FARHATAL-QALB

FARHATAL-QALB 14

PG:14_

Ahankali ta janye idanun ta daga kan gate din gidan da suka shiga. Kwantaccen gashin kansa daga baya kawai ta iya hangowa alokacin da Umma Hadizan ta mayar mata da gilashin idanunta

“Sannu baki bugu a wani wajen ba ko?”

“Eh…! Umma “

“Tohm Allah ya tsare gaba. Ungo wannan kya saya ko awara ce idan an taso ku tara (break) ” Ta karasa tana mika mata nera talatin.

“Du? Nagode Umma. Allah ya saka da alkhairi.”

“Aamin Aamin.”

Har kan kwana Umma Hadiza ta raka Waheedah, Sannan ta juya ta shiga gidan aikin nata.

Waheedah na tafe akan hanyar karasawa makaranta tana tunanin gwaren da sukayi da mutumin da bataga fuskar sa ba sai gashin girar sa da na kansa alokacin daya shiga gidan su.

Dan siririn tsaki ta saki kawai a kasan maqoshi tace,

“Allah ya kyauta… Shi da ya bige ni ai sai ya ban hakuri. , Su masu kudinnan dama wasunsu sai ahankali wallahi.” Mita ta shiga yi sosai har ta karasa makaranta.

××THE ADAMS RES.××

Sashen da yake a matsayin na mazan gidan ya nufa. Ya shige dakin sa yana buga kofar da karfi.

Gaban mudubi ya tsaya yana kallon kansa, Ya yinda ya saka dayan hannun sa ya shafo kasan keyar sa yana sakin ajiyar zuciya. Bai san musabbabin da zuciyar sa ke wani irin zillo ba da farin cikin daya kasa sanin na menene.?

Knocking kofar dakin nasa akayi. Yana daga tsaye yace,

“Yes!! Come in….”

“Assalamu alaikum… Bross.”

“Wa’alaykm Salam! Maza “

“Abunda kayi ba halin ka bane … Ya za kai haka?”

“What about it? Mena yi ?” Ya karasa fada yana unbuttoning rigar jikin sa.

“Ka fini sanin me kayi ai..”

“Kaga ni wanka zanyi malam “

“Okay haka zaka ce? Fine.”

Har ya kai kofa zai fita. Ya saka hannun sa akan handle din zai murda. Ya kirawo sunan sa.

“Basher…”

Dan murmushi basher din yayi ya juya. Kai kana gani kasan jini ne su. Domin suna kama. Sai dai daya yafi daya haske da karan hanci.

“Uhm muna magana .. Ina sauraron ka. Meyasa kai haka? Meyasa ba ka tsaya ka nemi afuwar ta ba bayan kasan kai ne me laifi, faulty . ….Why?? Meyasa Zayn.?”

Wanda ya kira da Zayn ya dan yi murmushi kawai. Yayinda ya dora towel din hannun sa akan kafadar sa. Ya zauna a gefen kujera yana jan kasan leben sa.

“Magana nake maka Zayn “

“Basher. Bansani ba. Bansan meyasa ba. Kawai na tsinci kai na cikin wani yanayi marar misaltuwa. Bansan wane irin yanayi bane basher. Nasan kuma nayi laifi. But wait ai ba da sanayya nayi hakan ba. Beside itama da lefin ta …”

“Bangane da lefin ta ba. Meta yi? Bayan ance maka bata gani sosai musanman ganin kusa . Short sited ness…”

“Eh ina nufin hankalinta na wani wajen ta tsaya chak. Ni kuma na juyo muna magana da kai, Ai baya bata gani ko? So Allah ya bata hakuri. “

“At least seka tsaya ka bata hakurin acan Zayn. …..”

“Uhm ,”

“Ba uhm ba. Kasan baka kyauta ba “

“Nace Allah yabata hakuri yanzu ai ko. ? Kuma Allah yaga zuciya ta. “

“Kai ka sani , Matsalar ka ce. Mutum sai taurin kan tsiya.” Basher na karasa magana ya mike yayi ficewar sa cikin takaicin dan uwan nasa.

Yana fita Zayn ya sauke nannauyar ajiyar zuciya hade da saka hannu ya dafe saitin zuciar sa dake tsananta zillo tamkar zata fado kasa.

“Ya Rabbi…!!!” Ya furta ahankali.idanuwan sa a lumshe.

Bedside drawer ya janyo ya dakko wani memo dinsa da biro yayi rubutu kadan aciki ya rufe.

Bandaki ya shige bayan yayi addua. Shower yasakarwa kansa. Ya dade ruwan dumin na dukan jikin sa. Ya saka hannun sa biyu ya kwantar da gashin sa baya da ruwan yake duka. A duk sanda ya runtse idanun sa hotunan dazu kawai zuciar sa ke hasaso masa na shi da yarinyar nan.

Siririn tsaki ya dan saki yana mai sake sauke ajiyar zuciya a karo na ba adadi. Sihirtaccen kamshin ta da ya do ki kofofin hancin sa. Yayi matukar tasiri acikin ran sa, kwakwalwar sa kai dama gangar jklin sa.

Haka ya karasa wankan nan. Wanda kusan rabin sa duk tunanin Waheedah ne. Ya rasa mai yasa dede da second daya bai man ce ta ba.

Lamarin tamkar almara ya dauke sa. Don shi gaba daya mata basa gaban sa idan ba wanda suke jini daya ba ko yan uwa. Sai gashi, Wai yau shine ya tsinci kansa cikin tunanin mace. Macen ma wadda baisan a wacce duniyar take ba. Uwa uba daga haduwar tsautsayi.

Ya sake sakin tsaki yana kambama lamarin sosai.

“Ko dai ba mutum bace?” Ya tanbayi kansa shi kadai. Don ko da wasa Kwatankwacin haka bai taba faruwa da shi ba.

Haka ya karasa shiryawa cikin kananun kaya riga da wando na jeans. Yabi ya feshe jikin sa da turarukan sa dake jere akan dressing mirror.

Harda shinshina kwalaben ko hancin sa ne. Tabbas lamarin ya fara bashi mamaki. Yadda sosai kamshin ta ke yawo a duk wasu rassa na sa musanman hancin sa da ko kadan bai gushe da kamshin ba.

Ganin zai batawa kansa lokaci da wani shirmen wata yar karamar yarinya da a girme ya girme mata sosai. Hakan ya sashi ficewa daga cikin dakin nasa bayan ya murza key.

Kai tsaye ya wuce sashen mahaifiyar sa. Yana tafe yana yan addoin sa a kasan maqoshi.

Da sallama ya karasa shiga ciki yana dan daga murya.

“Wa’alaykm Salam. ” Cewar Umma Hadiza da ke goge jikin dispenser.

“Barka da safiya.” Ta gayshe dashi.

“Barka ina kwana?” Ya amsa ta yana kalle kallen inda zai hango mahaifiyar ta su.

Umma Hadiza sam bata gane shine wanda sukayi gware da Waheedah ba dazu, Saboda kayan jikin sa ma ba irin na dazu bane. Kuma dai bata karewa fuskar sa kallo ba dazun.

“Maaaa “

“Zayn., Ga ni nan.” Cewar Dr. Hameedah dake saukowa daga saman bene.

Durkusawa yayi har kasa ya gayshe ta. Ta amsa masa hade da saka masa albarka. Ta cigabada cewa,

“Wannan itace baiwar Allah da nake gaya muku. Sunan ta Hadiza. A dayar unguwar suke ta bayan mu dinnan.”

“Oh okay Allah sarki….!” Ya fada yana dan kallota da gefen idanun sa. Tamkar itace matar dazu. Don suna yanayi da yarinyar da sukayi gware.

“Ga abincin ka can akan dinning…….

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button