HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 26-30

***Suna shiga part dinsu tun daga kofa ya daga ta sama, ta saki
siririn ihu tana kankame shi, da gaske taji tsoro dan bata yi tunani ba, sai ji
tayi anyi sama da ita, kin ajiyeta yayi sai da ya kai karshen falon sannan ya
zaunar da ita ya bita ya zauna a gefenta yana dariya

 

“Kin fiyaa tsoro Allah!”

 

“Ai it was unexpected shiyasa.”

 

“Ba wani, tsoro dai kawai, ki yarda, you have to be strong,
kinsan dai ance a wife of a soldier is a soldier!”

 

” Wasa suke suma wallahi.” Ta saka dariya

 

” Haka dai aka ce.” Yayi dariyar shima

 

 

“Yawwa… Dazu na gani a WhatsApp wai anyi calling off
strike?”

 

” I can’t say, bari na kira naji, amma zaki koma ne? Ko a
samu wata school din daban?”

 

” Duk yadda akayi yayi.”

 

” Owk toh bari naji.” Yace yana ciro wayar sa daga
aljihu, yayi dialing number wani lecturer abokin sa, suka gaisa sannan ya
tambaye shi, baa gama daidaitawa ba amma dai akwai yiwuwar komawar nan kusa.
Ajiye wayar yayi ya fad’a mata yadda sukayi

 

“Matsalar k’asar nan kenan, yanzu fisabilillahi fiye da
9month ana strike amma gwamnati tayi shiru? Shikenan karatun yara ya lalace
akan wani dalili mara tushe, it’s so unfortunate gaskiya.”

 

“Wallahi har sai mutum ma ya gaji da zaman, babu dadi
sam.”

 

“Dole ai, Allah ya kyauta.”

 

“Amin.” Tace sai sukaayi shiru, chan kuma yace

 

“Bari muga idan basu daidaita ba, kawai sai mu chanja ko
Base ne, ko kuma wata private uni din na Kano.”

 

“Owk Allah ya zaba mana mafi alkhairi.”

 

” Amin Matata!”

 

*** Tare suka shiga ciki bayan sun kammala duk abinda ya kamata
su kammala a falon, zama yayi ya kunna system ya shiga aiki ita kuma ta wuce
toilet dan ta watsa ruwa tazo ta kwanta. Sharp sharp tayi wankan ta fito sanye
da rigar da ta cire , be kalle ta ba, har ta isa gaban wardrobe ta dauki wata
mara nauyi iyakar ta kasan guiwa, dan duk sauran kayan da take dasu anan ba zata
iya kwanciya dasu ba, idan ma ta saka tasan shi, zai iya yin karfa karfa ya
hanata yayi amfani da damar yayi mata wayo. A gajiye take jin ta yau din ba wai
don tayi wani aiki ba, bata san dalili ba gaba daya jikin ta ciwo yake mata,
wankan da tayi take saka ran zai dan saka taji dama-dama.

  Kallon ta yayi bayan ta
sako rigar, yayi mata alamar tazo, ta taho ta zauna agefen sa, ya cigaba da
aikin da yake na hada kan wasu takardu masu muhimmanci sosai, yana lura da ita
yadda jikinta yayi sanyi sosai, jawo ta yayi bayan ya dan matsar da system din,
ya kwantar da kanta a jikin shi

 

“Goodnight sweet dreams.” Ya rankwafo yayi mata peck a
kunci, lumshe idon ta tayi bacci na cin karfin ta sosai. Be san iya adadin
awoyin da ya dauka a wajen ba, ya dade sosai har sai da ya fara jin
bishi-bishi, sannan ya rufe system din, ya gyarata a hankali sannan ya tashi
yana mika, alwala yayi yazo yayi sallah raka’ah biyu, ya lura da ko shafa’i da
wutri da ta saba yau bata yi ba, be san wanne irin bacci take ji haka ba, dan
har ya gama aikin sa ya tashi ko motsawa batayi ba. Taimaka mata yayi zuwa
gadon ya kwantar da ita ya lullube mata iya kafarta, sannan ya kwanta bayan ya
rage kayan jikin sa ya rage daga shi sai boxer kawai.

  Cikin dare sosai taji
ishirwa, irin wadda bata taba jin irin ta ba, tashi tayi ta lallaba ta fito
bayan ta duba fridge din dakin ta tuna babu ruwa a ciki, ta manta kuma bata
kawo ba dan bata bar kowa cikin masu aikin sun taba shigar mata dakin ba,
iyakar su falo shima dan babu yadda zatayi ne amma ko yaushe suna BQ sai wani
abu me muhimmanci sannan take kiran su.

   A kitchen ta samu
ruwan, tasha sannan ta dauko karamin katan na ruwan ta taho dashi. Falon yayi
dim amma kuma akwai dan haske kadan da ya hasko ta corridor din kitchen da yake
a kunne, kafarta take sawa a hankali tana tafiyar har ta kai tsakiyar falon, da
yake falo ne katon gaske da sai kayi tafiya tsakanin kitchen da corridor din
bedrooms din, motsi taji kad’an kad’an, tana matsowa yana karuwa har ta kusa
kai wa corridor din abinda ta gani a wajen ya sakata daskarewa a wajen. Chak ta
tsaya ta kwalla wata irin kara da ta tashi Moh daga bacci, ya mike a firgice
yana kiran sunan ta, sai kuma yayi hanyar fita daga dakin da sassarfa kirjin sa
na bugawa da karfi!

 

 

 

 

BIYAN BASHI ⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️😂😂😂😂😂

2/7/22, 19:06 – Buhainat: Halin Girma

      29

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

******* �

 

Tana daf da shigowa ta kira Samha tace ta wuce part dinta dan ba
zata iya zuwa wajen Ammi ba, tashi tayi ta fita bayan ta saka wayarta a cikin
purse dinta, taja kofar ta nufi wajen Laila din da ya kasance nata ita kadai
kusa da na Kilishi. A waje suka hadu ita tana fitowa daga mota ita kuma tazo
daidai bangaren, sallamar driver tayi yaran suka dauko mata kaya suka biyo ta,
suka hadu suka rankaya ciki tare da Samha. Bayan sun zaune ne Lailan ta tuge
mayafin kanta da yake dan yalolo da ta yane kan, ji taka kamar iska bata ratsa
kan nata sosai shiyasa duk take jin ranta a jagule babu dadi, ga haushin abinda
ya faru ga na karatun ta da take jin kamar ta rasa komai a yanxu.

 

“Kin ganki kuwa Queen, ya akayi haka?”

 

“Menene ma ba zaki gani ba, hmm wallahi bansan waye yayi
min zagon k’asa ba, amma ko waye toh tabbas baya kaunata ko kad’an!”

 

” Kin binciki Hadimar nan? Ba kince ita kadai tasan da plan
din ba.”

 

Girgiza kai tayi

 

” Ba ita bace ba, someone very close to me ne, dan yadda ba
kowa ke shiga part din nan ba, toh lallai wanda yake da direct access da part
din ne.”

 

” Lallai, gaskiya ko waye be kyauta mana ba, yanzu ya ake
ciki?”

 

” Wai hakuri? Wallahi ban ba,kinsan yadda nake son Capt tun
muna school haka shima kinsan kaunar da yake min ba kad’an bace, ba zan iya
rayuwa da kowa ba sai shi, bayan haka kinsan matsala ta da Dr. Bryan
Ford.”

 

” Haka ne, toh shikenan yanzu menene next move dinki?”

 

” Har yanxu ban dawo daidai ba, I need time to recover
nasan me zanyi.”

 

” Shikenan, duk abinda zakiyi dai kiyi informing dina, zan
baki shawara yadda ya kamata.”

 

” I know I can count on you, Nagode Bestie!”

 

“DM!”

 

 Tayi murmushi yana
relaxing sosai akan kujerar, tana tunanin yadda zatayi amfani da Laila ta samu
cikar burin ta!

   Sai wajen tara sannan
suka tafi, bayan Maman sun gama zantawa da Ammi, babbar aminiyar ta ce sama da
kowa a kaf adamawa dan da ita ta fara sabawa lokacin da aure ya kawota, sannan
yaransu ma tare suka taso ita tana da yara biyar compared to Ammi da take da
guda daya tal…

   Zuciyar ta fari kal
sanda suka isa gida, ta san ko babu komai zata dinga samun duk information din
da take so ta bakin Laila, tunda tayi masifar yarda da ita fiye da yadda ma ta
yarda da uwarta mahaifiya. Bata da kirki ko kad’an idan har ka shiga gonar ta,
amma kuma tana masifar ganin mutuncin Samha din, dan itace tafi mata kowa a
yanzu, gani take ma babu me kaunar ta sai Samha din kawai. Ko Kilishi ta san ta
Kamal kawai take yi ba tata ba, shiyasa itama bata wani sanar da ita idan
zatayi abu sai dai daga baya, daga Samha sai amintacciyar hadimar ta guda daya
wadda zata iya bada ranta fansa ga Laila din saboda tsabar biyayyar da take
mata.

  Wurgi tayi da tarkacen
da ta debo daga mota tayi a saman gadon ta, ta kwanta tana kallon sama ba tare
da ta cire dogon takalmin kafarta ba, murmushi take ita kadai duk kuwa da
abinda Muhammad din yayi ya bakanta mata rai, amma kuma ta raina yarinyar da ya
kira ta da matarsa, a shekaru ba wata babba bace haka ma wayewar rayuwar duniya
sam bata cikin sahun amma kuma tana da nutsuwa a yanayin ta, da kuma iya
handling abu dan yadda tayi da taji da wanda take waya ya matukar bata mamaki,
kamar bata fahimci komai ba bayan sarai ta gane, kuma bata ko bi takanta ba ,ko
ta tuhume shi ko ta chanja masa fuska sanda ya shigo, sai ma ta tarbi mijinta
da fara’ar da ta mantar dashi komai da kowa.

  Tashi tayi tsaye ta soma
zagaye a tsakanin dakin tana jin kamar taje ta jawo ta da karfin gaske ta fidda
ta daga gidan, duk yadda suka kai da wayewa amma ya tsallake su ya dauko wadda
bata kai ko rabin ajin sa ba, adah Laila kawai take jin haushi amma yanzu na
Laila ya daina damunta, dan tasan babu wani abu da zatayi sai da sanin ta,
yarinya karama ce yanzu take neman zame mata ciwon ido.

  

 

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button