yay ma Asabe a yanzun. Inama É—aya ne ko biyu da yanzu sai ta dawo abinta.
        To anan ma dai shirinsu suke tsaf duk da babu amarya har anko an fitar ma.

       SATIN BIKI

  Shiga satin biki ya saka ango da amarya dawowa cikin hankalinsu. Dan kuwa sun tabbatar yanzu kam da gaske ake Ć™warai. Ta ko ina sanar da wannan É—aurin aure ake a kafafen yaÉ—a labarai dana yanar gizo, yayinda wasu baĆ™i dake Ć™asashen Ć™etare suka fara sauka ciki harda su Sultana daba taron bikinne ya kawotaba kai tsaye. Dan tunda akace Ramadhan ya fito takarar shugabancin Ć™asar NAYA take son zuwa, sai kuma ga batun aurensa da yay matuĆ™ar tada hankalinta har takaita da kwanciya asibiti. Halin data shiga yasa Babanta yarda su Mufeed suzo da ita taga Ramadhan É—in.
     Sai dai kuma tun jiya suka iso amma ganin Ramadhan yay musu wahala saboda yana can suna shirye-shiryen zancen rantsarwa. Za’a É—aura auren ne juma’a, asabar ayi rantsuwa, lahadi su tare gidan gwamnati tilitin shugaban Ć™asa ya fara shiga office.


     Ga amarya kam itama ta yarda dai auren nan babu fashi, tunda aka shiga satin bikin aka sake ninka yanayin gyaran jikinta da akeyi, tayi Ć™oĆ™arin toshe duk wata hanya bata sake haÉ—uwa da Alhaji yaro glass ba duk da yana yawan zuwa gidan yanzun. Ana saura kwanaki biyu É—aurin aure daren da washe gari za’a maidata Hutawa kusan sha biyu yunwa ta addabeta, dan duk yinin yau bataci wani abincin kirki ba saboda damuwa. Bata son auren nan ko É—igo a ranta, gefe ga tsoro da fargabar tsantsar Ć™iyayyarta data hanga a cikin idon Gimbiya Su’adah da wasu a Ć™annen mijin nata. Jin har kamar zuciyarta na tashi dan yunwa ya sata fito da nufin zuwa kitchen ko tea ta haÉ—a.
     Da sauri taja birki jin kamar ana magana Ć™asa-Ć™asa dai-dai tana Ć™oĆ™arin sanyo Ć™afarta a falon, ta É—an laÉ“e tana leĆ™e daga corridor É—in É—akunan barcinsu ita da su Yasmin. Aunty Hannah ta hango da wasu mutane uku, babu wanda ta gane a cikinau sai Alhaji Yaro glass kawai. shima dan rabin jikin aunty Hannah nakan nasane. Dan tana zaune kusan a jikinsa ne ko kunyar sauran mutanen bataji. amma sauran ukun babu wanda ta sani.
     Jin an ambaci sunanta yasa gabanta faÉ—uwa. taÉ—an sake matsowa daf da hanyar fita corridor É—in ta kasa kunne taji da Ć™yau.
      Wanda yake a kujerar Ć™arshe mai sanye da jallabiya baĆ™a ya Ć™ara fuskantar aunty Hannah yana faÉ—in, “Hannah kinga dai mun matuĆ™ar yarda da ke, dukkan wani shirinmu a yanzu tamkar ya rataya a wuyanki ne. Bama son kuskure ga yarinyar nan, dan idan aka samu kai tsaye ke zamu É—aurama alhakin hakan”.
        Kanta ta jinjina masa tana tashi zaune sosai. “Alhaji Wada karkaji komai, na riga na É—aura Raudha bisa kowacce irin hanya da bazata iya bijire mana ba. Ku É—auka tamkar yaron nan ya mutu ya gama a shekara biyun da kuka É—eba masa. Adai É—aura auren jibi, da zarar sun tare za’a fara bata maganin tana saka masa a abinci, ko abin sha kamar yanda first lady ta sanar min..”
        “Hakan shine dai-dai, dan munaso ya fara masa aiki a hankali yanda ko bayan mutuwarsa za’a É—auka diabetis É—insa ce ba wani ba, tunda dama maganin zai Ć™ara Ć™arfin diabetis É—inne ya kuma haifar da hawan jini mai Ć™arfi. Sannan a yau da safe duk wani poison an sakashi a cikin ac É—in falonsa da bedroom dan a hankali mukeso ya fara ratsa jininsa shima ta yanda zai zama bashi da wani kuzarin nutsuwa yay aikin ma, dan cikin idon yaron nan ka kalla kasan bazaiyi mutunci ba. Yana gama gane kan mulkin nan mukanmu ba É—aga mana Ć™afa zaiyiba wlhy.”
         Alhaji Yaro glass ya karÉ“e da faÉ—in, “Ai dama shegene yaron nan, yanda kaga kakansa da taurin kai haka shima yake. Ni gani nakema mizai hana ita Raudha mu fito mata Ć™uru-Ć™uru akan aikin da muke son tai mana kawai dan yarinyace sai yanda mukai da ita.”
      “A’a wannan ganganci ne, idan kuma aka samu akasi ya faÉ—a sonta fa? Ko kuma itama tana sonsa yanzu haka? Dan yaron nada qualitys É—in da mata zasu so sa a Ć™anĆ™anin lokaci. Giyar soyayya kuwa zata iya janta ta sanar masa. Kawai muyi yanda muka tsara ayi amfani da ita”.
          Cikin zafin rai Mr MM yace, “Idan ma mun sanar matan tace zata tona mana asiri halakata zamuyi itama a banza….”
      “Ai ko yanzu É—in ba tsira zatai ba. Kana tunanin zata dinga shaĆ™ar gubar nan ta cikin ac ta tsallake itama. Yanda zata dinga masa illa a hankali itama hakanne zata kasance. Sai dai akwai wata allura da za’ai mata wadda gubar bazata yi tasiri a jikinta da wuri ba kamar shi”.
       A tare duk suka kalli Aunty Hannah bayan sun É—auke idonsu ga Dr Bonba daya gama bayanin.
     Kanta ta kaÉ—a musu tana watsa hannaye baya. “Miye na kallon nawa?, kun san dai Raudha É—iyar Ć™anwata ce. Duk da kuwa ina son zama first lady bashike nuna bana son abata ba. Nasan bai wuce kuce ya shawarar ta canja ba game da allurar riga kafin guba. Ku zauna kuyi tunani da hankalinku, babu ta yadda za’ai mu bari gubar tai tasiri a jikinsu lokaci guda, dan komai zai fito ne. Amma idan bayan ya shi ya mutu ne itama ta mutu za’a iya cewa zuciyartace ta buga saboda rashinsa itama tabisa”.
       “Woow!”.
Suka faɗa a tare suna tafawa. Shugaban ƙasa mai sauka yace, “Hannah kinada basira, anya kuwa idan mutumina ya zama shugaban ƙasa bake bazaki koma juya ƙasar ba kuwa?”.
        Wata shegiyar dariya tayi tana juya idanu, Alhaji Yaro glass ya sake rungumota jikinsa da manna mata kiss a kumatu. “Inaga shugaban Ć™asa biyu kam zakuyi”. Ya faÉ—a cikin raha. A can Ć™asan ransa kuwa yana ayyana ashe kuwa itama zata mutu nan kusa, dan Hannah bata isa shiga masa hanci bai fyatota ba duk da take matarsa………

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button