INAYAH 31-40

Sam batason kowa ya rabi ‘danta tafison kulawarsa da komai akanta ita kadai,
Shikuma Allah yayisa Mai tausayi da taimako tareda mutunta mutane Musamman marasa qarfi kusan sune mutanensa Dan yafison yayi mu’amala da wainda zasu ringa qaruwa dashi suna samun taimakonsa dan kawar da tasu matsalar.
Mahaifiyarsa kuma hakan ne yasata ta tsani duk wasu marasa karfin dake taredashi sbd ganin sunason samun kusanci dashi,
Ba abinda yake Basu bane baqin cikinta Dan idan duka zai Basu dukiya batada damuwa ita damuwarta kada kowa ya samu kusanci da ‘danta Bayan ita.
A American University of Nigeria yake karatunsa badan Haj umma tasoba tabarsa yake karatu a wani garinba sai Dan hakan mahaifinsa yaso,
Burin mahaifinsane ganin yayi karatunda zai mallaki komai nasa ya Gina kansa da kansa.
Fara karatunsa da yanda yake Dan jimawa baya gida yasa su Anty juwairiyyah suka fara samun shiga gurin Haj umma har suka fara kawo sabani tsakaninta da ABDULMAJEED ta hanyar saka Mata zargi Mai girma akan yafara ‘yan Mata hankinsa akansu yake Nan gaba ma mace Zata Raba tsakaninta da ‘danta.
Hankalin Haj umma tashi yayi sosai sbd yanda idonta ya rufe akan kaunar da kishin danta yasa komai aka fada Mata yarda takeyi Musamman da ABDULMAJEED din yayi budurwa kullum cikin kiransa take Dan tun Kiran Sumayya din na damunsa harya daina damunsa Dole ya saba.
Soyayyar MAJEED da sumayya ta daga hankalin Haj umma sbd sosai yanzu ta tabbarda mace Zata rabata da Dan ta Dan haka ta rufe Ido tamasa kaca kaca da fada takuma hanasa kula Mata saiya kammala karatun ita Zata Nemo masa matanda zai aura.
Ganin yanda ranta ya baci sosai yasa MAJEED din takaita muamalarsa da sumayya kwata kwata baisake bi takanta.
Amma duk da hakan shikenan Haj umma taringa saka Masa Ido takasa yarda dashi.
Wannan yakawo babban gibin dayasa su Anty juwairiyyah qarasa saka zargi da rashin sukuni a tsaninin Haj umma da majeed kusan yanzu kullum cikin fitinarta da fadanta yake akan Yana hulda da ‘yan Mata shiyasa yake jimawa a makaranta kafin yadawo hutu gida.
Wannan ne babban matsalar data fara kunno Kai a tsakaninsa da mahaifiyarsa wadda kwata kwata Bata yarda dashi sosai yanzu.
Su Anty juwairiyyah kuwa yanzu zancensune abin yardarta
Duk abinda suka fada mata hawa takeyi ta zauna daram tayita fada
Abbansu baya raye bare ya ganarda ita gaskiyar rashin kyautawa da tunani akan abinda takeyi.
*Shigowarsa gidan Kai tsaye Palo yashigo lokacin daga hajiyar sai Anty juwairiyyah da rumanah ‘yar anty juwairiyyah suna zaune palon anty juwairiyyah na bubbude kayanta dasuka iso daga Dubai yau na tsadaddun laces da abayas datake saidawa sosai.
Ko kallonsa hajiya bataiba lokacinda ya zauna kusada ita Yana riqo hannunta cikeda kulawa yace”
Umma…
Zare hannunta tayi tana juyowa ta kallesa fuska ba walwala tace”
Meya hadaka da asibiti kake warin asibitin?
Tun asuba fa akace ka fita¿
Ina kaje?
Ajiyar zuciya yayi cikin Hana kansa Jin rashin Jin dadin zancenta sbd takasa daina saka Masa dokar duk Ina yaje da Inda zashi saiya fada Mata bayan Shiba yaro bane da girmansa take Masa irin hakan,
Amma Kuma uwace Babu yanda zaiyi da ita bakuma zai iyajin haushintaba sbd yanda take kaunarsa haka yake tsananin kaunarta shima Dan tafiye Masa komai a rayuwarsa.
Ahankali ya bude Baki zai fada Mata abinda yake faruwa saiya dakata sbd tabbas yasan atake zatace Bata yafe yakoma gurin babynba yabarta can asibitin Susan yanda zasuyi da ita.
Ajiyar zuciya yayi tareda sakin murmushin boye damuwarsa yace”
Dubiya naje wani asibiti a kubwa.
Kasa yarda hajiyan tayi tana kallon fuskarsa dake kokarin Tona asirinsa sbd Bai iya qaryaba baikuma taba yintabama.
Miqewa yayi ya wuce dakinsa yayi wanka ya shirya yakuma sulalewa ya fice gidan batareda sun saniba.
Har dare Bai dawoba sai guraren 10 yadawo ya shige ya kwanta.
Washe garima daqyar ya iya tsayawa yasha ruwan tea kawai ya Kuma ficewa zuwa asibiti.
Kwana biyu kowa gidan ya saka Masa Ido ganin duk yabi ya rikice baya wani cikin nutsuwa gashi sai boye boye yakeyi sbd harga Allah bazai iya barin babynba shima hakama mahaifiyarsa yasan bazata taba Bari su dauki ‘yar ba Dan haka hankalinsa ya tashi sosai,
Yayi yawon bincike akan gidan marayu Amma Babu Inda yaji bayanin daya kwantar Masa da hankali Dan haka yasake shiga tsaka Mai wuya.
Ta Bangare Daya ya rikice ya haukace gurin Neman uwar babyn harya gaji Babu labari,
Komai yafara tsananta lalace Masa ne bayanda anty safiyyah ta ringa bin diddiqinsa tagano asibitin dayake zuwa kullum harma da babyn dayake jinya mai amfani da sunansa ABDULMAJEEDs.
Hankali tashe cikeda firgici da mamaki takawo labarin gida Inda suka dunguma sukaje suka ganarwa idonsu Kuma suka tabbatarda babyn dai ta ABDULMAJEED dince ta hanyar bayaninda nurse Tai musu shine mahaifin babyn.
Uwar babyn suka tambaya tace musu ta rasu gun haihuwa.
Dayake suma asibitin sun dade dafara gulmarsa akan kila baasan ya haifi yarinyarba shiyasa yakasa kawo ‘yan uwansa su tayasa hidimar babyn.
Gida suka koma hankali tashe suka zayyanewa hajiya komai.
Kasa yarda tayi da Abdul dinta zaiyi abinda suke fada kula Mata da aikata Zina harma da haihuwar ‘yar gaban fatiha.
Sunsan zaayi hakan Dan haka suka dauketa suka kwasa zuwa asibitin
Cikin saa kuwa suna zuwa suka taddasa rungumeda babyn an jikinsa cikin tsananin kulawa.
Sallamarsu ake tunanin Yi zuwa gobe dan haka yake Jin sanyi ta wani bangaren Kuma tashin hankalin yanda zaiyi da babyn.