NOVELSUncategorized

WUTSIYAR RAKUMI 20

*_NO.  20_*


………..Haka rayuwar taci gaba da tafiya a gidan nasu Ummu, babu mai shiga harkar wani tsakaninta da Yaa Amaan, iyakaci randa suka haɗu ta gaisheshi,
idan ya gadama ya amsa koya ɗaga mata hannu yay gaba, idan basu 7haɗuba kuwa ko oho, baruwansa da tanada lafiya ko akasin hakan.
     Abin na damunta matuƙa, ga kewar ahalinta da a kullu yaumin take a ciki, sai dai batada wata hanyar jinsu koda a wayane, dan batada number ɗin kowa, idanma tana dashi ina waya?, dama wannan rayuwar ta gudarma kanta tun farko, amma sai Baba ya kasa fahimtarta, tayaya ɗan gayu ɗan boko ɗan manyan mutane irin Yaa Amaan zai so ƴar ƙauye irinta, mai karatu iya secondary school? Bayan ƴaƴan manyanma dake amsa sunan ƙwarya tabi ƙwarya a tsakaninsu basu isheshi ko kalloba saboda tsabar murɗin hali, to bare ita kuma karan kaɗa miya, Inhar Baseer da suka rayu tare a gari ɗaya, matsayi ɗaya, zai gujeta bayan ALLAH yay masa wani nasibi to lallai kuwa ɗan gayu kamar Amaan bazai taɓa ya sota ba.
       Waɗannan tunanin sune suka zame mata abokan rayuwa, sai A’i dake jin daɗin halin da take ganin Ummu ɗin itada uwar ɗakinta Momcy, idan kaga walwalar Ummu to maman Ahmad ce tazo gidan, dan bata wani sakama desmond sosai, shi kansa yana girmamata tamakar yanda yake girmama wanda ya ajiyeta, dukda kuwa ya girmeta sosai.

★★★★

     Yau ta kasance laraba, haka kawai Ummu ta tashi zuciyarta babu daɗi, ga damuwa irinta kewa. Zaman ɗakinne ya isheta yau dai tafito harabar gidan dantasha iska, sanye take da doguwar riga ta atanfa, saboda ƴar ramar datai sai rigar tai mata burun-burun, saɓanin da datake cikata fam.
       Tayi nisa sosai a tunani har motarsa tashigo bata saniba, tunda suka shigo a kanta ya sauke manyan idanunsa, gajeran tsaki yaja kafin ya fito bayan Osin ya buɗe masa motar, shifa inma ba ganinta yayba mantawa yake da ita a gidan, garama idan yaga tsohuwar da suke tare wadda sam matar batai masaba ne yakan tuna da akwai mace matar aurensa wai a gidan.
           Sanye yake cikin kakin sojoji, sun masa ƙyau sosai dukda babu hula a kansa, fuskarnan tam babu alamun fara’a, tamkarma yana tare da damuwa.
       Takunsane ya ankarar da Ummukulsoom da batasan da shigowar tasaba, tai azamar ɗago kanta tareda sauke idanunta a kansa batareda ta shiryaba.
    Ba ƙaramar faɗuwa gabanta yayiba ganin ya kafeta da mayun idanunsa yana mata kallon sama da ƙasa, tamkar munafuka haka ta taso ta nufoshi tana masa sannu da zuwa, kallo ɗaya zakai mata ka fahimci kamar a firgicema take.
    Bai ko amsaba yay gaba abinsa yana sakin wani siririn tsakin ƙasan maƙoshi, hakan saiya kuma sanyaya jikin Ummu har hawaye na cika idanunta.

      Koda yashiga bai zauna a falonba, ya zube saman lafiyayyen gadonsa yana sauke wani nannauyan numfashi, dolenema yabi shawarar mahaifiyarsa koma yace Umarninta, anzo gaɓar da dolene sai yarinyarcan tabar gidansa, duk yanda Momcy ta tsara masa haka zaiyi, yasan wannan hanyarce kawai zata sakashi rabuwa da Dad lafiya batareda yaɗau zafi a wannan lamarinba.
     Ya lumshe idanunsa ya buɗe a hankali, kafin yatashi zaune sosai ya jawo drowa ɗin gefen gadon ya fiddo wani madaidaicin note book da pen, shiru yay tsawon lokaci yana kallon takardar, zuciyarsa na masa gargaɗi akan kar yayi haka, yayinda watacan ke angizashi akan hakan shine kawai mafita, ya saketa kawai, yarinyar bata dace da shiba, mizaiyi da baƙauya mara zurfin ilimi, ƙwaila.
     Kansa ya dafe tareda rumtse manyan idanunsa da ƙarfi, saiya koma ya kwanta ya cillar da biron yana jan wani tsakin mai ƙarfi.
   Dai-dai nan wayarsa ta fara ring, yay burus da ita harta tsinke aka sake kira, tsakin ya kumaja da ƙosawa da kiran, kafin ya cirota a aljihu ya buɗe idanunsa, Momcy ce, dan haka ya kirata saboda na biyunma ya tsinke.
       “Yaya Fodio ka rubuta mata?”.
      Numfashi ya sauke a hankali, murya a daƙile yace, “Momcy wlhy na kasa, sai nake ganin tamkar bamma dad adalciba, tamkar na wa…….”
     “Dalla yimin shiru shashasha shanyayye kawai, wlhy ban taɓa sanin kai ba jarumi bane sai yanzu Fodio, shin kodai kaima son nata kake?.”
     “Haba Mom, ni wlhy ban taɓajin son yarinyarnan a rainaba, mitake dashi da zan sota? Kawai na karɓetane a matsayin zaɓin mahaifina zuwa wani lokaci, da gudun saɓa masa, banaso ya kalleni mara biyayya a garesa”.
        “Yo aiko kayi masa biyayya shima ya sani, tunda aka ɗaura maka aure batareda jin ra’ayinka ba, aka kuma kawo maka yarinyar ka karɓa batare da bijirewaba, Fodio nagaji da gutsira magana akan wannan banzan auren naka, wlhy a wannan karon idan har baka saki yarinyarnanba saina tsine maka……..”
     A matuƙar firgice ya tashi zaune, “Momcy!”.
       “Eh kirani da kyau, wannan shine umarnin ƙarshe dazan baka wlhy kaji na faɗa maka”.
      “ALLAH ya huci zuciyarki, indai maganar sakine an gama, gobe zansa a kawota”.
     “Ina? Kasata a mota tanufi ƙauyensu badai nan gidanba, kuma ida ya tambayeka dalili kasan yadda zaka kare kanka, karkuma sunana ya fito a ciki”.
     “To” kawai yace mata ya yanke wayar.
    Hakan ba ƙaramin ɓata ran Momcy yay ba, itakam lamarin Fodio har tsoro yake bata, ta tabbata da yanason wannan yarinyar komi zatai bazai saketaba, ai tagodema ALLAH da zuciyarsa bata sotaba.
    
       Koda ya kashe wayar saiya kasa rubuta sakin, har aka kira sallar magrib yana saƙawa da kwancewa, saida yafito zaje massalacine yanufi ƙofar ɗakinta, batareda knocking ba ko sallama ya tura ƙofar ya leƙa kansa.
      Idonsa karaf akan ƙirjin Ummu dake ƙokarin saka riga, yayunda itakuma tai saurin duƙewa ƙasa ta rufe jikinta.
     Wani tsaki yaja dahar zuci Ummu ta jisa, kafin a matukar hasale ya buga ƙofar ya shigo sosai yana wani harare-harare, “K ki haɗa dukkan abinda kika san nakine a gidannan”.
    Iya abinda kawai yace mata kenan ya juya ya fita abinsa zuciyarsa na tsantsar takaici da ganinta, yatsani ƙwailar mace, dukda baya neman mata, bai taɓa zina ba a rayuwarsa, a tsarinsa shine ya auri cikakkiyar mace wadda tako ina ta haɗu, yatsani koda a bokansa yaga sun auri ƴar yarinya marar cikar halitta, shikam ganinma yanda take a shafene yakuma sakajin zuciyarsa tsanar zama da ita, lallai maganar Momcy gaskiyane, tsakaninsa da yarinyarnan *wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa.*

     
      Ummu dai ya barota cikin ruɗani, lokaci ɗaya jinta da ganinta suka gushe, da kyar ta iya ƙarasa saka rigar takoma bakin gado ta zauna tareda rabga tagumi, gaba ɗaya tunaninta ya gama tsayawa cak, tama rasa yazata fassara umarnin nasa.
      Har akai salla a masallacin Barrack ɗin aka sallame bata motsaba a wajen, saida isha’i ta kawo jikine ta iya yunkurawa dakyar tai salla tana hawayen da tun ɗazu basuzoba sai lokacin. Koda ta idar bata zaunaba, tsaf tashiga haɗa kayanta kamar yanda ya faɗa, tanayi tana hawaye, duk abinda ta iske a ɗakinma ta haɗashi waje ɗaya, hatta da kayan lefenta dako ɗayama ba’a ɗinkaba, sai dogayen riguna dana barci dataita sakawa, suma duk ta maidasu a akwatin. dan tasandai labarin gizo baya wuce na ƙoƙi, tunda dama ɗazun ta ritsa A’i na waya da Momcy.
      Komai ta haɗa abunta waje ɗaya, sai dai harta kwanta bai sake shigowa ba, dukdama barcin nata rabi da rabi ya zama.


*_Washe gari_*

    Ta idar da sallar asubahi ya shigo ɗakin hannunsa ɗauke da takarda guda biyu, ko kallonta bai yiba ya ɗorasu akan mirror tareda jingina da jikin mirror ɗin, murya a matukar daƙile yace, “Banida lokacin miki dogon bayani akan komai, sai dai kawai nace miki kisan maganar da zaki faɗama Dad akan zamanki a gidannan, karkuma ki kuskura sunana kona Momcy yafito a ciki, bakikai maceba balle har zuciyata ni Usman Majmud Usaman ta soki, banason ƙwailar mace mara zurfin ilimi, na sakeki saki ɗaya, wannan kuɗin kiyi amfani dashi, ga driver can yana jiranki a waje”.
       Ko motsi Ummu batayiba harya gama jawabinsa, saima kafesa da ido datai tamkar tasamu magiji, tana masa kallo irin wanda tunda tazo gidan bata taɓa nutsuwar masaba koda a sace, harya ficema bata dawo hayyacintaba.
        A’i da yau takejinta fayau tashigo ita da desmond da baisan abinda ke faruwaba, sudai ance kawai suzo su fidda kaya.
     Dukkan kayan da Ummu ta haɗa suka shiga ɗiba suna fita dasu, hatta da akwatunanta na lefe dayace su ɗaukar mata saida suka fiddasu.
       Saida suka gama fidda komaine tadawo hayyacinta, wasu hawayen baƙin ciki suka gangaro bisa kumatunta, lallai ta yarda *Namiji ɗan kunama ne* miyasa maza sukeson wasa da *ZUCIYARTA DA RAYUWARTA NE?*, Basiru ya kaɗa nasa taken, yau ga Amaan ya karɓi garayar, a hankali ta miƙe zuwa gaban mirror inda ya ajiye takardun biyu, ta farko ta taɓa taji mai kuɗince, dan haka saita ajiye ta ɗauki ɗayar tareda gyara tsayuwarta tana bin kanta da kallo a cikin madubin.
     Wani malalacin murmushi ta saki tareda share hawayen dake bin kumatun nata dukda basu daina fitaba, ta nuna kanta da take kallo acikin madubi tana magana cikin kakkausar murya da hasala irin wadda ba’a taɓa sanin tana da itaba, tace,
      “Minene narasa na mace dahar maza suke neman maidani cingom?, kowa ya tauna zaƙin ya ƙare saiya yadda matsayin amfanina ya kare, Basiru ka yaudareni alokacin da nake buƙatarka, kaci zarafina a cikin garina na haihuwa saboda kasamu ƴar masu kuɗi mai zurfin ilimi, nayi kuka, nayi ciwo saboda sonka dayayma zuciyata illa. Usman Mahmud Usaman ni Ummukulsoom Buhari ka kira da ƙwaila, marar ilimi, dukda nama iyayena biyayyane na aureka badan nima naji sonkaba, to lallai a wannan karon ban dace da zama mace mai rauni akan tozarcin ƴaƴa mazaba, ban cancanci sake bama wani namiji damar cin tuwo a kainaba, anyi biyu ba za’a sake na ukuba, na ɗauki alwashin zame muku *_WUTSIYAR RAƘUMI_* daga kaina bazaku sake raina ɗiya mace ba, zan tabbatar muku da cewa ɗiya mace ma mutumce tamkar kowa, zan tabbatar muku cewa dukiya ba ita bace ta banbanta tsakanin mutane, zan tabbatar muku da cewa Duk abinda *_ƳAN BIRNI SUKAI ƳAN ƘAUYEMA ZASUYI MAFIYINSA_*, kalmarka daka sanarma karuwarka cewa *_ABUN BA’A JIKI BANE_* tabbas ni Ummukulsoom Buhari ɗilau babban gida saina tabbatar maka da ita inhar ina numfashi a doron duniya, saina zamarma mazaje masu irin halayyarku *RAINA KAMA..!!*” ta faɗa da naushin mirror batareda tunanin komaiba.
    Ko takan hannunta dake jini batabiba ta figi takardar ta fice tareda bangaje A’i dake tsaye a bayanta, sai dai zuwanta kenan bataji dukkan alwashin Ummukulsoom ba.
      Galala A’i tabi Ummu da kallo baki a hangame, “Tofa, kekuma sakin da sabon salo yazo miki na nuna rashin tarbiyya? Eh lallai keko jar miyar dasamun (desmond???????????? ) da wainar ƙwai ta ratsaki, to wlhy bazan bi motarkuba ta kasuwa zanje na hau, garama mu rabata hanya tun anan karkije ƙaramin haukarki ya sakaki shakeni”.
      Oho Ummu batasan tanaiba, shi kansa boss Amaan dake zaune a falon yana jiran fitowarta ko kallonsa bataiba ta fice abinta, shima bakinsa ya taɓe tareda ɗage kafaɗa alamar matsalartace. Dan baya buƙatar ɓata ransa a kanta, a ganinsa batakai matsayinba, dadai babu Dad a tsakaninsu lallai saiya koya mata tarbiyya da girmama manya.

       Dukkan kayan Ummukulsoom dana A’i angama lodasu a mota, danhaka Ummu tashige mota abinta tana koƙarin danne wutar dake ruruwa a ranta ta tsananin fushin da bata taɓa tunani ko sanin tana da itaba, tabbas tasan tun a kuruciyarta ta tsani wulaƙanci, amma sam batada zafi ko hayaniya, saidaifa daga wannan ranar tayi alƙawarin shafe babin wancan tarihin ta maye gurbinsa da jarumta.

       Desmond harda kukansa saboda ganin Ummu zata tafi, dukda baisan ainahin abinda ke faruwarba sai da A’i ta sanar masa cikin ƙwarewa a gulma, da ace shi wanine a igadan daya bama boss shawarar karyay wannan gangancin, dan shidai harga ALLAH Ummukulsoom tamasa, yarinyar akwai nutsuwa da sanin darajar mutane.
        Yasan ogansa murɗaɗɗen mutumne na bugawa a jarida, amma sam baida wulaƙanci shima, shiyyasa bai taɓa tunanin hakan daga garesaba, kodai A’i ƙarya ta faɗa masane?.
     Har Motar su Ummu tafice a gidan bayan A’i ta shiga tana habaice-habaice desmond yana wajen tsaye yana hawaye..

        A yaune Ummu ta tabbatar da zargin da tadaɗe tanama A’i na sakama zaman aurenta ido da ɗaukarta CID ɗin Momcy, koda taketa sakin magana a motar dajan Driver da hira murmushi kawai ummu tayi, ita kallon uwa take mata darajar girmanta, hakanne zaisa tabarta da halinta, duniyace zata koya mata hankali, ba itace a gabantaba a halin yanzu….

⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

        Attahir baisan mike faruwaba har washe gari, da yaje Office ya iske maganar turasu ƙasar Seria ta tabbata, kuma harda sunan Amaan da kowa bai taɓa tunaniba.
    Hankalinsa tashe ya nufi office ɗin Amaan ɗin,  shaƙuwarsu ta sanya baya neman ison shiga Office ɗinsa, dan haka sojan dake tsaye a wajen yay salute nashi tareda ƙamewa sannan ya buɗe masa ƙofar ya shiga.
    Lafiyayyen Office dayaji abubuwan more rayuwa gwargwadon iko.
         Kwance yake cikin kujera ido a lumshe, sai faman girgiza ƙafa yake alamar akwai abinda ke damunsa.
      Attahir dayaja wasu mintuna a kansa ya sauke ajiyar zuciya, kafin ya zauna gefensa jiki a matuƙar sanyaye.
     Dukda yanajin motsinsa da tabbatar dashine hakan baisa ya ko motsaba.
       Cikin tsantsar damuwa Attahir ya kirayi sunansa.
     “Ajiwa”.
Shiru bai amsaba, baikuma motsaba tsawon wasu mintuna, kafin ya buɗe manyan idanunsa da suka ƙara girma dayin ja na alamar ɓacin rai ko rashin samun isashen barci, ido kawai ya zubama Attahir amma bakinsa yamasa nauyi.
      Attahir ya kallesa tareda sake gyara zama yana fuskantarsa, shi duk tunaninsa akan maganar turasu Seria ɗinne, dan haka cikin kwantar da murya yace,
      “Ajiwa dan ALLAH ina roƙonka ka janye makaman yaƙinka akan mutanennan, sunfimu fawa a matsayin manyanmu, sun fimu sanin kowanne irin tuggu dake a gidan soji, sun fimu ƙarfin iko a wajen shugabanni, katina kaifa yanzu mai iyaline, dukda ba zaman fahinta kukeyi da matarkaba zata fuskanci babban ƙalubale idan wani abu ya sameka, muma haka, familyn ka ma haka, ma…….”
         Dakatar da Attahir yay cikin ɗaga masa hannu, ya tashi zaune shima sosai, babu abinda yake sai sauke tagwayen ajiyar zuciya na alamar yana tareda tsantsar hasala da fushi,
      “Attahir wlhy kaji na rantse maka bazan janyeba, tabbas duk abinda ka lissafa sun fini, amma bazan zuba idanu aitamana illaba ta ƙarƙashin ƙasa, a kullum ɗaukar yaranmu ake aikin soji, amma sai illatamu ake ta ƙarƙashin ƙasa, daga yaye yara basu wani ƙware a yaƙiba, basu gama fuskantar a ina sukeba sai a ɗebesu akaisu dajika wai su bada tsaro, sai ai amfani da rauninsu aje a saka musu bama bamai ko a buɗe musu wuta duk su mutu, kaga an ɗiba yara sama da miliyan ɗaya zuwa daji da nufin yaƙi kafin wata uku idan ka duba zakaga basufi guda 100 suka rageba, sauran duk an kashesu, sai a dawo kafafen yaɗa labarai ana farfagandar ƴan ta’addane, shin wai ƴan ta’addarnan basa ƙarewane Attahir? Kowa yasan a ƙa’idar yaƙi sai kakai shekaru goma sha a gidan soji kafin a turaka, amma mu a ƙasarmu ko kaɗan ba haka baneba, bakuma komai ke janyo hakanba sai amfanuwa da manyanmu keyi ta wannan hanyar, kuɗaɗen da ake fitarwa kullum akan matsalar tsaroce basaso a dakata, Attahir idan har zamu cigaba da saka ido waɗanan abubuwan na faruwa baka tunanin wataran sai anrasa matashi ko ɗaya daga yankin arewa a gidan soji? Akumayi amfani da wannan damar acigaba da haddasa mana masifa akawo sojojin suyita kashemu suma tunda kullum burin ƙarar damu ake dama, tabbas ina mamakin yanda wasu manyanmu ƴan yankinmu suka zaɓi saida mutuncinmu akan dukiya, Attahir dukiyafa mai karewa, wadda idan yau ALLAH yace saikazo gareshi a matsayin gawa dolene katafi ka barta, wlhy turani wata ƙasa da a kai bashine yake nufin sunci galaba a kainaba, kona mutu a wannan yaƙin da aka turani za’a haifi wanda ya fini….” Magana yake amma hawaye na kwarara a idonsa saboda tsantsar kaiwa ƙarshe da zuciyarsa tayi a ɓacin rai.
     Hakan saiya kuma ɗagama Attahir hankali, Yau Ajiwa daya sanine ke kuka a gabansa saikace wani mace, lallai zuciyarsa takai ƙololuwa a matuƙar ɓaci kuwa.
    Saurin riƙe masa hannu yay alamar lallashi,
        “Ya isa haka dan ALLAH Ajiwa, kukafa kakeyi, abinda tunda nake a rayuwata ban taɓa ganiba”.
      “Humm Attahir bazaka gane bane, bazaka gane yanda zuciyata kejiba akan zalunci kala-kala da al’ummar mu ke fuskanta, bazaka gane ya nakejiba idan na tuna ɗunbin zalinci da tauye haƙƙi da wasu a shigabanninmu ke mana, sai yaushene zamuji daɗin ƙasarmu? Sai yaushene zamu sami ƴanci a ƙasarmu? Sai yaushene yankinmu zai samu kwanciyar hankali? A duk sanda aka tare wancan bala’i saikaji wanda ya fisa ya ɓullo, miyasa a yankinmu kawai waɗannan abubuwan suke tasirine Attahir?”.
         “Gaskiyane Ajiwa, maganarka tana a kan hanya wlhy, saidai yazamuyi tunda mafiya yawan masu madafun ikon riɓaɓɓu sunfi yawa, sannan mu kanmu talakawan zukatanmu babu ƙyau, rashin gaskiya da zalintar junanmu kawai mukasa a gaba, ALLAH dai ya gayaramu gaba ɗaya muda shugabannin. Ajiwa ya maganar matarka? Zata koma kaduna ne kokuwa zaka barta anan?”.
          “Hummm” yaa Amaan ya faɗa cikin tsantsar takaici yana maida manyan idanunsa ya lumeshe, bai sake cewa uffanba har zuwa wani tsawon lokaci kafin yaja siririn tsaki da faɗin “Ni banida wata mata yanzu, dan na maidata gida yau”.
      “Ajiwa saki kake nufi komi? Kasanko mi kake faɗa?”.
      Idanunsa ya buɗe tareda zuba ma  Attahir harara ya maida idanun nasa ya kuma lumshewa yanama Attahir nuni da ƙofa alamar ya fice masa.
     Ko kaɗan Attahir bai yarda da zancenba, dukda basu taɓa irin wannan wasar da Ajiwan ba, ko sallama bai masaba ya tafi cikin sassarfa.
     Wayar maman Ahmad yakira akan taje gidan Amaan ta duba masa Ummu.
    Amma sai tace tana makaranta.
      “Kinga Please, ko lecture kuke kifita kije ki duba tana nan?”.
     “Ban gane tana nanba Dadyn Ahmad?, wace irin maganace wannan kuma?”.
      “Hafsat Please, banason jan magana jeki dan ALLAH, daga baya mayi wannan”.
    Da “to” kawai ta amsa masa ta kashe wayar………..✍????

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button