NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 31 to 40

Ta jima tana kallon yarinyan wanda a baɗini tunani ta lula a kan abinda ke faruwa a ƙasar mu, wanda Fyaɗe ya zama ruwan dare a wannan zamanin

Hannun ta tajanye ta miƙe daga kan gadon ta fito waje

Matar dake zaune bakin ƙofan a ƙasa tana kuka ta ɗago kai da sauri tana kallon Ɗahira, sai kuma ta miƙe cikin rawan baki tace, “Likita..”

Kuka ne yaci ƙarfin ta dole tayi shiru

Ƙwallan da ya cika mata idanu na tsaban tausayin matar da ƴarta ta share sannan ta dubi matar a tsanake tace, “Calm down, she will be relieved by God’s will, but follow ME and we will talk”.

Kallon ta Matar tayi alamun kamar bata fahimta ba

Hakan yasa Ɗahira ta sake maimaita mata da Hausa, “ki kwantar da hankalin ki zata samu sauƙi da yardan Allah, amma ki biyo NI ofiice muyi magana”.

Gyaɗa kanta tayi tana saka gefen zanin ta ta share hawayen ta da suka haɗe da majina, sannan tabi bayan Ɗahira da har ta soma tafiya

Office ɗin ta suka zarce, sai da suka zauna sannan Ɗahira ta kalle ta tace, “zan so ki bani bayani a kan abinda ya faru, sam abun be min daɗi ba kuma tabbas dole ne hukuma ta ɗau mata fansa”.

Numfashi taja kafin taci gaba, “Mun rigada mun cire spain ɗin waɗanda sukai mata wannan aika-aikan, kuma insha Allahu idan result ya fito zamu miƙa case ɗin ga hukuma domin abi mata haƙƙin ta”.

Cikin kuka Matar ta soma magana da faɗin, “Likita mun rigada mun bar su da Allah, sam baza mu iya Shari’a dasu ba domin kuwa waɗanda suka aikata mata hakan sun fi ƙarfin mu nesa ba kusa ba, Ni fata na Allah ya tashi kafaɗun ƴar mu domin kuwa ban san me zance wa Mahaifin ta ba idan ya dawo ya tarda abinda ya faru..” Sai ta fashe da kuka tana ɗaura hannun ta ɗaya saman fuskarta

Kallon ta kawai Ɗahira take yi na tsawon lokaci kafin tace, “kar ki damu dole ne mu miƙa wannan case ɗin ga hukuma, domin a yanzu zancen da nake miki Human right sun shiga zancen nan, kuma ya kamata ki kira mijin naki duk inda yake yazo ya ga abinda ya faru hakan shi ne maslaha, sannan ina so muyi magana dashi”. Taƙarike maganar tana janyo Pepper gaban ta taɗau Bairo ta soma rubutu

Matar bata ce komi ba sai kukan ta da take yi

Miƙa mata Peppern da ta gama rubutu tayi, “Ki je ki siyo wannan alluran ina buƙatar su yanzu”.

Hannu ta saka ta’amsa tana jan majina, “Na gode Likita Allah ya saka da alheri”.

Murmushi kawai Ɗahira tayi mata bata ce komi ba, tana bin ta da kallo har ta fice sannan ta kau da kanta tana sauke ajiyan zuciya, hannu biyu ta saka ta tallabo haɓan ta bayan ta ɗaura gwiwowin hannun saman table, sosai take cikin damuwa akan abin da ke faruwa da yaran mutane

“Wai shin mene ne matsalan hakan? Meke jawo yawan Fyaɗe a wannan lokacin? Sannan mene ne mafita?”

Nocking ɗin da aka yi yasaka ta dawowa hayyacin ta, numfashi taja tana kallon Baffa da ya turo ƙofan ya shigo.

[5/28, 8:08 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

              *FAMILY DOCTORS*

                      ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

  *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

_NAFISAT ISMA’IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*????????‍

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

               *P.W.A✍️*

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

*SADAUKARWA*

_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA’S FAMILY*_

      *EPISODE Eighteen*

      “Yayana baka tafi ba?”

Murmushi yayi ya tako ya zauna yana cewa, “yanzu na tashi nace bari inzo inga ƙanwa ta”.

“Allah Sarki Yayana, ina to budurwan taka ko ta tafi ne?” Tayi maganar tana dariya

Shima dariyan yayi yace, “kai sis yaushe nace miki budurwa ta ce?”

Ɗage kafaɗa tayi tana taɓe baki tace, “Ni naga alama ne ai”.

“Serious ba budurwa ta bace freindship ne kawai a tsakanin mu”.

“Anya Yaya ban yarda ba?”

Langaɓe kansa yayi yace, “shikenan tunda baza ki yarda ba?”

Ɗahira dariya tayi tace, “na yarda to, yaushe ne kuma zaka haɗa ni da budurwan ka ko sai ka kawo ta gida ne zamu ganta?”.

“Very soon lokaci nake jira ai”.

Ɓata fuska tayi tana shirin magana aka yi Nocking

“Yess come in”. Tafaɗa idanun ta a kan ƙofan

Matar da ta fita ɗazu ne ta dawo

“Sis bari in tafi sai mun haɗu a gida”. Baffa yafaɗa yana miƙe wa

“Ok Byeee Yaya”.

Sannan ta kalli matar tace zauna

Zama tayi kamar yanda ta buƙata sannan ta miƙa mata alluran da ta siyo

Amsa Ɗahira tayi ta duba kafin ta kalli matar tace, “Shin Mijin naki ya zo?”

Girgiza kanta tayi sannan tace, “yana Zaria ne a yanzu haka, sai dai kuma na faɗa masa yace min yana kan hanyan dawo wa”.

Gyaɗa kanta tayi kafin tace, “to ki je ki kula da ita, Dr. Rahab zata riƙa zuwa ta duba ta, idan ya ƙariso sai ku taho tare ina son ganin ku”.

Jinjina kanta matar tayi sannan ta miƙe tayi hanyar ƙofa ta fice

Waya ta ɗauka tayi kira sannan ta kara a kunne

“Ki zo ina son ganin ki”. Abun da tafaɗa kenan kafin ta’ajiye wayan taci gaba da duba files ɗin gaban ta

Babu jima wa wata Nurse ta shigo bayan tayi Nocking an ba ta izni

“Gani Doctor” Nurse ɗin tace hakan bayan ta tsaya a gaban table ɗin Ɗahiran

Lokacin ne ta ɗago kai ta kalle ta, sannan taɗau alluran ta miƙo mata tace, “Yauwa Sister ga shi ki je ɗakin da yarinyan nan da aka kawo jiya take kwance kiyi mata alluran nan, Please yanzu zaki yi mata Dr. Rahab bata kusa ne Ni kuma ban yi sallah ba lokaci ya ƙure, ki kula da ita zuwa sanda zata dawo sabida ako yaushe zata iya farka wa kinji?”

Murmusawa Nurse ɗin tayi sannan tasaka hannu ta’amsa alluran a lokaci ɗaya take faɗin “insha Allahu doctor”. Sannan ta juya ta fice

Ita kuma Ɗahira miƙe wa tayi ta cire Labcoat ɗin ta; ta rataye a Hanger, sannan ta zare Eyeglasess ɗin ta tare da agogon hannun ta ta’ajiye ta nufi cikin Toilet ɗauro alwala.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

             Sai da suka gama kitumurmuran su na abin da suke ƙulla wa a kan Baffa da Ɗahira kafin Shakiran ta sauke ta a bakin gidan su sannan taja motan ta tatafi

Ayush bata shiga gidan ba sai ta nufi cikin anguwan, gidan ƙawarta Rumanatu

Rumanatu ƙawa ce wajen Ayush tun na yarinta, da gidan su Ayush ɗin da gidan su Rumanatu gida ɗaya yaraba su, sun taso makaranta tare komi nasu tare har zuwa matakin da suka kai NCE, inda daga nan ne Rumanatu ta dakata da karatun nata, yanzu haka shekara biyu kenan da auren ta, ta taɓa haihuwa ɗan nata na da wata bakwai ya rasu

Gidan ba wani babba bane gidan Rumanatun but gida ne na masu hali tunda mijin ta yana da ƙumban Susa, shima a anguwan yake da zama da iyayen sa

Ƙofar gidan ta ƙwanƙwasa tunda a rufe yake daga ciki, babu jima wa aka zo aka buɗe mata

Rumanatun ce da kanta, ganin Ayush a gaban gidan ta sai ta kwantsama ihu tana rungume ta tare da faɗin, “Ayushhhh”.

Dariya Ayush tayi itama tana rungume ta ɗin, kafin suka saki juna suka shige ta rufo ƙofan, cikin gidan suka shiga suka yaɗa zango a parlour

“Waiii wata sabon gani ai nayi fushi wlh”. Cewar Rumanatu tana ajiye mata farantin silver da ta ciko da drinks

Dariya Ayush tayi bata ce komi ba ta ɗauki Robbern Coke tana buɗe wa

Rumanatun ta sake cewa, “tunda kin zama big girl me amsar Albashi duk wata ai dole ki guje mu”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button