HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 3

 *HALIN GIRMA*Hafsat Rano

3

****

Tsaye yayi jikin gate din gidan yana kare masa kallo, tunanin ta yadda zai fara shiga yake musamman da ba sanin sunan ta yayi ba, ya dai saka mata suna da zuciyar sa kuma be taba yunkurin tsaidata balle yaji sunan ta ba.

  Lekowa maigadin gidan yayi, ganin mutum a tsaye yasa shi fitowa gaba daya

“Sannu.” Yace masa yana kokarin daidaita muryar sa

“Yawwa sannu, wa kake nema?” Maigadin ya tambaye shi yana kare masa kallon cikin rashin sani.

Nan fa ake yinta, shiru yayi kamar me nazari shi kuma maigadin ya kafe shi da ido yana son jin abinda ya kawo shi.

“Am… Amm nazo wajen…”

“Malam Iliya.” Zeenat dake fitowa ta kirashi tana leko wa.

“Na’am ranki ya dade!”

“Siyo min kati na 500 kayi sauri dan Allah.”

“Yanzu kuwa, ga wani bako nan bansan wajen wa yazo ba dai kin tambaye shi.” 

Yayi gaba, kallon sa tayi tun daga sama har kasa a wulakanci ta yatsine baki tace

“Wa kake nema kai kuma Malam?”

“Yar uwarki nake nema dan Allah, wata me zuwa islamiya kasan layin nan doguwa haka fara.”

“Waye kai a wajen ta?”

Kallon cikin ido yayi mata, ta ja tsaki tana juya fuskar ta

“Ban fiye son kallo ba Malam, ka shigo ciki bari na tura maka ita dama ai sai dai ita din…”

Gaba tayi tana cigaba da sababi

“A kaf gidan nan wa zai kwaso mutum irin wannman dan Allah! Ji shi kamar wani mahaukaci.” 

Sai ta kwashe da dariya tana sake daga kafa.

A kwance ta tarar da Iman tana danna wayar ta da ba kasafai ta cika wani amfani da ita ba, yanzun ma wani labari ne yaja hankalin ta a Facebook take karantawa.

” Kina da babban bako a waje da galleliyar ranar nan.”

” Waye?”

” Idan kika je idon ki zai gane miki shi.”

” Owk.” 

    Tace tana tashi zaune, har yanzu bata gama dawowa daidai ba amma haka ta karfafa jikinta tayi ayyukan ta. Hijab ta saka madaidaici akan doguwar rigar jikinta ta fito. Daga chan hanyar gate ta hange shi a tsaye ya rataye hannayen sa a bayan sa, kansa a kasa yana wasa da kafar sa. 

   Dogo ne na ajin farko, jikin sa ko ina a murje babu alamun rama ko kad’an, yanayin shigar sa bata dace da tsarin zubin halittar sa ba, kafin ta karasa ta gama ayyana shi a ranta. Da sallama ta isa, ya dago da sauri a lokaci daya kwayar idon sa ta sauka a cikin ta ta, gabanta ne yayi masifar faduwa, tayi saurin janye idon ta, ta russuna kad’an tace

“Ina wuni?” Lumshe idon sa yayi ya bud’e, fuskar sa dake cike da kasumba ta dan yi fadi alamun farin ciki, ya tattaro dukkan nutsuwa da jaruntar sa yayi gyaran murya yace

“Kina lafiya?”

“Alhamdulillah.” Tace a gajarce ta matsa wajen wasu kujerun roba guda biyu ta dauko daya ta kawo masa.

“Bismillah zauna kana ta tsaiwa.”

Hannun sa ya dora a saman kujerar ta kalli hannun yayi saurin janye shi ya zauna sannan yace

“Kefa?” 

Wani dan tudu a wajen ta nuna masa da hannu, ta zauna akai tana jin duk ta takura ganin yadda yake bin ta da kallo da wasu irin idanun sa da suka sake shiga ciki sosai.

“Na same ki lafiya? Ya gida yasu Mama da yan uwa?”

“Lafiya lou Alhamdulillah.”

“Ban gane waye ba amma?”

“Me sonki ne, me kaunar ki da son duk wani farin cikin ki, yan kwanakin nan da na dauka banga wucewar ki ba, sun zame min kwanaki mafiya muni a rayuwa ta. Na kan zauna a duk yini ina dakon wucewarki, ban taba yunkurin yi miki magana ba, sai dai zuciya ta, ta gaza dauka har sai dana biyo bayanki, ina fatan ban takura miki ba?”

Girgiza kai tayi tana jin wani bawai, wai ita ake karantawa wannan kalaman, idan har taji daidai wato ya dade yana bibiyar ta, bata ma sani ba.

” Kinyi shiru!” Yace yana gyara zaman sa

Shirun ta sake yi dan bata san me zata ce masa ba.

” Nasan dama karambani ne irin nawa, ban kai ajin ko da me wanke miki takalmi bane, kiyi hakuri idan nayi miki shishigi a rayuwar ki.”

” A ah wallahi, ba haka bane ba, a kalla mutumin da yace yana son ka ai yafi makiyinka, nagode sosai da soyayyar ka gareni.”  Tace da sauri sannan tayi murmushi, ji yayi kamar zuciyar sa zata fito daga kirjin sa, ya danne sosai ya maida mata murnushin

“Nagode Nuryyy… Nagode sosai.”

Shiru ya biyo baya, ta dinga wasa da gefen Hijab dinta shi kuma yana satar kallon ta. Nutsuwarta tafi komai tafiya dashi.

“Bari na wuce.”

Da sauri ta mike kamar me jiran kad’an, 

 

“Ka gaida gida.” Tace tana saurin yin gaba

“Ko zan samu number waya dan Allah?”

Tsayawa tayi ta mika masa hannu, ya shafa aljihun sa dukka

“Kinga garin sauri na manta wayar a daki, amma zan rik’e fad’a min.”

“Ok .” Tace ta karanto masa, 

” Nagode sunana Muhammad.”

” Fatima, ka gaida gida.”

Ta juya ta barshi a tsaye a wajen. Sake maimaita sunan Fatiman yayi, ya saki murmushi a hankali sannan ya juya ya fice daga gidan.

***A zaune a falo ta tarar da Mama na waya, zata wuce ta tsaida ta da hannu ta cigaba da wayar ta

” Ba za dai ka bar maganar nan ba ko Khalil? Toh shikenan sai kazo din dai ma sake tattaunata, idan yaso ko a dangi ne sai ka duba sosai ba za’a rasa ba ai.”

Amsa ya bata daga bangaren sa, ta ja tsaki tace

” Matsalata da kai kafiya wallahi toh sai anjima, sai kazo din.”

Ta kashe wayar ta dangwarar da ita a gefen ta

” Na rasa shegen taurin kai irin na Khalil wallahi, sam baya kaunar ya ganni cikin farin ciki, mtsw.”

Ta sake jan tsaki a karo na ba adadi.

” Daga ina kike?”ta jeho mata tambayar bayan ta riga ta san inda take.

” Wani ne yazo dama.”

” Waye shi?”

” Bansan shi ba nima, wai a bayan layi yake.”

” Toh kina jina? Idan zaki yiwa kanki kiyamullaili ki rik’e shi hannu bibiyu toh, idan kuma kika yi wasarairai da shi shima ya gudu kamar sauran, sai ki zauna muyi ta jerawa a gidan nan,tunda dai bakin hali ya hana samarin zama kowa yazo sai ya tafi.”

Bata dago ba, bata kuma ce kala ba, tana jin Maman tana kuma ajiye kowacce magana a mazaunin da ya dace, sai da ta gama yi mata cin fuskar sanann tace

” Khalil zai zo gobe, babu ruwanki dashi da shiga harkar sa, ko falo bana so naga kina kaiwa da komowa har ya tafi, zan fi so ki tattara ki koma wajen Gaji da zama aikin ma na yafe miki, idan ya gama kwanakin ya tafi shikenan, bana son daukar magana dan shi ba kunya magana yake ji ba, kinji dai na gaya miki.”

” In sha Allah.” 

” Jeki.”

Tashi tayi ta bita da kallo ranta na tafasa, da gaske take kishi da ita dukda bata zauna da mahaifiyar ta ba, amma duk sanda ta kalle ta sai ta tuno abinda ya faru.

****A guje suka taso ganin ya fito, ya nufi wajen da jerin motocin ke fake suna jiran sa, ransa a bace yake da kiran amma bashi da ikon kin amsawa, dole ya ajiye shirin sa a gefe ya kirawo su domin ba zai taba yarda da shigar masa shirin sa ba. Shiyasa su kansu basu da yakini ko masaniyar komai, dan ya tabbatar da zasu taimaka wajen lalata masa shirin sa. Dan su din basu da ikon kansu sai abinda aka gindaya musu.

   Bud’e masa bayan motar daya daga ciki yayi, ya russuna kad’an sannan yace

“We are very sorry sir!”

Be tanka masa ba, ya shige cikin motar ya jingina bayan sa da kujerar ya lumshe idon sa.

“Oga Main house zamu?” Yayi tambayar yana tada motar

   

“Lamido Crescent!” Yace yana sake rufe idon sa. 

Chan suka wuce direct, suna isa ya fito ya shige ciki, tun daga falo ya fara wurgi da kayan jikin sa, ya rage daga shi sai boxer da farar singlet, kallon kansa yayi a jikin tangamemen mudubin dake tsaye kikam a falon, ya juya ya sake juyawa sannan ya wuce zuwa cikin bedroom din sa.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button