NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 31 to 40

Su dai sauran sai dariya suke musu, basu tashi ba sai da aka kira sallan la’asar, sai ma lokacin ne su Ɗahiran suka tuna basu yi azahar ba, ganin ƴan uwa da hira ya shagaltar dasu

Ɗakin su Salma suka wuce, wasu daga cikin su kuma suka koma nasu Part ɗin, sallan suka gabatar kafin Ɗahira ta miƙe tana kallon Firdausi dake zaune kan sallaya, tana latsa wayan ta da aka kira time ɗin tana sallah

“Fido tashi ki raka Ni mukai gaisuwa wajen Granny da ƴar tsohuwar matar sa, tun kafin ma ya aiko”.

Ɗago kai Firdausi tayi tana dariya tace, “wlh nima dai naga haƙurin sa da be aiko a kira ki ba”.

“Ko dai be san ta zo bane?” Cewar Haneefa dake zaune itama kan dadduman

“He knows, tunda Ni naje na shafa masa labari har ɗakin sa yau za su zo”.

Ɗahira ta murmusa tana faɗin, “Let’s go. Please, I’m too tired to see him, because I’m missing him.”

Salma tace, “oh wa yaga Ɗahira matar tsofaffi, Ni na kula ma tsofaffin nan duk sun fi son ki, Anya ba da ɗaya za ayi ba between Kaka and Granny?”

Dariya suka kwashe dashi sauran cike da shaƙiyanci.

      Fadila da Shakira ma duk tashi suka yi suka bi bayan su Ɗahira don su gaida Granny ɗin, a Parlour suka tarar da Yusra dake zaune ita da Hajiya Laila, nan suka yi mata bayanin “za su je gaishe da Granny ne daga nan su je sauran ɓangaren su gaishe su,” har da Yusran suka tarkata  suka tafi.

     Part ɗin Granny suka soma zuwa, lokacin Inna Haja na sallah a ɗakin ta

Koda suka leƙa suka ga tana sallah ne sai suka nufi ɗakin Granny, yana zaune kuwa yana duba ƙur’ani, shima idar da sallan sa kenan, dayake ba ya iya fita sabida ciwon ƙafa da yake fama dashi, duk da ba’a Wheel chair yake zaune ba, kuma yana iya tafiya amma ba me nisa ba

General Isah Basheer Isah (Walid) kenan, tsoho me ran ƙarfe, kai da gani kasan an zuba ƙaƙƙarfan jarumi sanda yake matashi, har yanzu kuma idan ka kalle sa zaka ga zubin jarumtar sa, don daga gani kasan da sauran ƙarfin sa sosai, sai dai kawai tsufa ne da yayi, ga furfura da duk ya cika masa kai, kasancewar sa ba me barin gemu ba shiyasa babu komi a wajen sai ƙananun gashi farare kaɗan-kaɗan.

      Shigowar su yasaka ya ajiye ƙur’anin yana ɗago kansa tare da cire medical Glass ɗin sa, fuskar sa yalwace da murmushi yake amsa gaisuwar da suke masa tare da bin su ɗaya bayan ɗaya yana kallo

Cikin tsokana Firdausi tace, “wai kuwa ka gane su Granny? Ko sai na maka bayani tunda naga idanun naka sun tsufa da yawa?”

Dariya yayi kafin yace, “ke kam baki da kirki Nana Firdausi, yo idan har bazan gane su ba kema ai bazan iya gane ki ba”.

Gaba ɗaya fashe wa da dariya suka yi, ban da Firdausi da ta kwaɓe fuska tana ma Granny shagwaɓa.

         Nan ya soma tsokanar su Ɗahira bayan ya tambaye su mutanen gida, suka zauna suka biye masa suna ta kwasan dariya

Itama Inna Haja da ta idar da sallan, ɗakin ta shigo ta zauna ana yi da ita.

     Sai da suka daɗe a nan shashin kafin suka wuce sauran sasukan, suka gaishe da su, a Part ɗin Baba ƙarami suka shantake sukai ta kwasan hiran su.

    Washe gari da safe sai ga Hajiya Ikram ta bugo sammako, ita da ƙannin Shamsiyya, sai Babban ƴar ta wacce take aure a Katsinan Aunty Mimi da nata yaran sun taho tare

Zuwa wajen sha ɗaya su Aunty Zulaiha da Aunty Zainab su ma suka zo, gida sai sake cika yake yi kowa ya hallara.

     Da yamma sai ga su Aunty Amarya, Hajiya da Umma sun taho, ban da Hajja Fatu, ita zata biyo su Big Dady ne washe gari ranan auren, idan kuma za su koma su Big Dadyn sai su Hajiya su bi su, ita kuma Hajja Fatu za su dawo ranan Lahadi tare da su Ɗahira.

       Tunda safe su Ɗahiran ma suka tafi yawon su, babu inda ba su zagaya ba, ba su nan ba su can, ko zama ba sa yi, sai da dare ne ma da suka dawo daga yawon na su suka ga su Hajiya sun zo.

     The following day aka ɗaura auren Amarya Salma, sannan aka wuce gidajen Sauran amaren yayyin su aka ɗaura na su

Biki yayi biki, mutane tamkar tsaki, haka suke ta ɓulɓulo wa, su Yusra ma ko ganin ƙeyan su ba ka yi, ana can ana ta shan biki.

     Da dare tare da su aka kai amarya gidan ta, sai dai a cikin su babu wacce ta kwana sai Yusra tunda za’a kwanar ma Amarya, tare da sauran dangi da aka bar mata.

    Zuwa washe gari da yamma suka yi haraman tafiya, ƙarfe 06:30pm. Suka shigo Kaduna.

         

            *WASHE GARI*

      Monday tushen aiki, tunda Ɗahira ta shiga Office ɗin ta yau bata huta ba, sosai take da Patients waɗanda zata duba, shiyasa tunda ta shiga ta duƙufe take faman aiki, gaba ɗaya ta gama gajiya ga shi taƙi huta wa kanta.

        Ƙarfe 05:30pm ta tashi, ta fito daga Office ɗin ta tarufe da keey tayi hanyan Lifter, dayake ta gaji sosai shiyasa tafiyan nata ma sai ya sauya salo, dama gata akwai yanga bare kuma yau me lasisi ne, buɗe Liftern tayi ta shige, tana shirin rufe wa sai ga Usman cikin saurin shima ya shigo, be ma kula da ita ba sai da ya shigo ɗin idanun su suka faɗa na juna, da sauri ko wannen su ya janye nashi suna haɗe rai alokaci ɗaya

Ƙofan fita Ɗahira tayi zata fice, don baza ta iya haɗa hanya dashi ba, sai dai kafin takai ga ficewar sai ji tayi ya jawo ta kiiiiiii.. ta dawo baya, ya jefar da ita wanda tuni ta je ta haɗe da jikin Liftern, saboda azaba ta ƙwalla ƙara tana dafe ƙeyan ta da sauri

Ko a jikin sa sai ma danna number da yayi ya rufe ƙofan, sannan ya tsayar da Liftern cak, yana juyowa gare ta fuska a haɗe..

[5/30, 11:09 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

              *FAMILY DOCTOR’S*

                         ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

   *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

                 _NAFISAT ISMA’IL LAWAL._

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*????????‍

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

               *P.W.A✍️*

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

        

????????????????????????????????????????

???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.

        *EPISODE Twenty One*

         Wani kallon tsana yake aika mata dashi, sai dai ya kasa magana duk da kuwa so yake yi ya faɗi wani abun

Ɗahira a hankali ta ɗago kanta her eyes filled with tears, and she looked at him, yanda ya haɗe rai yasaka ta kasa faɗa masa magana, illa haɗiye yawu da tayi tana aika masa da kallo me cike da tsana gami da haushin sa

Sake haɗe rai yayi, cikin izza irin ta shi yace, “har ke kin isa ki kai ƙara ta wajen iyayena ko? Kina jin kin girma kin zama macen da zaki iya ja da Usman Noor Al’ameen?”

Ɗauke kanta tayi a kansa tana sake dafe ƙeyan ta

Tsawa ya daka mata da faɗin, “Am I not talking? Uban wa ya baki ƙwarin gwiwan da zaki kai ƙara na wajen iyaye na?”

Sosai Ɗahira ta tsorata da yanda ya daka mata tsawa, nan da nan jikin ta ya soma rawa ta ƙanƙame jikin ta tana hawaye

Matsowa kusa da ita yayi yana saka hannu ya jawo kanta ta yanda za su haɗa idanu, sosai ya matse mata kan, wanda ya sa ta dinga zubar da hawaye tare da rufe idanun ta gam

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button